Chapter 20
Chapter 20
sauri na sakesa na cigaba da yimai godiyar ya ce"su Rashida dasu Nadiya anjima zan kai musu tasu". da sauri na ce"yaya yau zan koma gida nima na yi missing ɗin mutanen gida musamman Hajiya kaka ta".dariya ya yi sannan ya ce"caɓɓi rabani da tsohuwar rigima yanzu ina zuwa sashenta to fa na shiga uku na don sai ta ɗauko laifi ta ɗoramin kinsan kaka ko baka yi laifi ba to fa ita awajenka ka yi laifi". Sai kuwa Anty Khadija babu ko kunya ta ce"ah ni dai ki bari sai na haihu sai ki koma gida,tunda kinga bana iya komai kuma gashi kina ɗan yimin aiki".kallon ƙasa da sama yaya Aliyu ya yi mata sannan ya ce"ai kuwa tunda ta ce gidan za ta to sai ta tafi,ke ko kunya ma bakiji ba,ke da gidanki sai yarinya ƙarama ta gyara miki?Allah ya wadaran naka ya lala ce".yana faɗar hakan ya yi tsaki ya yi wucewarsa yana jin wani mugun haushin matarsa arayuwarsa ya tsani ƙazanta ko kaɗan sai gashi Allah ya jarabcesa da mace ƙazama. Nima tashi na yi na tafi abina don idan suna faɗansu tashi na ke in basu waje don ance tsakanin mata da miji sai Allah,don anjima kuma dai kaga sun shirya. Ina kitchen ina girki sai na ɗanji hayani na fito da sauri,Anty khadija naji tana ce wa"wallahi yau sai na fasa wannan wayar idan wannan shegiyar yarinyar ta ƙara kiranka." "to idan kin isa don Allah ki fasa min waya kigani wallahi sai kinyo nadamar yin hakan,ke babu abinda kika iya na farantawa miji sai kullum faɗa da zargi da tashin hankali,to wallahi ko mema zakiyi ki yi idan naso yin aure na baki isa ki hana ba,wawiyar mace kawai".yana faɗar hakan ya kalleni ya ce"khairat ki shirya zanzo anjima na ɗaukeki".a ɗan ɗarare na ce"to yaya".na laɓe ajikin bangon kitchen ɗin. Anty khadija ta zube guiwowinta awajen ta saki kuka kamar ƙaramar yarinya,a hankali na ƙarasa kusa da ita ban iya ce wa komai ba,don ta bani tausayi masu iya magana kuma sukace baƙin cikin ƴa mace na ƴa mace ne. A hankali ta kalleni da idanuwanta waɗanda suka rine sukayi jawur kamar gauta, alamar ma ta daɗe tana kukanta ,ta tashi da ƙer saboda cikinta daya tsufa haihuwa ko yau ko gobe ta tafi ɗakinta,kallonta na yi sosai na fuskanci itama tana bala'in son yaya Aliyu saboda yadda take nuna mugun kishi ko da akai na ne idan muna hira sai inga har wani haɗa rai take,sai dai kawai in kalleta inyi murmushi. Inw gama girkin na zuba akula na ajje a kitchen ɗin ba tare dana jera a dining ba,don na ga mutunen gidan acikin fushi suke.nima ban iya na ci abincin ba saboda ni arayuwata na tsani tashin hankali ko kaɗan. Bai wani daɗe ba sai gashi ya dawo,nima lokacin na shirya,shima wankan ya sake ya saka manyan kaya shadda ruwan army colour ta yi masa masifar ƙyau ya saka hularsa i'tama kalar army colour da ɗan ratsin fari da baƙi yana fitowa ya kalleni yana ɗaura agogon hannunsa ya ce"to ABIN CIKIN ƘWAI tashi mu tafi,yau sai ganin hajiya kaka ko?"ƴar dariya kaɗan na yi don tun ɗazu da sukayi faɗa da anty khadija sai duk naji babu daɗi. Na tashi kenan zan shiga ɗakin antt khadija inyi mata sallama sai gata ta fito fuskar nan tamau kamar zata yi kuka ta ce"sai ina kuma"?.ta kalli yaya Aliyu tana gwalalo mai idanuwa. Ɗan murmushi ya yi alamar rainin wayo samnan ya ce"inda kika aikeni uwata".?yana faɗar hakan ya fita abunsa amman dai da tasha gabansa tana kuka ta ce"wallahi Aliyu babu inda zaka je wato kasha ƙwalliya kana sauri ka tafi wajen zance shine zaka wani fake da kai ƙanwarka gida ko?to wallahi duk inda kaje nima sai na bika". da alama tashin hankalin ya fara isarsa don haka ya ce"Khadija!je ki shirya mu tafi sai kiga inda zani ɗin ko?". Ai kuwa da sauri ta sako mayafinta ta saka har tana neman faɗuwa saboda sauri sai na jiyo sa yana ce wa"yi a hankali kada ki jiwa ɗana ciwo".hararsa ta yi ta shiga gaban motar ni kuma na zauna abaya sai wani cin magani take.ni dariya ma abin na su ya ke bani wallahi kamar wasu yara ƴan ƙananu. Sai da muka tsaya a super market ya lodomin kaya sosai ya ajje a bayan boot,ina kallon anty khadija tana wani hararar kayan sanda ya fito daga super market ɗin.ni kuwa a zuciyata mamakinta kawai na ke yadda take nuna baƙin cikinta afili babu ko kunya. Muna zuwa gidan da sauri na fito har ina haɗa hanya,yaya Aliyu ya ce"ke zo nan"?.ina zuwa ya ce"kina sauri kije kiga tsohuwar kakarki ko?to tsaya ki tafi da tsarabarki".ƴar dariya na yi na tsunna na ɗauka na shiga cikin gidan,daga nan itama uwar rigimar ta fito da ƙaton cikinta tana tafiya daƙer,tana ganin ya koma motarsa zai tafi da sauri ta dawo har tana tuntuɓe ta ce"ikon Allah ka shigo cikin gidan mana ku gaisa ina kuma zakaje".bai ko kulata ba ya haye motarsa ya tafi. Don shi yaya Aliyu yana da wasa ba kamar yaya salim ba amman kuma baya son raini ko kaɗan,don yaga idan ya biyewa khadija sai su ƙwana atsaye shiyasa ya yi wucewarsa don ayau zai nunawa Khadija sam ba tada wayo. ina shiga cikin gidan ban zarce ko ina ba sai sashen hajiya kaka,tana ganin na shigo ta yi saurin ɓoye wani abu,na kalleta irin kallon tuhumar nan na ce"Hajiya kakz duniya,me kuma ake ɓoyewa?"da sauri ta ce"kai ke kuwa khairat me zan ɓoye,ashe kina tafe?da yau na ke cewa Ammar zai kaini gidan Aliyu ɗin tunda dai tunda ki ka tafi ko awaya ma ba'a samunki"?. ɗan murmushi na yi sannan na ce"wallahi nima kaka na kasa nutsuwa sai dai na takura masa ya kawoni". iv ɗin ɗaurin aure na gani abayanta na ce"au Hajiya kaka i.v ɗin ki ke ɓoyemin?na bikinsu Rashida ne ko?". "kai khairat ƙureni kuma zaki yi?to wallahi ko inyamura ce tazo nan yasin baza ta gani ba".dariya kawai na yo muka cigaba da hira na buɗe tsaraba ta ina ba ta,sai ga Nadiya ta shigo ko sallama babu ta faɗo.Kaka ta yi salati ta ce"ke jahilar banza baki iya sallama bane?".turo baki Nadiya ta yi sannan ta ce"na iya mana?ni dai gaskiya kaka na gaji da wannan uban aikin da ki ke lodo mana kayan wankin kutanen gidannan duk mu muke wankewa?ba'a barmu anan bama harda sharar harabar gidannan duk yawansa?gaskiya kaka ki duba mana?". riƙe baki Hajiya kaka ta yi sannan ta ce"eh lallai yarinyar baki da ko kunyar yin magana?au don ban saka soja ya ƙar lakaɗa muku na jaki bane shiyasa ki ke faɗar haka ko?to yasin ko fulanin daji ce tazo nan wallahi sai kinyi aikin nan,ƴar banza mara mutunci kawai,halin fulanin daji na hauka tsaf ikilima ta kwasa muku,ni dai Allah yabi wa ɗana haƙƙinsa,irin wannan ɗibar albarkar da me ya yi kama haka?"sai ta ɗakko wani madoki za ta ƙwaɗawa Nadiya da gudu ta fita.ta sauke labulen ɗakinta wanda ta ɗagashi saboda duka ta ce"da mana ki taho ki cigaba da haukan da kinsan kinyi da ƴar halak". ta dawo tana haki na
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87