Skip to content

Chapter 3

Chapter 3

Abin Cikin Kwai Book One Complete Hausa Novel 1,276 words 0 views Progress saved
Download Book

ne mata ƴaƴan kaka goma maza,nan fa kaka ta shiga gaya musu wai tana ji lokacinda aka ce a ƙara volume tunda masifaffiya ta iso. *Miss green ce* [23/09, 16:15] Miss Green🍀: _*🥚ABIN CIKIN ƘWAI...!*_ 📃Littafi na 1 By🪶 *Ummu maher(Miss green)🍏* *GAWURTATTU 5* ----------------------- *wattpad user name* https://www.wattpad.com/user/Rabiatu333 --------------- *Arewa book user* https://arewabooks.com/u/rabiattu0444 -------------------- *Sirrinmu* manzon Allah (s.A.W) ya hanemu da gujewa mazajenmu a shimfiɗa yin hakan babban laifi ne kuma tsinuwar mala'iku za ta tabbata akanki. -------------------------------- 3🟪4 .. .Dukansu suka haɗa baki wajen ce wa "umma lafiya me ya faru?".kukan ta ƙara fasawa tana ce wa"yanzu har lokacin wulaƙanta ni agidannan ya yi?gaskiya zan bar muku gidannan ku zauna ku da matanku tunda haka kuka zaɓa". dukansu shiru suka yi sai malik ne ya ce"Umma ki faɗa mana abinda ya faru,don mun shiga cikin duhu wallahi". "To matarka ce inya mura ita ce ta ɓata min rai,wai ga masifaffiya nan ta iso,don ubanta gidan inyamurai ne nan da za ta tara mana ƴan bariki suna muskuta ɗuwaiwaka kamar gidan maguxawa?to wallahi ni nagaji xan barmuku gidanku".sai ta fashe da kuka sosai har da majina,Hajiya Iklima ta ce"kaka don Allah ki yi haƙuri ki daina kuka"sai kuwa kaka ta Juyo a fusace ta ce"indai na kuka ko?tunda ba uwarki ce taka kukan ba ai dole ki ce haka?ni tashi ma shi ki barni in yi magana da ƴaƴana bana son bare awajen. wani malulun baƙin ciki ne ya cika zuciyar Hajiya iklima ta Kalli fuskar hajiya kaka ta harareta,ita ta rasa wacce irin mata ce ba ta ɗaukar zuga ko kaɗan,amman ta yi alƙawarin muddin tana raye sai ta haɗa Hajiya kaka da dukkanin surukanta ta zama ita ce ta gaban goshi. Tashi ta yi ta fita tana mai ƙara jin haushin cin fuskar da Hajiya kaka ta yi mata,sai kuwa kaka ta ce"to as dai a fita don bana son ina shawara da ƴaƴa na a zo asakamin idanu irin na fulanin daji". wannan magana da kaka ta faɗa ba ƙaramin mugun haushi ya bawa Hajiya iklima ba,don tasan sarai da ita take don asalinta fulanin daji ce,don itama kafin ta bari a aurota ba ƙaramin gwagwarmaya aka sha ba. "Umma insha Allsh daga yau Zulaihat ba xa ta ƙara yi miki wani abu da zai ɓata miki rai ba,yanzu ma ba sai anjima ba za ta baki haƙuri",yana faɗar hakan ya yi saurin fita. Usman autan Hajiya kaka ya ce"gaskiya umma ki daina yi wa wannan baiwar Allahm haka,gaskiya ba a ƙyauta mata wallahi saboda ita ba yaranmu ba ce sai kuma ace za abi a tsaneta". "ah lallai ƙanin Zulai ka ce kaima an jiƙa an baka,kamar yadda sukayi wa ɗan uwanka a da cen baya,yanzu kuwa Allah ya dawo min da hankalin ɗana jikinsa,yanzu muna nan da kai za kaga caccakar da zai yi musu shegu masu cin arziƙi,tunda suka zo ina kula dasu babu abinda suke sai dafa nama daga an sauke wancen a ɗora wannan,ɗana yana ta kawowa suna cinyewa". dukkansu shiru sukayi har Alhaji Aliyu wato babban ɗan ta don shima ba'a bar matarsa ba,don haka haƙuri kawai ya iya bawa Hajiya kaka yaja bakinsa ya yi shiru. A ɗakinsa ta samesa yana kaiwa yana kawowa hannayensa ya rungumesu a baya,sallama ta yi ta samu waje ta zauna kanta a ƙasa sai ta ji ya ce cikin zafi"Yanzu Xulaihat abinda ki ka yi wa mahaifiyata ya yi miki daɗi kenan? ki tara ƴan uwanki suna zagar min mahaifiya ta to wallahi ba zan lamunta ba,kowa ya haɗa kayansa ya barmin gidana don ba zan lamunci cin fuskar kowaccenku akan mahaifiyata ba. Muryarta na rawa zata yi magana da sauri ya ɗaga mata hannu ran tsohon soja ya tashi ya fita yabar mata ɗakin,ya koma wajen mahaifiyarsa ya cigaba da lallaɓa ta,don yana fatan ya gama da ita lafiya. Kuka sosai ta yi awajen kafin ta tashi ta fita,tana tunanin ta yadda za ta gayawa ƴan uwanta wannan maganar garinsu da sai a yini a kusan ƙwana ana tafiya sannan sai da yamma ta yi sannan za a ce su koma da yamman nan ko kai amarya ba ayi ba sunga gida. Ɗaki ta koma tasha kukanta sosai,a hankali na buɗe ƙofar ɗakin mahaifiyata halin dana ganta a ciku shine ya ƙara jagula min tuna nina,na ƙarasa kusa da ita hankalina atashe ganin fuskarta ta jiƙe sosai da hawaye cikin daburce wa na ce"Mama lafiya me ya faru da ke?" Bata iya ce wa komai ba ta tashi ta fita,binta na yi da kallo ina hasashen abinda ya faru tabbas hajiya kaka ce ba wani ba,don tun ina ƙarama na sha kama mama tana kuka kuma ba kowa ne musababin kukanba sai hajiya kaka,sam bata san mama na ban san abinda ta yi mata ta tsaneta haka ba.nima bani da zaɓi daya wuce in fito daga ɗakin don haka na yo waje don ƙawayenmu duk sunci ƙwalliya don kai amarya,ina fitowa Rashida ta ce"lafiya naga fuskar mama duk ta canza?ko ke ce kika yi mata wani abin". "hmm Rashida ni kuwa me zanyi wa mama da za ta yi fushi dani haka?kawai dai kin san tsakaninta da hajiya kaka ina ganin wannan ne amman ba ni ba ce." "kin san Allah Khairat matar nab gaba ki ɗaya ta ishemu a gidannan,ni na rasa dalilin daya sa duk iyayenmu suke cikin gidannan kamar dole,ita kuma ba bari take a zauna lafiya ba,kullum sai faɗa ni wallahi matar nan ma na matsu ta margaya mu huta da jarabarta. Saurin rufe mata baki na yi na ce"wallahi Rashida ki kiyayi wannan bakin na ki kinsan dai matar nan kakarmu ce,babu yadda zamuyi da ita suma iyayenmu haƙuri suke da ita,muma ya kamata muyi haƙurin ko?" Iman da Salimat da suke juyo hirar da su Khairat suke sai kuwa suka ce"Hmm Rashida wallahi ki cigaba da maganarki kada ki biyewa wannan wacce bata san inda ya ke mata feeling ba,don haka ko muma wallahi mun tsaneta wallahi tunda bata san iyayenmu mu ma dole ne mu tsaneta". ni dai fitowa na yi babban hall ɗin da ake hidimar bikin abin mamaki duk babu ƴan uwan mama na awajen abin ya ɗaure min kai sosai,yanzu fa na gansu awajen amman har na nemesu ban gansu ba. Aranar dangin mama na duka suka koma ba tare da sun tsaya sai washe garin ba,hankalina ya tashi sosai na fito na yi sashen hajiya kaka,tana zaune ita da wata ƙawarta Hajiya Inna,na gaisheta tana tsokana ta tana ce wa saura na mu muma,kunya ce ta rufeni sai kuwa na ji Hajiya kaka na ce wa"Hmm Hajiya Inna kema dai kya faɗa wallahi wataran idan na ga yaran nan suna shiga suna fice agidannan su kusan ashirin duk ƴan mata,sai in shiga ɗaki inyi ta kuka sai ta buɗe injirnta ta ce"kinga duk inda na yi ƙashin wuya saboda yarannan duk dun tsotseni wallahi". duk da ina cikin tashin hankali sai da na yi dariya sannan na ce"Hajiya kaka kina da masaniyar dangin mamana duk sun bar gidannan acikin wannan daren ko kai amaryar basu yi ba sunga gidan brother". "brozo na ce ungo ƴar nema. to sai me don sun bar gidan ai ni sauƙina ne don wallahi idan na

Table of Contents

Chapters

87 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87