Chapter 27
Chapter 27
amman sai dai me?tun kafin ta sauke hannunta itama meron ta rama jika ke tas tas maruka har biyu. Da sauri na riƘe hannun mero ina janta gefe sai kuwa mero ta ce"anty wallahi ki daina ja na don wallahi yau sai na fasawa wannan farar kamar Ƙwai baki". da Ƙer naja ta gefe tana Ta faman kumfar baki. ranar sosai aka yi rigima agidan momi iklima ta dage wai sai ta ramawa nadiya mari hajiya kaka ta ce taje idan ta isa ta dake ta,ai kuwa ta shige Ɗaki ba tare da ta Ƙara magana ba,don tasan halin hajiya kaka kaƊan daga aikinta ta ciwa mutum mutumci,musamman idan ta rufe waƊannan fici-ficin idanuwanta,sai ta wanke mutum tsaf. Sosai muke shirin yin sauka ni da rashida muke abinmu su nadiya ma nasu suke,don yanzu tsakanin rashida da nadiya abin ya Ɓaci,don ita nadiya kallon kishiya takewa rashida,ita kuwa rashidar ko kallon inuwar Nadiyar bata yi,don ta ce rashida bata isa ta yi kishi da ita ba,don bata kai wannan matsayin ba. sosai hajiya kaka ke ihu duk hankalinmu ya tashi,sai dai me!?muna zuwa muka tarar da ita ta saka kuƊinta agaba wanda suka kekkece kamar an Ɗakkosu a bakin kura. mamaki sosai kowa ya ke ga kuƊi da yawa amman kaƊanne ba'a keta su ba. Nice na yi Ƙarfin halin zuwa wajenta na ce"hajiya kaka me ya faru da kuƊinki haka?". Kukan ta cigaba da yi sannan ta ce"khairat ranar da kiga ina Ƙirga kuƊinnan?" sai kuwa na Ɗaga kai alamar na gane,ta ce"to tsautsayi ina Ɗakkosu A ƙarƙashin gado shine naga duk Ɓeraye sun cinye min". kowa guntse dariyarsa ya yi,sai kuwa mero ta ce"ah kiji min tsohuwa da wayo?yanzu ai gashinan kinyi biyu babu".? madoki hajiya kaka ta Ɗakko tana ce wa wallahi sai in dake ki in daki kuƊina wallahi". Da gudu ta yi gefe ta cigaba da dariyarta. yaya mukhatar wanda shigowarsa kenan ya ce"to yanzi kinga sai aje asaka kuƊin abola ko?". da sauri ta juyo ta ce"to ai ba haƊejawa ne suka bani kuƊin ba?Da dangin uwarkane suka bani yau da nasan sai sun garƘameni". Jan bakinsa ya yi kawai ya yi shiru,Ƙarshe dai yaya mk da yaya Aliyu sunyi mata alƘawarin biyanta kuƊinta wanda ta ce dubu sittin ne,don muddin basu biya taba aƘwai matsala. anan aka Ƙirga dubu shabiyar waɗanda su babu abinda ya shafesu,hajiya kaka sai tsinewa Ɓeraye take tana kuka. Su nadiya sai dariya suke don daman haushinta suke ji. ina fitowa daga sashen hajiya kaka yaya mk ya biyoni,yana kiran sunana haushi da kuma nadamar haƊuwa dashi suka saka baki Ɗaya na kasa koda kallonsa,shi kuma gani ya ke kamar kunyarsa na ke,amman fa azuciyata tsanarsa ce fal araina. da sauri na tsaya awani lungu wanda ya raba sashenmu dana baba Ƙasim,saboda san bana son kowa ya ganmu. hira sosai ya ke min ni kuwa Allah2 na ke ya Ƙeleni in tafi don ni Ƙwana biyu da ya yi tafiya har wani daƊi ne ya keji wai don ma bai san ina da waya ba,da na shiga uku da waya. kuƊi sosai ya bani wai inyi shagalin sauka ta dashi naƘi amsa amman duk da haka sai da ya takuramin na amsa,har na shiga Ɓangarenmu bai daina kallona ba,yadda kasan zai biyo ni,har tausayi ya fara Ɗan bani don mai sonka ka soshi ko yaya ne. mama na nunawa kuƊin,ta kalleni sannan ta ce"khairat wai ni mukhatar aƘwai wani abu da ke tsakaninku dashi ne?". kai na a sunkuye na ce"mama wai ce wa ya yi yana sona".da sauri mama wai mama sona ya ke mama". "khairat kinfi kowa sanin ce wa bara'atu fa ya ke so,tun kafin a gane kuna tare dashi ki rabu dashi don gaskiya ni bana son tashin hankali". GyaƊa kai kawai na yi don nima daƊin hakan na keso,don ni zuciyar nan tawa A.D,Ne kawai acikinta ma'ana yaya Bilal. **** sosai filin saukar ya cika ana sauraran Ƙira'ah mai masifar daƊi daga bakin jikar hajiya kaka ABIN CIKIN ƘWAI,wato khairat da yawan mutane hankalinsu na kan khairat yawancin mazan wajen kuma ce wa suke dama khairat ta zama matarsu don yarinyar Allah ya yi mata baiwa sosai,khairat dai ba wata mai Ƙyau ba ce,tana dai da baiwa sosai diri tana da shape wanda ake ce wa coca cola shape ga wani dimfil wanda ya Ƙawata doguwar fuskarta,kuma ita dai ba fara bace kamar sauran Ƴan gidansu,amman tana da baiwa ta ilimi na arabi da boko. abin mamaki da aka kira jidda wata Ƴar ajinmu da Ƙer ta kai karatun saukar na ta,amman wai sai mukaji ana sanarwar wai wani wanda ake kira da ADMIRAL BILAL ABDULLAHI,wanda aka fi sani da A.D ya bata Ƙyautar mota. Sosai kowa ya yi mamakin jin hakan duba da irin yadda karatuna ya Ɗauki hankalin mutane da dama,kuma nima na samu Ƙyautuka sosai ciki har da Ƙyautar wata hamshaƘiyar computer wanda Ɗan majalisa ya bani,sannan na samu Ƙyauta ta dubu Ɗari biyu daga hannun wani mai kuƊi. har muka dawo gida zuciyata tana wajen Ƙyautar da yaya Bilal ya bawa jidda Ƴar ajinmu. To me ye tsakanin jidda da yaya Bilal?babu mai bani amsar hakan,don haka na zubawa sarautar Allah ido ammab zuciyata sai kai kawo take,saboda tunanin abunda ya shige min duhu. satin bikinsu Rashida ya kama,sosai ƘwaƘwalwata ta yi busy duk hankalina kacokan yana kan bukin,ni da maryam ne manyan Ƙawayen amarya don haka tare muke komai. Wata rana ranar da bazan taƁa mantawa da ita ba,ita ce rabar dinner Ɗinsu rashida,yaya Bilal naga ni da jidda ya sama mata kujera ta zauna tasha anko irin namu sak,onion color ne material Ɗin sai mukayi pitet gown amman ita jidda riga da siket ta saka wanda sukayi masifar yi mata Ƙyau. Sosai jikina ya ke rawa hankalina idan ya yi dubu to ya Ɓaci,wasu zafafan hawaye masu zafi suka zubomin,na fito daga wajen baki Ɗaya,na samu wani wajen flower's kuraye shar,na tsugunna na fara wani irin kuka mai tsanani,ina jan doguwar rigar dana saka kamar ita ce ta yi min laifin. Dafa kafaƊa ta naji anyi,maryam ta bayyana agaba na,ta Ɗago haƁa ta cikin tausayi sannan ta ce"ki yi haƘuri khairat naga duk abinda ki ka gani,amman ina son ki daurewa zuciyarki ki yi haƘuri don Allah a Ƙarasa bikin dinner Ɗinnan kada kowa ya gane abinda ke faruwa,shi so haka ya ke yana da zafi musamman idan wanda ka keso baya sonka,to tabbas zaka shiga wani hali,nasan abinda ki keji tunda nima na taƁa shiga irin wannan halin." ta damƘe hannuwa na sannan ta ce"khairat ina tare da ke ako ina insha Allah sai kin auri yaya Bilal,ni Ɗinnan zan tsaya miki insha Allah",Ta kalleni tana saukemin idanu itama duk hankalinta atashe amman kuma tana dauriyar dannewa saboda ni. Nan dai ta cigaba da rarrashi na ta bani hoda na Ɗan shafa saboda kada a gane kukan dana yi. yaya salim yana zuma akan kujera,mero wacce take ta faman zuba ita da wata Ƴar Ƙyauye irinta,ga kuma wani lemo a hannunta tana ta faman zuƘa kamar za ta shanye har da bottle Ɗin. Tsi ta zubawa yaya salim a jikinsa duk ta Ɓata mishi kayansa,da sauri ya tashi alokacin yana waya da budurwarsa mai suna salimat yana
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87