Skip to content

Chapter 42

Chapter 42

Abin Cikin Kwai Book One Complete Hausa Novel 1,316 words 0 views Progress saved
Download Book

bikinda Hajiya kaka ta taɓa kashe kuɗi irin bikina,ta kashe kuɗi ba na wasa ba,har tausayi ta bani. Ana cikin wannan kiɗanne na zagaye a hankali na fita na koma ɗakin Hajiya kaka na dinga cin kukana idanuwa na sukayi jawur kamar gauta. A hankali mama ta ƙaraso inda na ke,ta ɗago fuskata sosai ta sharemin hawaye na sannan ta ce"khairat aƙwai abubuwa da yawa da ya kamata in faɗa miki amatsayi na,na mahaifiyarki duk wata uwa tagari tana yi wa ƴarta da nasiha da tabi mijinta,ta yi masa biyayya,yi na yi bari na bari sannan aƙwai wasu abubuwan da ya kamata in faɗa miki na farko shine,kada ki sake mijinki yaji wari ko wani bashi ajikinki,ki kasance mai tsarkake jikinki ki zamo kullum cikin tsafta,yin hakan zai ƙara kusanta ki da mijinki sannan tsafta na ɗaya daga cikin ginshiƙin aure,matuƙar mace ƙazama ce to za kiga babu inda auren ya ke kaiwa,kullum cikin faɗace2 da kai ƙara,abu na biyu kuma shine ki kasance mai kula masa da dukiyarsa wala yana nan wala baya nan,ke dai ki zamo mai saka idanu akan kula da dukiyarsa,sannan ki rintse idaniyarki akan kuɗinsa,duk yawan kuɗin da zai ajje kada ki ɗaukar masa,khairat nasan halinki nasan baki taɓa yin hakan ba amman ki kiyaye hakan.ladabi da kuma biyayya indai ya baki umarni ko menene ki yi,indai har bai take addini ba to ina mai jan hankalinki ki yi sa,iya girki nasan ke gwana ce akan hakan amman yanzu tunda miji zaki yiwa to tabbas ya kamata ki ƙara ƙwazo sosai ta yadda zaki yi fice aduniyar girki. Khairat idan har na ce zan zaunar dake inyi ta yi miki magana akan aure to tabbas zamu ƙwana ban gama ba,sai dai ince Allah ubangiji ya baku xaman lafiya me ɗorewa. Tana faɗar hakan ta rungume ni tana kuka sosai,nima kukan na ke a haka Rashida ta shigo ta samemu,itama ta taya mu kukan,babu mai rarrashin wani. Mama ta ce"khairat wannan envelope da kika bani wanda wannan bawan Allahn ya baki,jiya na buɗesa naga kuɗi ne aciki har dubu ɗari,to shine na wuce kasuwa na siyo miki wasu abubuwan,banso na yi amfani dashi ba amman Aliyu ya tabbatar min da mutumin arziƙine,sannan yau daya zo ɗaurin aure ya baki ƙyautar mota guda,amman mahaifinki ce wa yayi ba za'a amsa ba,amayar masa amman motar tana gidan Aliyu,za'a siyar a siya miki wani abin mai amfani." Na yi mamakin Ahmad sosai kamar bai san daɗin kuɗi ba?irin wannan zubar da kuɗi haka?nan dai mama ta sakani agaba na shiga banɗaki ta zubamin wani abu mai ƙamshi acikin ruwan,na shiga na yi wanka ƙamshi duk ya baɗe ɗakin,ina fitowa ta bani wata zuma mai kauri tace insha,babu musu na ɗaga kaina nasha,sannan ta bani wasu abubuwan ta koyamin yadda zanyi amfani dasu koda bayan aure idan ina da buƙata. Yadda ake haɗa zumar mata. *Zuma* *citta* *kanunfari* *minanas* *Riɗi* *sassaƙen ɓaure* *sassaƙen gamji* *ƙwaƙwa* Ki samu zumarki mai ƙyau,sai ki samu sassaƙen ɓaure amman bayan kin dakashi ya yi luƙui kin tankaɗeshi,sai ki ɗora zumar akan wuta kiɗan ƙara ruwa kaɗan,sai ki zuba garin minanas da kuma garin ɓauren da kika daka,sai gamji shima kamar garin ɓaure,chokali biyu biyu zaji zuba,ya danganta da yawan zumarki don ba'a son ya cika kauri da yawa,sai ki zuba garin citta,da kuma garin kanumfari,sai kiɗan soya ƙwaƙwa daban daman kun riga da kin soyata ƙananu sai ki zuba aciki,riɗinki ma ki zuba bayan kin wankeshi kin busar dashi sosai.sai ki rage wuta kina juyawa kaɗan kaɗan,shi wannan haɗin ba'a son ki cika masa wuta. Za kiji yana ƙamshi to alamar ya yi kenan,sai ki sauke ki samu ƙwalbarki mai ƙyau ki zuba aciki,ki dinga shan chokali 2 da safe biyu da yamma. Hmm ni dai bazance komai ba,sai an gwada akan san na ƙwarai. ***** "Ai Bilal ba sai ka nunamin ce wa baka son yarinyar nan ba?ƙarfe nawa yanzu?ɗaga kanka ka duba agogo?".a hankali ya ɗaga kansa ya duba agogon ƙarfe 10 na dare,ya sauke kansa sannan ya ce"kai Hajiya kaka gaskiya kina takuramin wallahi,yanzu me ki ke son inyi miki?". sheƙeƙe ta kallesa sannan ta ce"ungo Ruƙayya zaka yi min"?.ta faɗi hakan tana harararshi,ga dai mata nan ka bari agidanku ka ƙi ka kawo motocin da za'a kaita gidanka,mero wacce zata zauna agidannan tun biyar akazo aka ɗauketa,amman kai shine zaka gaya min maganar banza ko"?. "Haba grany!ba fa ita kaɗai ce matata ba,ga Jidda nan,amman ita babu wanda ya damu,sai ita ƴar gwal,kuma ni zanje in ɗauko jidda da kaina,ita kuma xan aiko azo a ɗauketa,shikkenan?". Ya faɗi hakan yana ɗagawa Hajiya kaka gira,ta ce"ai wallahi kuwa baka isa ba Bilal,wato ma har ka ke cemin ita wannan figigiyar matar taka kai za kaje ka ɗakkota,ita kuma wannan za'ka aiko a ɗauketa ko?to ban yarda ba,sai dai ita ka tura a ɗakkota wallahi,kuma ni zan kaita har ɗakinta". Ta faɗi hakan tana shiga ɓangarenta,daman mama ta sakani na canja kayana,wata haɗaɗɗiyar lifaya mai ƙyau,fara ƙal da ratsin kore na yafa ta har kaina na rufe ruf,hajiya kaka ta janyo hannuna mama tana ta rarrashina,muka fito waje. Yana tsaye inda kaka ta barsa,ya hangota ya juya kai abinsa,azuciyarsa yana ce wa yarinyar da aka haifeta agabana na raineta sannan yanzu acw wai ita ce matata?wannan ma ai janyowa mutum raini ne.ya shiga cikin motar ya tayar da ita abaya muka zauna nida hajiya kaka,sai ƴar uwar mamana guda ɗaya. Karatun qur'anine ke tashi acikin motar,ga ƙamshin freshner ya cika motar mai sanyin daɗi,har mukaje kuka na ke,duk haushi ya cika sa a fili ya ce"wannan ai dole mutum yasha pain reliep".Hajiya kaka na jinsa ta hararesa ta baya. Abakin kyakkyawan ɓangare na aka saukeni,ɓangare uku ne agidan,ɗaya nawa,ɗaya na jidda ɗaya na me gidan,ɓangare na ya yi kyau sosai,ko sisin mahaifina babu aciki Baba Abdullahi shi ya yi rawa ya yi tsaki,kayan da aka sakamin ko su Rashida dasu ke matsayin ƴaƴansa bai yi musu shi ba.har kayan kitchen bawan Allahn nan shine ya yi,ya bawa ƙannansa su Aisha suka siyo masu matuƙar kyau. Koda zamu shiga sashen nawa hajiya kaka ta ce"ki yi bismillah kafin ki shiga Allah ya kareki daga sharrin duk wani mai sharri". Da ƙafar dama na shiga gabana yana dukan uku uku,shikkenan ta faru ta ƙare yau dai Allah ya kawoni gidan da za'a gasa ni kamar yadda na nema,jikina duk ya yi sanyi sosai. Sai asannan aka dinga kawo mutane aka cika gida ɓam,Jidda kuwa ta cika ta yi ɓam,don ta kirasa amman bai gani ba wayarsa na silent,sai sannan ya duba ya gani,tuni jidda tafi awa agidan,don Babanta ya ce akawo ta tunda masu ɗaukarta basu zo ba,a sabuwar motar Jidda ɗin aka kawota,sabuwa dal sai sheƙi take. Shigowar saƙo wayarsa ne yasa ya duba alokacin yana shirin zuwa ya ɗauko jidda,da sauri ya kalli sashen jidda ɗin sannan ya kalli wajen motocin gidan,sosai abin ya basa mamaki me yasa bata jira yazo da kansa ya ɗauketa ba,wani kishi ya tokare masa ƙirjinsa,yanzu haka wasu mazan duk sun kalle masa matarsa. Kai tsaye sai da ya fara shiga sashensa ya ajje wasu abubuwan sannan ya shiga wajen jiddarsa,yana shiga ɗakin na ta ya hangota kan gadonta babu ko lulluɓin idanuwanta sun kumbura saboda kuka,ta

Table of Contents

Chapters

87 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87