Chapter 75
Chapter 75
a ƙasa ya ce"khairat na yi bincike akan yaron nan balaraben nan,kuma na gano yaron arziƙi ne har mahaifinsa wanda Allah ya yiwa rasuwa,kuma gobe zasu zo a saka ranar aure da komai".murmushi kawai na yi kaina yana a ƙasa na tashi na tafi da sauri saboda kunyar baba dana ke ji. Haryanzu su twins basu dawo ɓangarenmu ba,nima ban damu ba don da kansu yaran ke zuwa waje na su cika nima da surutu don haka na ke kaɗa kansu su tafi baki ɗaya ma,wannan abin ba ƙaramin tsayawa Bilal arai ya yi ba,ya shirya kayansa ya koma wajen aiki ransa duk babu daɗi don gani ya ke kome ya yiwa khairat bai cancanci ta tsanesa har haka ba. Ƴan huɗu kuka sosai suke da tafiyar mahaifinsu,suka saka Kakarsu agaba Hajiya Ruƙayya wai su sai sun dawo banu yadda ta iya haka nan ta dawomin dasu,ai kuwa wataran har paracetamol na ke sha saboda fitinarsu,wataran idan na fita zance bina suke Shahid kuwa ya biye musu suyi ta yi masa shirme,har sai na gaji na korasu gida sannan suke haƙura.ai kuwa shahid yana yi musu hidima sosai,kuɗi kuwa kullum cikin turomin su ya ke,inyi ta fushi saboda kuɗin sunyi yawa,idan na yi magana shima haushin ya ke ji sosai don haka sai na daina yin maganar. Rashida fa ta dage wai tana fushi dani akan abubuwan da na ke yiwa yayanta,ni har mamaki suke bani daga ita har yayan nata da duk wani meson na koma gidanshi,don gani na ke kamar ilimin addini bai ishesu ba,don duk wanda ya yi ilimi bazai ce na koma gidan Bilal ba. ********* sosai mutanen gidanmu suka tisa gulmata agaba,wai zan auri ɗan yankan kai,don irin kuɗin da aka kawo na aure na ya girgixa kunnuwansu sosai,ya bada sadaki miliyan biyar,ai kuwa duk hankalinsu ya tashi don gani suke kamar shahid bai da hankali,don idan da yana da hankalu bazaiyi haka ba. Hmm maganar gulma kuwa yanzu ta ƙaru alokacin da aka fara.shigowa da lefe na cikin gidanmu,aƙwatina suka ƙi ƙarewa sau shigowa dasu ake,ƴan uwa da sukazo ƙarɓar lefe sai da suka gaji da ƙirgawa,Aƙwati dozin huɗu haka aka kawo min,Hajiya kaka sai buɗa take tana yada magana a fakaice tana ce wa"ho ho ina gwanin wani ga naka,lallai yau ake harkar arziƙi agidan nan,Ba lefi aƙwati shida ba alokacin ma wai tana budurwa kenan?aka kawo mata wannan lefan kamar ƴar tsana,yanzu kuwa gashi Allah ya fidda ta,ni atarihi ma ban taɓa ganin yarinyar da aka kawowa lefe har haka ba". Tuni aka dinga ɗaukar hotunansu ana turawa ta facebook,lefe na ya girgiza ƴan mata da dama sosai,suka shiga burin ina ma ace suma su samu wannan kaya haka. Sosai na shiga gyaran jiki na ciki da waje,mama da kanta ta hau gyara ni sosai na yi kyau kamar ba ni ba,Mama ta ɗaukomin me gyaran jiki har gida ai kuwa kafin kace me na yi wani irin mugun kyau kamar ka ɗauke ni,sau ɗaukar ido na ke,na karɓi hutu a skull saboda gyaran da na ke,abin mamaki kawai sai ga Xuhra ta zo wai taji labarin biki na,na yi mamaki sosai harda dariya ta,wato daman tana gaba da nine saboda kada in auri mijinta?babu yadda zanyi don daman ni ban riƙe ta ba,muka cigaba da al'amuranmu tare har yanzu bata haihu ba Allah bai kawo ba. Shahid ya maƙale murya kamar yaro ya ce"gaskiya Hayatee na gaji ki fito ko kaɗanne in ganki mana?tunda aka fara sha'anin biki bana ganinki,sai ɓoyemin kanki ki ke?".shgwaɓa ya dinga yimin kamar yaro,babu yadda zanyi dole na saka wata arabian gown,me kyau sosai kalar yellow,na yafa velt ɗin akaina na fito,gashi na yasha gyara sosai. Tun daga nesa ya sakani agaba da kallo kamar zai cinye ni,kunya duk ta ishe ni Iman ta biyo ni da gudu wai zata bini,maimakon tazo inda na ke sai naga ta canja ƙwana tana ce wa"Baba oyoyo". Da sauri na ɗaga kai na ina kallon wanda take kira da baban Bilal na hango yana sanye cikin kayan sojinsa ya haɗe rai kamar bai taɓa wata dariya ba.. ... .✍🏿 07068606171 *GAWURTATTU BIYAR, TAFIYAR TA MUSAMMAMN CE. 👯♀️👎👇👇* 1, *MU GANI A ƘASA...*🔥 _Ummu Affan_ 2, *ABIN CIKIN ƘWAI..*🥚 _Ummu Maher_ 3, *GUNTUN GORO..*💥 _Mom Islam_ 4, *GISHIRIN ZAMAN DUNIYA*🌎 _Mrs Bukhari_ 5, *AUREN WATA TARA*👩❤️👨 _Miss Hajo_ Guda biyar 1k Guda huɗu N700 Guda uku N600 Guda biyu N500 Guda ɗaya N300 *DOMIN TURA KUƊIN KAI TSAYE*👇 0037219728 Fatima Rabiu Sunusi StanbicIBTC Bank. Domin tura shaidar biya👇 0810 433 5144 Masu tura katin MTN👇 0814 179 9224 Ƴan Ƙasar Niger zasu tura nasu anan.👇 0817 952 3215 Guda biyar 1000f Guda huɗu 700f Guda uku 600f Guda biyu 500f Guda ɗaya 300f *TEAM GAWURTATTU BIYAR TAKUN FARKO TAFIYA TA MUSAMMAN.* 🔥🥚💥🌎👩❤️👨 _*Miss green ce*_🤙🏿 [23/09, 16:30] Miss Green🍀: 91. . . . . . .92 . . . . . . .nunawa na yi kamar bansan abinda suke ba,na yi wuce wata gaba zuwa wajsn masoyi na,fuskata Ɗauke da murmushi,wani irin kallo me cike da soyayya ya ke yimin yadda yaga na komar kamar Ƴar shekara goma yarinta na ta Ƙara fitowa sosai,ga wani irin mugun Ƙamshin dana ke fitarwa me gigita namiji,ai kuwa shahid ya gigice Ɗin sosai amman duk da haka hankalinsa na kan Bilal wanda ya Ɗaga iman sama yana yi mata wasa. Ya ce"hayatee wannan shine baban lovely children Ɗina"?.sosai gabana ya faƊi ahankali na ce"eh shine na manta ban faƊa maka ba,yaya ya ke gare ni".sai naga fuskarsa ta haƊe nan da nan,na lura shahid shima namijin kishi ne sosai,daman kuma ance larabawa sunfi kowa kishi. Ya ce"ayya kada ki damu don na tambaye ki ki yi haƘuri,amman wannan yayan na ki wata macece za ta ce bata sonshi?babu abinda Allah bai yi Masa ba,amman na yi mamakin rabuwarku,kuma kema khairat nasan ba zai so rabuwa da ke ba,sai dai Ƙaddara amman duk namijin daya sakeki khairat wallahi ya yi asara gaskiya". Murmushi kawai Na yi don bani da amsar da zan bashi,don kada yabi inda muke sai ya Ɗauki Ƴarsa suka yi gaba abinsu.Ina jinsa yana tambayarta Ƴan uwanta,sai kuwa iman ta ce"dady mamanmu ta Ƙara yi mana wani dadyn ka ganchi cen ma".ta fara nuno inda Muke.Bilal bai san lokacin da wasu hawaye masu zafi suka fara zubo masa ba ya yi saurin gogewa ya wuce. to ranar dai da Ƙer shahid ya barni na wuce gida na lura bai gajiya da kallona,idan na biye masa kuma sai muyi ta tsayuwa awajen,don haka na ce"habibee ni zan tafi gida fa mun daƊe".na faƊi hakan cikin shagwaƁa,sosai na burgesa ya ce"ah lallai baki so kije gida yanzu,ni wannan shagwaƁar taki tafi komai tafiya dani",yauwa khairat ki yi haƘuri ni dinner bata cikin tsarina sam,duk kuwa kuƊin da na ke dashi,amman mu al'adarmu a musulunce shine bayan anyi aure ana walima washe gari,to ni dai hakan yafi Ƙwantamin". murmushi na yi sannan na ce"kada Ka damu nima duk wannan bidi'ar bata gabana albarkar auren shi na keso".sosai na burgesa amman fa muna cikin zancen naji alert Ɗin kuƊi awayata na ce"habibee naga ka turomin kuƊi me zanyi dasu haka"?.murmushi ya yi sannan ya ce"ki yi wani abin dasu,amarya ta me sirrin kyau".ya faƊi hakan
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87