Chapter 34
Chapter 34
ta yi,kowaccs mata agidan so take Bilal ya ce yana son ƴaƴansu amman shi ya yi kunnrn uwar shegu harkokinsa kawai ya ke. To wannan maganar sosai ta hargitsa ƙwanyar ƴan gidanmu,musamman ma waɗanda daman ba so na suke ba,daga ni har mahaifiyata su mama iklima dukkansu jikinsu ya yi sanyi,wato ita wannan yarinyar duk muguntar da suka yi mata,ƙarshe sai dai ta zamo mata alkhairi,inji masu iya magana suka ce hassada ga mai tabo taki ce. Daga ni har mahaifiyata babu wanda yasan wannan maganar,saboda tunda mama tazo ko hirar ƴan gidanmu ba ballan tana ma har muji komai. Yaya Aliyu kuwa yasan komai don Baba Abdullahi ya kirasa ya faɗa masa komai,sannan ya ce kada a sake a gayawa ita khairat ɗin gaya mata kamar zai janyo wata matsalar,sannan suma ƴan gidanmu duk iyayenmu sunja musu kunne sosai akan kada a faɗawa Bilal har sai an ɗaura aure. **** "yanzu kai mukhtar saboda wannan lalatacciyar yarinyar ka ke kuka?yarinyar da agidannan har ciki ta yi shine don na ce baza ka aure ta ba,shine yanzu zaka sakani agaba kana kuka kamar wani yaro?"To wallahi ka buƊe kunnuwanka da Ƙyau ba zaka auri wannan yarinyar ba irin tsiya irin inyamurai,ni banda ma ubanka da ubanta ciki Ɗaya suke me zaisa ma in haƊa iri dasu,Kaji dai na faƊa maka don ni na tsani haƊa aure irin na kakarku ta haƊa kara da kishiya waje Ɗaya azo ayi ta masifa to ni haƊin nan ba dani ba,don haka ka maida hankalinka,bara'atun ma da ta liƘe maka ta yi ta gama don babu Ƴar da zaka aura ehe kaji dai na faƊa maka".tana faƊar hakan ta yi gaba abinta. Sosai mukhtar yaji haushin wannan mummunan zagin da mahaifiyarsa ta kewa sahibarsa khairat,sam ko a mafarki ba zai yarda ce wa khairat za tayi cikin shege ba,sai gashi ana yi mata Ƙazafi da ta yi ciki,tabbas zaiyi amfani da aikinsa na lauya ya tsaya tsayin dafi akan wannan Ƙazafin da aka yi wa baiwar Allah. ****** "yanzu Alhaji Ɗan na wa ne zai auri wannan yarinyar wacce ta zubar da mutuncinta tun awaje har ta Ɗakko ciki,shine ni za'a laƘabawa Ɗana ita saboda anga bai damu da kowa ba". "Hajiya RuƘayya haƘiƘa zanyi miki abinda baki taƁa zata ba,idan ki ka Ƙara ce wa khairat ta yi ciki?me yasa ku mutane arayuwarku kanku kawai kuka sani?muƘaddara ma hakan ya faru?ita sai aƘi aurenta saboda wannan?mata nawa ne suka yi cikin shege agidan iyayensu har suka haihu kuma hakan bai sa an sakesu ba?sai ita za'a ce baza a aureta ba?no possible ace kuma Ɗan uwanta bazai rufa mata asiri ba?abinda zan gaya miki shine,duk ranar da ki ka Ƙara zagin khairat kisan da ce wa zaki yi nadamar da baki taƁa tunani ba kinji na gaya miki,ruwan ki kiso auren ruwanki kiƘi so?"yana faƊar hakan ya yi fitarsa cikin tsananin fushi. A tun rayuwar aurensu Abdullahi bai taƁa fushi da ita irin na yau ba,sam bai da faƊa ko hayaniya mutum ne shi mai tsananin haƘuri kafin kaga abinda zai saka shi fushi ana daƊewa,daƁar ta zauna akan kujera wacce take tree seater azuciyarta tana tunanin ta yadda za'ayi wannan auren alhalin ranta bai so. ****** Na fara zuwa makarantar jami'a Ado bayero university kano,ina karantar fannin law(lauya),ban taɓa tunanin zanyi ƙoƙari kamar yadda na ka yi yanzu ba,saboda halin dana tsinci kaina har yanzu babu wanda ya faɗamin zancen aure na da yaya Bilal ko awajensu Rashida ban tsinci zancen ba,ga mama da muke tare itama bata sani ba ko abakin su yaya Salim kuma babu wanda bai san zancen acikinsu ba. Muna zaune a aji muna ɗaukar lecture,wata ƙawata Salima ta ɗan buge ni kaɗan ta ce"hmm Rahma ga fa mutumin ke nan?wallahi yana matuƙar burgeni sosai,handsome dashi". Banza na yi mata don ni sam hankalina baya wajensa yana kan wani note dana ke dubawa,ƙamshin turarensa yasa na ɗago don ƙamshin turarensa sak dana yaya Bilal. Ina ɗagowa muka haɗa ido dashi kyakkyawa ne sosai ba laifi,sai dai ko kaɗan bai kai yaya Bilal ba,na rintse idanuwa na ina jin zuciyata tana ƙuna sosai don tuno da yaya Bilal,na yarda ayanzu a tunanin yaya Bilal akashi ɗari yanzu babu goma aciki saboda yadda mama take ƙoƙari sosai akan in rage tunanin ko da kaɗanne. Hankalina yana cen kan tunani wanda na ƙwana biyu banyi ba,sosai ya ƙurawa khairat ido kamar zai cinye ta,yarinyar tana matuƙar burgesa sosai yana son mutumin da bai damu da duniya ba,wanda babu ruwanshi da tashin hankali so silent,bai taɓa tunanin zai auri mace mara mutunci irin matarsa ba,ga shegen surutu kamar aku amman kuma bata taɓa ganinshi da gemon arziƙi ba,idan kaga tana wani lallaminshi to tana son yin wani abu da kuɗine to zai ga kalolin tarairaya kala kala. Yana cikin tunanin monitor ɗin ajin ya shigo yana ta yi mai magana amman baiji ba,hankalinsa yana kan kallon khairat sai da monitor ɗin yaɗan buga desk ɗin sannan ya dawo cikin hankalinsa,duk kunya ta ishesa khairat ɗin ma hankalinta na cen tunani bata ma san wainar da ake toyawa ba,Salima sai dariya take ƙasa-ƙasa taɗan bangaji khairat ɗin sannan itama ta dawo cikin nutsuwarta,duk ɗagowarta sai sun haɗa ido dashi ta takura sosai tana addu'ar ya fita ko ta huta da wannan kallon. Ina dawowa daga makaranta naga yaya Aliyu da yaya Salim harda maher muka gaisa dasu hankalina na kan mama don ban jiyo muryar ta ba,ina zuwa falon naji tsit babu sai ƙarar tv dake kunne,abin ya bani mamaki don nasan mama afalo take zama gabana ya yanke ya faɗi,to ina mama taje?babu mai bani amsa don haka kai tsaye na shige ɗakinta wanda take ƙwana da ita da kakarsu. Sosai ta yi mamaki gani babu kowa,sai taji kanta har ya fara sara mata tabbas uwa ta dabance tunda mamana tazo bata taɓa barina ni kaɗai na yi tunanina ba,hankalinta na kai na tana bani labarai kala-kala ni kuma inyi ta dariya. Ina cikin wannan halin suka shigo,sai naji duk haushinsu na ke ji kamar su suka suga mama ta tafi,ana cikin hakan Anty khadija ma ta fito,ta wani kalleni ta watsar Khairat na hannunta. Yaya Aliyu ya ce"khairat sai kiga mama ta tafi ko?ki yi haƙuri lil sis bata son ki sani ne shiyasa ta tafi amman ta ce zata dawo ƙwanan nan."waau hawaye ne suka fara zubomin ina kukan na ce"wayyo mamana!yanzu waye zai dinga rarrashina ?mamana tana da lokaci na,bata son in shiga wani hali".sai na fashe da kuka kamar ƴar yarinya. Yaya Salim ya ce"haba khairat kamar wata ƴar yarinya insha Allah mu zamu dinga rarrashinki kamar mama tananan".ya faɗi hakan yana ɗago haɓata wadda ta gama jiƙewa da ruwan hawaye. Cire hannunsa na yi daga kan haɓata na ce"a'ah yaya Salim ba zaku iya kula dani kamar mama ba,ku mazane dole ko ta wajen ƙwanciya bacci zamu rabu,amman mamana har baci muke tare da ita,ni dai wajen mamana kawai zan koma". Na faɗi hakan ina kukan shagwaɓa Maher ya ce"kai anty khairat jibe kifa ƙatuwa dake kina wani kuka harda shgwaɓa ni idan na kula ma harda majina".?ya faɗi hakan cikin sigar zolaya. Da gudu na tashi na fara dukansa yana karewa da fillon kujerar,ni kuma ina
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87