Chapter 15
Chapter 15
ta ce"hmm kyaji dashi dai da kin gansa sai ki kama wani rarraba idanuwa kamar mujiya yo sojan har wani abu ne da zaki dinga tsoronsa haka?Ni fa kakanku nasha yi masa kuka akan ya kaini barrek Ɗinsu don a tafi filin daga dani saboda rashin tsorona,yo me aka yi aka yi wani soja". baiyi niyyar dariya ba amman sao da ya yi ya ce"to ke hajiya idan akaje naushi Ɗaya za'ayi miku ki baje awajen". ni dai raƁewa na yi a gefe kamar wata munafuka ya buga min wani banzan kallo sannan ya ce"ke tashi ki fita ni sa'anki ne da zaki zauna kina kallon bakina ina magana,comon dalla tashi ki fita Ƙazama kawai me shegen kallo kamar mayya". *Miss green ce* *GAWURTATTU BIYAR,5🤚TAFIYAR TA MUSAMANCE* 1, *MU GANI A ƘASA..🔥* _Ummu Affan_ 2, *ABIN CIKIN ƘWAI..🥚* _Ummu Maher_ 3, *GUNTUN GORO..*💥 _Mom Islam_ 4, *GISHIRIN ZAMAN DUNIYA*🌎 _Mrs Bukhari_ 5_ *AUREN WATA TARA👩❤️👨* _Miss Hajo_ Guda ɗaya N300 Guda biyu N500 Guda uku N600 Guda huɗu N700 Guda biyar 1k *ZAKU TURA KUƊINKU TA WANNAN HANYAR👇* Fatima Rabiu Sunusi 0037219728 StanbicIBTC Bank. Shaidar biya tanan 👇 0810 433 5144 Masu tura katin MTN👇 0814 179 9224 ...........🥚👩❤️👨💥🌎.... *ƳAN NIGER GA HANYOYIN BIYAN KUƊINKU👇 Guda biyar 1000f Guda huɗu 700f Guda uku 600f Guda biyu 500f Guda ɗaya 300f Kai tsaye ku tura da katin Airtel ta wannan number👇 +227 84 50 64 76 *MUN GODE DA KASANCEWA DA GAWURTATTU TAKUN FARKO* [23/09, 16:17] Miss Green🍀: _*🥚ABIN CIKIN ƘWAI...!*_ 📃Littafi na 1 By🪶 *Ummu maher(Miss green)🍏* *GAWURTATTU 5* ----------------------- *Wattpad user name* https://www.wattpad.com/user/Rabiatu333 ------------------------- *Arewa book user name* https://arewabooks.com/u/rabiattu0444 ---------------------- masu buƙatar talla 2k Ne,zamu dinga Ɗora muku a dukkanin shafukanmu a kowani social media don samun costumer cikin sauƘi. *Sirrinmu* Manzon Allah(S.A.W)ya hanemu da cin naman mutane,ma'ana gulma ka yi gulmar mutamin da baya wajen Allah ya tsaremu amin. ----------------------- 13🟦14 ........sosai sukayi mamakin kalamin kakar ta su,wai su za'a mayar ƴan aiki ko kuwa?bata ƙara kallonsu ba ta yi wucewarta,don ta yi alƙawarin sai ta koya musu hankali har kuka sai da ta yi don jin abinda jikokinta suke ai'katawa. Washe gari a babban farlon gidan aka haɗu na cin abinci ƙaton teburine wanda ake haɗuwa duka family aci abinci don ƙara zumunci,kowa ya yi tsit baka jin ƙarar komai sai ƙarar cokali,wasu suna ci amman kamar suna cin kashi don hankalinsu a tashe ya ke da wannan haɗuwar wasun kuwa ba wasu bane illa su Nadiya,iman,samira,unaisa,khalisat,intisar,raudar,amina. Duk hankulansu a matuƙar tashe ya ke don sun san har wanda bai san abinda sukayi ba to yau sai ya sani don wannan kakar tasu sai ta faɗa. "To kunyi zungui zungui kuna kallona kamar baku sanni ba?to daman mun haɗune anan don wani gangarumin taro,don haka kowa ya buɗe kunnuwansa yaji." Kowa kallon kaka ya ke saboda sun san aƙwai wata a ƙasa aƙwai wanda ya ke da rabon shan wulaƙanci shiyasa kowa ya kama bakinsa daga su har iyayensu,itama kakar kallonsu take azuciyarta ta ce yau kowa sai ya gane kurensa don wallahi baza'a janyo musu ɓarna har acikin gidansu ba. Su kuwa ƴaƴanta babu wanda baisan abinda kaka za ta faɗa ba,don jiya da daddare sunyi meeting akan hakan,Hajiya kaka ta kalli Baba Abdullahi ba tare da ta ce komai ba,sanin abinda take nufi ne ya yi gyaran murya ya fara jawabi kamar haka. "Abisa yarjejeniyar da muka yanke tsakaninmu da mahaifiyarmu mun ɗaukar mata alƙawari kuma ayau zamu cika mata shi,ba neman shawarar kowa muke acikinku ba a'ah saboda haƙƙin kune a faɗa muku,mun yanke shawarar haɗa aure ga ƴaƴanmu don ƙara ƙulla zumunci." gaban jikokin na su ne ya yanke ya faɗi karma ace maka su Nadiya sukayi tsiru suna kallon iyayen na su don jin waɗanda aka haɗa auren,ko har dasu oho?kai har dasu ɗinma tunda dai sune ƴan matan gidan,tuni cikinsu ya bada sauti ƙuuu alamun gudawa. Baba Abdullahi ya cigaba da ce wa"to mun yanke shawarar gaɗa,Aliyu aure da Nadiya".zaro idanuwansu sukayi waje daga Aliyun har Nadiyar. "Salimat kuma da Abbas,Amina da munir,khalisat da Sadiƙ,intisar da Hafiz,iman da Irfan,unaisa da maher,samira kuma da Arman." dukkansu tashi sukayi tsaye suna kallon ikon Allah don basu taɓa tunanin wannan abin ba unexpected.babu wanda ya basu damar ce wa komai Baba malik mahaifinsu Khairat ya ce"mun saka ranar aure nan da wata biyu masu zuwa,dukkanku bama neman wani abu daga hannayenku duk abinda ya kama zamuyi sauran abubuwa ku tuntuɓi iyayenku".yana faɗar hakan ya tashi ya ce"to ni zan tafi wajen aiki ina da meeting sai anjima ".ya yiwa ƴan uwansa sallama da mahaifiyarsa sannan ya tafi. Kallon juna aka shiga yi a babban farlon musamman waɗanda aka haɗa auren,gabansu sai faɗuwa ya ke acikinsu aƙwai waɗanda basu damu ba da haɗin da akayi musu amman fa Nadiya tafi shiga cikin tashin hankali don ita gani take ma kamar baza ta iya zaman auren ba. Bayan taro ya tashi ko wa da abinda ya ke saƙawa acikin zuciyarsa,Rashid ta kalli Khairat cikin tsokana ta ce"to ikon Allah yanzu fa agidannan mune muka zana gwauraye don kowa da mijinsa".nima ƴar dariyar na yi sannan na ce"gaskiya wannan haɗin ya yi min sosai wallahi kinga ni daman su Nadiya na ke tunanin amman kinga yanzu rayuwarsu za ta inganta kuma yaya Aliyu mutunne mai mutunci da karramawa."Rashida ta yi min sannan ta ce"wai kina nufin daman Nadiya da Aliyu aka haɗa?".saurin ɗaga mata kai na yi alamar eh.hawaye naga yana fitowa a idanuwan Rashida na ce"a'ah me ya faru kuma"?. ruƙo hannuwa na ta yi duka biyu muka shiga ɗan lungu da ke manne dana kaka,a hankali cikin siririyar murya ta ce"Khairat muna soyayya da yaya Aliyu fa?".da sauri naja ɗan baya na zaro idanuwa na waje alamar tsoro. tausayi ta bani sosai a zuciyata kuma ina tuna girman zurfin cikin ita Rashidan da ko ni ban taɓa sani ba,a hankali na ce"haba Rashida gaskiya kinyi kuskure ba kaɗan ba wallahi,ko ni baki taɓa gayawa ba?ballan tana ma in taimaka miki ta wani ɓangaren,kin san yanzu kan iyayenmu a haɗe ya ke kada azo ayi abinda kansu zai rabe,kin san kawu Auwalu matarsa ta fi ƙarfinsa sai yadda ta yi dashi gashi kuma basa shiri da Mamanku kinga hakan kamar zai janyo wata matsala fa"?. "Na sani Khairat amman wallahi mundaɗe muna soyayyarmu daman munƙi bayyanawa ne sai har mun gama makaranta. Kasa ce wa komai na yi cen dai na ruƙo hannuwanta duka biyu na ce"Rashida aduk halin da zaki shiga bazan taɓa gudunki ba ina nan tare da ke,tun daga kan wasan ƙasa har zuwa yanzu munanan tare babu wani mahaluƙin da ya taɓa shiga tsakaninmu don haka kinga yanzuma dole in tsaya kaida ƙafa inga wannan al'amarin ya dai daita". Kamar daga sama mukaji ana ce wa"ya dai dai ta ma ai".muryar kaka mukaji ta nufo inda muke ta ce"munafukar yarinya au ke yanzu daman kina son gadanga ƙusar yaƙi kika ƙi magana sai yanzu".?ƙada da kai Rashida ta yi tana zubarda hawaye tausayinta ya ɗarsu a zuciyar Hajiya kaka ta ruƙo hannun Rashida suka nufo ɗakin kaka Yaya Aliyu yana zaune akan kujerar kaka wadda aka zuba mata ƙwanannan kansa a ƙasa idanuwansa sunyi jawur kamar harda kayan aikinsa ma ajikinsa ba
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87