Skip to content

Chapter 46

Chapter 46

Abin Cikin Kwai Book One Complete Hausa Novel 1,286 words 0 views Progress saved
Download Book

don ba nida wata amsar da zan bata,don na fitar azuciyata ce wa na cire tsammanin wai wataran Yaya Bilal zai soni kamar yadda na ke sonshi. "Yauwa gobe ne fa hutunki zai ƙare amarsu don wallahi nida zee munyi matuƙar missing ɗinki sosai,mutuminki ma sir Deen sai tambayarki ya ke muka ce masa ai kin riga da kinyi aure,wallahi ina baki labarin har kuka sai da muka laɓe mukaga yana yi,kai ni da zee munga abin mamaki." "Hmm" kawai na ce don ni yanzu ban ma san yadda za'ayi da makarantar ba. ina gama cin abincin na tashi na fita duk jikina asanyaye,sun daɗe da dawowa don haka kai tsaye na wuce sashen Jidda,suna zaune afalo suna kallo Jidda ta jingina da kafaɗar Yaya Bilal na yi sallama na shiga. Gabana ya bada wani rassss,kaɗan ya rage zuciyata ta buga,dukkansu wani kallo suka bini dashi,cikin sarƙewar murya na fara gaishesa,wani banzan kallo ya yi min sannan ya cigaba da shafa kan jidda kamar me yi mata shafa. Da ƙer na buɗe bakina sannan na ce"daman Yaya Bilal ina son ka bani izini gobe zan koma skull ne". Ko kallon ƙura ta bai yi ba,sai da ƴar gaban goshin nasa ta ce"honey kace ta fitar min a ɓangare na wallahi wari take... .✍🏿 07068606171 *GAWURTATTU BIYAR, TAFIYAR TA MUSAMMAMN CE. 👯‍♀️👎👇👇* 1, *MU GANI A ƘASA...*🔥 _Ummu Affan_ 2, *ABIN CIKIN ƘWAI..*🥚 _Ummu Maher_ 3, *GUNTUN GORO..*💥 _Mom Islam_ 4, *GISHIRIN ZAMAN DUNIYA*🌎 _Mrs Bukhari_ 5, *AUREN WATA TARA*👩‍❤️‍👨 _Miss Hajo_ Guda biyar 1k Guda huɗu N700 Guda uku N600 Guda biyu N500 Guda ɗaya N300 *DOMIN TURA KUƊIN KAI TSAYE*👇 0037219728 Fatima Rabiu Sunusi StanbicIBTC Bank. Domin tura shaidar biya👇 0810 433 5144 Masu tura katin MTN👇 0814 179 9224 Ƴan Ƙasar Niger zasu tura nasu anan.👇 0817 952 3215 Guda biyar 1000f Guda huɗu 700f Guda uku 600f Guda biyu 500f Guda ɗaya 300f *TEAM GAWURTATTU BIYAR TAKUN FARKO TAFIYA TA MUSAMMAN.* 🔥🥚💥🌎👩‍❤️‍👨 _*Miss green ce*_🤙🏿 [23/09, 16:23] Miss Green🍀: 51. . . .52 . . . .tsananin mamakin wulaƙancin jidda yasa na kasa koda motsawa,sosi maganar jidda ta daki zuciyata,wato ma nice na ke wari?lallai jidda tazo da abinda bazan ɗauko ba. Kallon ƙasa na yi wa jidda kafin Bilal ya buɗe bakinsa ya yi wata magana,cikin fushi na ce"jidda haƙiƙa ke acikin mutane ta dabance shiyasa kike ganin kanki kamar wata sarauniya,to ki sani dama ɗaya ce arayuwar ɗan adam,idan kuma ka bari ta wuce ka to ta wuce ka har abada,don haka ki taka asannu2 duniya ce tafi bagaruwa jima daɗi". Ina faɗar hakan na fita da sauri daga ɓangaren,zuciyata tana ƙuna sosai wato yau nice na ke wari awajen jidda?yarinyar da da kuɗina nasha biya mata kuɗin watan makarantar islamiyya,wai yau ita ce ke kira da me wari.na faɗa sashe na ina wani irin kuka mai cin rai,tabbas idan waɗannan abubuwan suka cigaba da faruwa to tabbas barin gidan nan zanyi,don naga alama yaya Bilal so yake ya sakamin ciwon zuciya don gab take da ta buga ƙarshe kuma inyi wa iyayena asara,don ko kusa nasan yaya Bilal ba zaiji ciwon mutuwa ta ba tunda ba damuwa ya yi dani ba. Ina fita jidda ta kalli Bilal wanda kansa ke wajen system ɗinsa,yana shigar da wasu bayanai akan Damas,sai kuwa jidda ta saka idanuwanta sosai,ta ɗauki wayarta ƙirar iphone,ta ɗauki hoton abinda Bilal ya ke,ganin ya juyo yasa tayi saurin ajiye wayar don kada ya ganta. Ya ce"jidda bana son kina biyewa wannan yarinyar,don sam ni bana sakata acikin masu hankali shiyasa ma kika ga ban kula ta ba,don ko kallon inda take bana son kalla".sosai jidda taji daɗin hakan ta ƙwanta a faffaɗan ƙirjinsa tana shafa sa ahankali cikin kissa irin tamu ta mata ta ce"hmm shiyasa darling kaga ko kallonta banyi ba.don warin jikinta ma ya ishi mutum". Wayarsa ce ta fara ringing ya ɗaga yana ce wa"Ahmad lafiya dai ko?dan kasan idan ina tare da iyalina bana san kowa ya shiga sabga ta".? Dariya captain ya yi sannan ya ce"ikon Allah masu mata manya,to idan banda abin ka yaushe ne ma kayi auren?".ya faɗi hakan yana dariya ya ce"to ka fito waje nazo inason yin magana da kai?idan madam ɗin ta bari sai ka fito,Angon Hauwa da khairat".wannan magana ta ƙarshe da captain ya faɗa ita ce tafi tsayawa jidda ta kalli wayar ji take kamar taje ta shaƙe Ahmad ta cikin wayar don Allah ya gani ta tsanesa. Bilal bai ce komai ba ya fita tare da janyo jidda ya yi mata wani irin hot kiss sannan ya fita,ta tsaya kamar tabi sa taje ta shaƙe wannan captain ɗin,sam ta tsani taji an danganta wata mace da Bilal don son da take wa Bilal,tare da matsanancin kishinsa. "A'ah kaga angon mata biyu har ka fito?".Banxa Bilal ya yi masa sannan ya ce"kaga mlm faɗi abinda ya kawo ka?kawai ina cikin nishaɗi na da matata ka wani zomin?sai kace gauro,ƙarfe nawa yanzu?". Sosai captain ke dariya harda riƙe ciki,Bilal cikin jin haushinsa ya ce"au daman iskanci ne ya kawo ka?to maza zo ka tafi wallahi".gimtse dariyar ya yi don yasan mutuminsa aƙwai shi da saurin fushi. Haɗe rai shima captain ɗin ya yi sannan ya ce"to akoma bakin aiki yanzu,kana sane da abubuwanda suke faruwa kuwa?a game da Alhaji Damas?na yi bincike sosai na gane tabbas aƙwai wanda ya ke naɗar duk wani sirrinmu yana kai masa,don a yanzu duk wani plan da muka haɗa masa yasan komai". "A'ah mlm daga ni sai kai muke wannan binciken,sai dai idan kai ne kake kai masa to sai ka faɗamin"?. "ah haba mutumina ta yaya za'ayi in haɗa kai da wannan mutumin?kar ka manta fa Damass shine ya yi sanadin mutuwar ƙanwata,shine ya sace ta ya tafi da ita ƙarshe ya kashe ta,duk dalilin taƙi aurensa,saboda munanan aikinsa,kuma ta yaya kake tunanin hakan daga waje na,no matter how hakan ta kasance,ni dai abu ɗaya zan faɗa maka shine aƙwai na kusa damu wanda ya keson ya san komai,sannan ya ruguza mana plan wanda muka daɗe da gama kayanmu". "hmm zan duba maganarka captain,amman gaskiya ina mamakin wannan waye kuwa"?. "Hmm Bilal kenan aishi makashinka yana tare da kai,don haka gwara ma kawai musan abinyi yanzu,kada mu tsaya kallon kifi kwaɗo ya yi mana ƙafa." bayan sun gama wannan maganar ne captain ya ke faɗa masa matarsa zata zo gidansa gobe. Bilal ya ce"ok Allah ya kawo ta lafiya".amin captain ya ce sannan suka cigaba da hirarsu. Sosai na ke kallon yaya Bilal wanda ke ta dariya kamar ba shi ba,ina kallonsa ta sama window ɗin ɗaki na,Ina ji araina dama dani yake wannan hirar,yau da har sadaka sai na yi saboda murna,amman kash!ba dani ya ke ba. Na saki labulen ɗakin na zauna abakin gadona ina tunanin irin wannan zaman dana ke,sai kace wani auren ƙwangila?ah to idan ma auren ƙwangila ne ai da sauƙi tunda dai ana kula da matar?amman ni ina nan dai zaune kamar wata gunki,ko kallon arziƙi ban taɓa samu daga wajen me gidan ba. **** Ƙarar wayar jidda ne ya karaɗe wajen,tana sama kan bene tana wanka,Bilal na kusa da wayar ya shiga kiranta da honey!honey!!amman jidda bata ma san yana yi ba,ya ɗaga wayar don ya bada

Table of Contents

Chapters

87 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87