Chapter 61
Chapter 61
tashi,Bilal ya nuna takaddar shaidar aikinsa..da sauri suka amshi mahaifin Bilal saboda sanin waye Bilal ɗin,aka fara taimakon gaggawa. Ya samu waje ya zauna cikin ɗaya daga cikin kujerun da aka ajje awajen don zama,ya riƙe kansa wanda ya ke shirin tsage masa gida biyu,saboda masifar da ya ke ciki,ga sakin da ya yiwa Khairat har yanzu yana jin abin aransa. ga kuma kamata da ya yi da ƙwarto,bayan haka kuma ga abinda ya faru da mahaifinsa. ******** kai tsaye sashen Hajiya kaka muka yi nida Yaya Aliyu,da kayana wanda Rashida ta ɗebomin agidan Bilal wanda akan wannan kayan sai da akaso faɗa da Jidda wai Rashida baza ta shiga ba,ai kuwa ta bangaje ta,ta shige ta ɗebo kayan. Muna zuwa Hajiya kaka ta miƙe tana ce wa"a'ah Abin cikin ƙwai lafiya nags hannunki harda bandeji"?.Yaya Aliyu ya ce"ba tada lafiya ne kaka".muka samu waje muka zauna da ƙer na zauna saboda hannun nawa,gashi ƙasan mara ta yanzu wanda ya yimin kamar dutse kuma ina jin wajen kamar dutse,ga wani motsi da ya kemin,ina jin tsoron hakan don tun ƙwanaki na kejin wannan motsin wajen wata biyu,wannan masifar dana shiga ita ce ta saka na manta da wannan motsin dana keji. Babu abinda yaya Aliyu ya ɓoyewa Hajiya kaka tun farko har yanzu,Salati kaka ta yi sannan ta ce"yanzu Bilal ɗin da kansa ne ya yanke wannan ɗanyan hikuncin?tabbas aƙwai wani wanda ya haɗa wannan abin,amman babu komai aƙwai Allah khairat shine zai shige mana gaba". *MU GANI A ƘASA...*🔥 _Ummu Affan_ 2, *ABIN CIKIN ƘWAI..*🥚 _Ummu Maher_ 3, *GUNTUN GORO..*💥 _Mom Islam_ 4, *GISHIRIN ZAMAN DUNIYA*🌎 Badi'at Ibrahim _Mrs Bukhari_ 5, *AUREN WATA TARA*👩❤️👨 _Miss Hajo_ Guda biyar 1k Guda huɗu N700 Guda uku N600 Guda biyu N500 Guda ɗaya N300 *DOMIN TURA KUƊIN KAI TSAYE*👇 0037219728 Fatima Rabiu Sunusi StanbicIBTC Bank. Domin tura shaidar biya👇 0810 433 5144 Masu tura katin MTN👇 0814 179 9224 Ƴan Ƙasar Niger zasu tura nasu anan.👇 0817 952 3215 Guda biyar 1000f Guda huɗu 700f Guda uku 600f Guda biyu 500f Guda ɗaya 300f *TEAM GAWURTATTU BIYAR TAKUN FARKO TAFIYA TA MUSAMMAN.* 🔥🥚💥🌎👩❤️👨 Instagram links👇 https://www.instagram.com/p/CgPTv1-oML6/?igshid=MDJmNzVkMjY= Facbook group https://facebook.com/groups/463653111781414/ Telegram links https://t.me/+xYZCR9JY-aMzNDFk *YADDA AKE BUƊE ACCOUNT A AREWABOOKS* Bayan kaje play store ka ɗakko ya sauka a kan wayarka. Za'a cike Form ɗin kamar haka: - *Enter your name:* (Cikakken sunanki) *Enter your mail:* (Email ɗinki) *Enter an username* (Sunanki) *Enter your password:* ( misali 12341234) *Confirm password:* (misali 12341234) Sai a taɓa *Sign Up* shikenan an buɗe account a ArewaBooks💃🏻😂. *Continue with Google* - Idan kana da gmail/email akan wayarka kawai Continue with Google za'a taɓa zata buɗe maka account a ArewaBooks kaitsaye. *Register* - Shine cike form domin buɗe account a ArewaBooks. Masu iPhone Zaku iya bibiyar shafinmu https://arewabooks.com MISS GREEN CE [23/09, 16:29] Miss Green🍀: *🏮ABIN CIKIN ƘWAI🏮* littafi na 3 *by✍🏿* Ummu maher(miss green)🍀 Wattpad user name Rabiatu333 Arewabooks rabiattu0444 *Sirrinki👂🏻🌈* ki kasance mai yawan yin sadaka da kuma istighfari,yin hakan zai Ƙara kusanta ki ga Allah mahalaccinmu,don haka ƴan uwana mu yawaita yin sadaka. -------------------------------- 79. . . . . 80 . . . . ."Wallahi ƙarya ya ke yimin,ni ban aikata hakan ba".?da sauri Anty kishirya ta ce"Hajiya Iklima ki yarda kawai munyi,kin san kece da kanki ki kaje wajen boka ki ka amso maganin da khairat za tayi ta zubar da jini a ɗauka ta zubar da ciki ne,don haka gwara ki faɗi gaskiya ki zauna lafiya". Da sauri Hajiya iklima ta rirriƙe ƙafar Babanmu tana ce wa"don Allsh Alhaji ka yafemin wallahi sharrin zuciya ne. . . "Bau barts ta ƙarasa ba cikin fushi ya ce"Iklima kin cuce ni kuma kin cuci kanki da ƴaƴanki,ban taɓa zaton hakan daga gurinki ba,kin sa na tsani ƴata tsana mafi muni,sannan kuma na saki matata wacce na kesonta,so me tsanani,ita ce farin ciki na ni kaɗai nasan yanzu halin dana ke ciki idan na buɗe idanuwa na ban ganta kusa dani ba.yanzu duk wannan bai isheki ba Iklima keda ƴar uwar rashin kirkin naki?.ki sani ayau zan sallameki bazan iya xama da me mugun hali irinki ba,Allah shine zai yimin sakayyar duk abinda ki ka yimin". Da sauri Hajiya kaka ta ce"a'ah malik kada ka ɗauki saki abu na wasa ka yi tayinsa kamar jahili,tabbas zama da waɗannan babbar annoba ce,amman ka barsu ko zaman ƴaƴansu sunyi,kada ƴaƴanka su zauna babu iyaye". Da sauri Malik ya juyo ya ce"in barsu fa umma?sam bazan iya zama dasu ba tsakanina kuma dasu sai dai ince Allah ya isa,Allah shine zai ƙwatarmin hakkina,yana faɗar hakan ya ce"ke daman Iklima aƙwai saki ɗaya akanki,don haka yanzu na cika sa ya zama uku,ke kuma na sakeki saki uku,kuma daga yanzu kada na ƙara ganin ƙafafuwanku a gidana tunda ba gidan ubanku bane". Sosai Ɗakin ake kuka su mama iklima,da ƴaƴansu sai Jidda wadda ke kuka kamar ranta zai fita,Bilal ya cilla mata wata takarda ya ce"wannan takardar sakinki ce,amman kafin ki tafi gida zan kira iyayenki suzo suji itin laifin da ki ka yi".kuka sosai take tana bashi haƙuri amman ko kallonta baiyi ba. Hafsat da mijinta bayan sunje gidan Bilal babu kowa sai ta juyo ta ce"kasan gidan iyayenshi ne?".da sauri Hanza ya ce eh na sani".ta hararesa ta ce"to maza muje".ai kuwa da sauri ya shiga mota suka tafi. Suna zuwa aka yi iso wajen Bilal,Bilal ya fito don ganin waye?yana hango Hamza ya ce"ok ashe ka kawo kanka ma maci amana,butulu maci amana ƙasa".Hafsat ta sunkuyar da kanta ƙasa kamar za tayi kuka tsabar takaicin abinda mijinta ya yi,ta nisa ta ce"yallaɓai wallahi abinda su Hamza suka aikata haƙiƙa laifine babba,shiyasa na kawo maka shi ka yi masa hukunci dai dai da abinda ya aikata". Bilal ya ce"haƙiƙa kin cika mata tagari abar son kowani namiji,don awannan lokacin ba kyaun mace ne burgewa ba,a'ah gaskiya ita ce mafi kyau acikin aure".daga nan ya yiwa sojojin nan fito sai gasu sun fito,suka kama Hamza shima.Hafsat ta saka kanta gaban motar da sukazo da ita ta fashe da kuka me mugun ciwo,tana masifar son mijinta Hamza ta shafa cikinta wanda ya fito sosai wata shida kenan,ta fashe da kuka tana ce wa"Allah sarki ɗana mahaifin ya kasance me cin amanar ƙasarshi,ya kasance mara gaskiya,gashinan yanzu ya zamar da kai maraya don ban san irin hukuncin da za'a yanke masa ba. Ta daure ta shigo babban wajen inda aka shiga dasu Hamza,Hajiya kaka ta ce"Allah sarki khairat baiwar Allah,haƙiƙa Allah baya barin haƙƙin wani akan wani,gashinan tun kafin akai ko'ina Allah ya tona musu asiri,ni kuma da kuke ce wa zaku gama dani,sai dai ku gama da iyayenku don su ya kamata ku gama dasu,don sune suka koya muku mugun hali,da zuciyar rashin imani,don duk wata rashin tarbiyya da yaro ya ke ɗakkowa daga wajen iyayensa ne,mahaifiyar khairat da kullum na ke zagi akan ce wa inyamura ce,to wallahi duk ta fiku tarbiyya saboda ita iyayenta sun koya mata tarbiyya,gaskiya,riƙo da amana,da sauran halaye masu kyau don kuwa gashinan mun gani ko akan jikokinmu don sunfi Ƴaƴanku tarbiyya.shiyasa arayuwa ka auri mace ɓe tarbiyya ma wani abune,muddin ka yi rashin sa'ar mata musamman ma ta farko to za kaga komai ya lalace". Da sauri Su Baba Ƙasim suka haɗa baki wajen ce
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87