Skip to content

Chapter 21

Chapter 21

Abin Cikin Kwai Book One Complete Hausa Novel 1,279 words 0 views Progress saved
Download Book

ce"ke kuwa hajiya kaka me ya kaiki dukan nadiya ai jikinki sai ya yi ciwo,kinga yadda take fa kamar wata ingausa".kaka ta ce"yo ƴar nema ai ta saba da shaƙe ƴaƴan mutane ai dole ta munmurɗe haka,ni dai Allah ya karemin jikana kada wataran ra murɗeshi shima".dariya kawai na saka awajen don hajiya kaka ba dai abin dariya ba,muna cikin haka wayata ta fara ƙara na ɗaga da sallama ta. "Maryam ykk y ƙwana biyu"?.ina jiyo dariyarta ta ce"ke khairat bar wannab zancen wai yau sai ga yaya Aliyu a gidanmu?". *hmmm muje zuwa Fans ba a fara komai ba yanzu salon wasan zai fara Kudai kawai Karku gaji da comment sharhi tare da sharing akwai daddadar tafiya nan gaba* *GAWURTATTU BIYAR,5🤚TAFIYAR TA MUSAMANCE* 1, *MU GANI A ƘASA..🔥* _Ummu Affan_ 2, *ABIN CIKIN ƘWAI..🥚* _Ummu Maher_ 3, *GUNTUN GORO..*💥 _Mom Islam_ 4, *GISHIRIN ZAMAN DUNIYA*🌎 _Mrs Bukhari_ 5_ *AUREN WATA TARA👩‍❤️‍👨* _Miss Hajo_ Guda ɗaya N300 Guda biyu N500 Guda uku N600 Guda huɗu N700 Guda biyar 1k *ZAKU TURA KUƊINKU TA WANNAN HANYAR👇* Fatima Rabiu Sunusi 0037219728 StanbicIBTC Bank. Shaidar biya tanan 👇 0810 433 5144 Masu tura katin MTN👇 0814 179 9224 ...........🥚👩‍❤️‍👨💥🌎.... *ƳAN NIGER GA HANYOYIN BIYAN KUƊINKU👇 Guda biyar 1000f Guda huɗu 700f Guda uku 600f Guda biyu 500f Guda ɗaya 300f Kai tsaye ku tura da katin Airtel ta wannan number👇 +227 84 50 64 76 *MUN GODE DA KASANCEWA DA GAWURTATTU TAKUN FARKO* *miss green ce👉🏼* [23/09, 16:17] Miss Green🍀: *🥚ABIN CIKIN ƘWAI...!🥚* 📃Littafi na 1 By🪶 *®️Ummu maher(Miss green)🍏* _*TEAM GAWURTATTU BIYAR 5🔥*_ *Wattpad user name* https://www.wattpad.com/user/Rabiatu333 ------------------------- *Arewa book user name* https://arewabooks.com/u/rabiattu0444 ---------------------- masu buƙatar talla 2k Ne,zamu dinga Ɗora muku a dukkanin shafukanmu a kowani social media don samun costumer cikin sauƘi. *Sirrinmu* yawan barin jikinmu awaje shine ya ke saka miyagu shiga jikinmu da kuma rashin addu'ah,Allah yasa mu dace baki ɗaya. ------------------- 19🟨20 . ..dukkaninsu kallon Hajiya kaka suke ta ce"to me ye kuma akr kallona kamar na faɗi ba dai dai ba?shi fa Damas ɗinnan ɗan shege ne ma bashi da uba,asalinsu arnan daji ne tun kakarsa ta wajen uwa,uban dai nasa ne ba'asan inda ya ke ba".ta faɗi hakan tana kallonsu.tabbas haka ne mahafiyarsu ta faɗi gaskiya sai dai mutuminne yana da hatsari sosai. Wanene Alhaji Damas? Adamu shine asalin sunansa nahaifiyarsa kuma Sadiya sunanta,asalin Damas ɗin sunansa ya haɗa dana mahaifiyarsa,ya taso da sonta sosai sai dai baiyi rayuwa da ita mai tsayi ba,aka shigo har cikin gida aka kasheta kisan wulaƙanci,sai dai ba kowane ya janyo mata wannan kisan wulaƙancin ba sai ɗanta Damas faɗa ne ya haɗashi da wasu miyagun mutane kuma ya cucesu akan harkar don haka suka ɗauki wannan mummunan matakin,don mutane ne marasa imani sosai tun daga mutuwar mahaifiyarsa shikkenan wani rashin imani yazo mai,kashe mutum awajensa ba kimai bane,kowa yasan yadda arnan daji ke da asiri,don ma a haka mahaifiyarsa ta musulunta kafin ta mutu shine ma yasa ta dawo cikin gari taje zaune gidan haya,tana ƴar sana'ar mai da ƙuli ƙuli dashi take samu take ciyar da ƴaƴanta,yaranta biyu mace dana miji,Ruƙayya da Adam Ruƙayya ita ce ƙarama sai Adam saɓanin Adam bashi da uba,ita kuma Ruƙayya taba da uba,shi Adam tun a garinsu ta haifesa ita kuma Ruƙayya sai bayan ta shigo birni ne ta yi auren ta haifeta auren ma kuma ya mutu. Bayan mutuwar mahaifiyarsa ya taso cikin ƙuncin rayuwa shi ya ke zuwa ya samowa ƙanwarsa abinci ta kowacce irin hanya haka ya ke zuwa ya samo ya kawo mata,Ruƙayya ta kasance mai ƙyamar mahaifinta ako da yaushe,don wataranma idan ya kawo mata abincin bata ci don tasan ta hanyar daya samo. Tun abin na Adam bai yi nisa ba har ya yi nisa,babu irin aikin da ba ya yi,shine safarar miyagun abubuwa daga ƙasar nan zuwa wata ƙasar,shine safarar mata daga waccen jaha zuwa wannan kai har ya zama har ƙasar waje,sai a ɗauki yara dag nan ace za'a fita dasu birni aiki amman kuma daga haka bazaka ƙara ganin ɗanka ba,shikkenan kunyi bye bye. Ganin haka yasa ƙanwarsa Ruƙayya guduwa garin mahaifinta tunda tasan garin,Adam ya yi baƙin cikin barin ƙanwarsa gida don yana sonta sosai,kai tsaye shima yabar unguwar don daman saboda ƙanwarsa ya zauna agidan,don ya yi da ita ta koma gidansa daya ƙera taƙi yadda dole ya ƙyaleta ya cigaba da miyagun aikinsa,aka daina jin ɗuriyarsa a unguwar don daman suma ya fara isarsu,ko da idan ya yi wani kaifin ka kaishi wajen ɗan sanda to fa washe gari za'a sakosa don ya samu masu goya masa baya cikin manyan masu kuɗi na ƙasa baki ɗaya.Ga shi da mugun asiri don ko biyosa akayi ba'a samunsa saboda ɓacewa ya ke. Wannan shine taƙaitaccen tarihin Alhaji damas. **** daga zuwa na gidan Anty Khadija gidan ya koma gidan amarya sak saboda tsafta ina tashi da safe babu abinda na ke farawa da na yi sallah na yi azkhar da karatun alqur'ani to ajjewa na ke in fita in gyara gidan tsaf ɗakinta kuma sai bayan ta tashi na ke gyarawa,sannan inyi girki inyi wanka sai dai matar gidan ta fito taci ta koma tana yimin sannu,ni kuwa har mamakinta na ke,wata shegiyar rigar bacci tun ranar da nazo gidan na sameta da ita kusan sati biyu har yanzu bata wanketa ba,kuma me wanke yana zuwa wai sai ta ce mai ya tagi bata da wanki,kuma ga kuɗin me wankin anbata amman tana baƙin cikin fitar da kuɗin,ko da daman yaya Aliyu yasan halinta sai da ya siyo komai na kayan da ake buƙata komai da komai har nama sai da ya saka a fridge don shegen son kuɗine da ita. Ko da nazo gidan har nan yaya mk ya ke biyoni yazo ya tafi ya barni da tunanin waninsa yaya Bilal don nifa babu namijin da ke cikin ƙwaƙwalwarnan tawa idan ba shi ba,ko da na yi tunanin ciresa araina bai taɓa ciruwa.sam ko kaɗan bana son yaya mk har tausayi ya ke bani yadda duk ya matu akaina,bana son nuna masa bana sonsa ne saboda halinda zai shiga ina dai lallaɓasa ne dai mu rabu lafiya. Babu yadda baiyi dani ba da in amshi wayar daya kawomin naƙi amsa saboda Baba ya ce baza a bamu waya yanzu ba,haka ya koma da abarsa sai dai tun a fuska naga bai ji daɗi ba don fuskarsa ta canja,na lallaɓashi na bashi haƙuri.muna rabuwa na dawo cikin gidan na sameta tana cin abinci,daman aikin kensn taci abinci ta ƙoshi shine aikinta babu abinda take sai bacci,sai kuwa ta juyo ta ce"wai ni Khairat in tambayeki?"da sauri na ce"ina jin ki anty khadija". Gyara zamanta ta yi sannan ta ce"wai da gaske yaya mk sonki ya ke"?.ta jeho mun wannan tambayar alokacin da ban shirya ba na ce"eh sona ya ke".na bata amsa nima sai kuwa ta ce"kai ƴan gidan mu ma sai abarsu Bara'atu fa baki ga yadda take sonshi ba,kuma wallahi har soyayya suke amman shine ya komo wajenki?amman ya cika mayaudari".ta faɗi hakan tana kallona. ɗan murmushi na yi sannan na ce"to ni yanzu Anty khadija meye na wa a ciki?ina shi ya ce yana sona ko?kinga ba ni na ce ina sonsa ba kinga ai ta ƙwana gidan

Table of Contents

Chapters

87 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87