Skip to content

Chapter 55

Chapter 55

Abin Cikin Kwai Book One Complete Hausa Novel 1,316 words 0 views Progress saved
Download Book

na tafi skull duk jikina babu daɗi,yau dai na shirya indai na dawo daga skull zanje asibiti don in san meke damuna,don na kasa gane kai na ko kaɗan.abin mamaki kawai sai naga Xuhra da Ahmad wai ya kawo ta makaranta,abin ya bani mamaki sosai amman sai na ɓoye mamakin nawa na ƙarasa don mu gaisa,Ahmad ya ce"Kinga abin mamaki ko?to a gaskiya ba abin mamaki bane don ayanzu tsakanina da Xuhra mun sasanta kanmu,insha Allah nan da wasu ƴan watanni zamu angonce." Murmushi na yi inajin daɗin hakan har zuciyata na ce"kai masha Allah amman fa naji daɗi sosai wallahi Allah ubangiji ya barku tare".na faɗi hakan ina murmushi. Ranar yini muka yi muna shan hirar Ahmad awajen Xuhra,har sai da Xainab ta gaji ta ce"kai Xuhra mudai yau wallahi mungaji da wannan hirar,ayi ta hirar abu ɗaya?haba ai da gajiya"?. wannan magana sai da taso ta haddasa matsala,ni ce ma na shiga tsakaninsu har aka samu dai daito,gashi kaina kamar zai rabe gida biyu,na kasa motsa koda yatsana,ganin ina cikin wannan halinne yasa duk kuma hankalinsu ya tashi suka shiga tambayata abinda ke damuna,ɗaga musu kai kawai na yi,saboda ni kaɗai nasan abinda ya ke damuna. Tun kafin driver na yazo suka kaini gida,duk hankalinsu atashe,kamar jira na ke muxo gida sai kuma amai sosai na dinga yinsa kamar zan amayar da ƴaƴan cikina.daman kuma gashi ba wani abin arziƙi na ke ci ba,abin ma da ƙer ya ke samun waje. Basu tafi d wuri ba,amman sun sanar agida abinda ya sakasu tsayawa,to dukkansu an yarda dasu agidansu,basu da wata matsala don haka suka gyara inda na ɓata suka kaini har kan gado na suka lulluɓeni,suka dafa min ruwan lipton suka ajjemin acikin flask kusa dani,wai idan na tashi insha ko da cikin dare ne,sai kuman Bread ma da suka ajjemin.tuni bacci ya ƙwasheni,suka tafi gidajen iyayensu,duk hankalinsu akaina. ******* To fa ɓarnar Jidda bata tsaya a iya mijinta ba,har satar yara yanzu take tana kaiwa Alhaji Damas,waɗan nan yara ana satar odojinsu ne,don siyarwa waɗansu mutane ɓata gari,wanda ba ƙaramin kuɗi suke samu da wannan ba,sannan sai a ɗinke cikin yaran kuma baza a mayar dasu wajen iyayensu ba,ƙarshe sai a kaisu ƙasar waje ana lalata dasu,don dole su zama ɓata gari. Wa'iya zubillah!don Allah iyaye ku dinga kula da ƴaƴanku yadda ya kamata,wallahi musamman ma ƴaƴsn talakawa haka zaki gansu akan titi,a layikansu,suna yawo kamar basu da iyaye,daga nan sai kiga ko a sacesu ko kuma a lalata mana yaranmu,don Allah mudinga kula dasu amanar ubangiji ce awajenmu. Waɗannan satar yara da aka yi ba ƙaramin tashin hankali Bilal ya shiga ba,tun yana Holland yaji Allah Allah ya ke ya dawo don gani ya ke kamar za'ayi ta Ɗiban yaran ne,ai kuwa washe gari Bilal ya dawo,kai tsaye sai daya fara zuwa ofishinsa, ya shigar da wannan rahoton a kundinsa, suka zauna meeting akan wannan matsalar. Aranar Bilal ya saka tsasttsauran bincike akan waƊan nan mutanen,ai kuwa direct majiyarsa ta nuna masa daga Ɓangaren Alhaji damas ne, yana son taimakon waƊan nan yaran don baya son rayuwarsu ta shiga babbsn hatsari. Yana zaune gaban ogansa ya ce"Admiral ba wai muna hana ka shiga shirgin damas bane,mutumin yana da hatsari yadda baka tunani,kuma mutum ne me hatsari sosai don haka sai ka kiyaye sosai,ni zan taimaka maka da dakaru don su taimake ka,amman Bilal ka kula da kanka saboda muna ji dakai sosai acikin sojojinmu,don kai na dabanne acikinsu. ****** "Jidda gaskiya kada ki yiwa wannan yarinyar wannan abin,saboda ita bata taƁa binki da sharri ba,tana zaune da ke lafiya,infact ma awannan lokacin da muke ciki ba kowace kishiya bace za taga kina yawo ta yi shiru da bakinta ba,jidda wallahi yarinyar ba tada matsala kada ki cuce ta." "Dalla Rabi'a ki rufemin baki,wa'azi na ce ki yimin?ko Kuma shawara na ce kiban?na dai tambaye kine ko a unguwarku za'a samu wani talakan ya yi mana wannan aikin?tunda unguwarku duk talakawa ne,amman shine zaki nemi yimin wa'axi?ina son kafin in buƊe ido na ki fita daga gidan nan,idan muka wallahi naji labarin kin gayawa wani wannan maganar,zan Ɓatar da ke ne aduniyar nan,don kinsan ina da kuƊin da zan iya yi miki hakan." "Babu komai jidda ni dai nasan kema kafin ki zama komai kema talakance,harma na fiki rufin asiri,kinga kuwa ashe duka muna Ɗaya ne,kuma zan bar miki gidanki,amman ki sani shi sharri Ɗan aike ne". wani banzan kallo tabi Rabi'a dashi sannan ta ce"as as bana nemanki anan,ki fita tun kafin in saka ayimin waje da ke,banza faƘiriya kawai,talakan banza talakan wofi,insha Allah a haka zaki Ƙare a talauce tunda aure ya gagara,an gama iskanci da Ƴan iskan unguwa. Kuka sosai Rabi'ah ta yi na wulaƘancin da aminiyar ta jidda ta yi mata,ko a mafarki bata taƁa tunanin jidda za ta iya koda makamancin haka ba,ta goge hawayenta ta fita daga gidan,tana tuna ranar da jidda za ta yi nadama,don tabbas tasan aƘwai ranar nadama. *** Ina kallon tv naga wai wani ya Ƙwaci yara daga hannun mugu Alhaji damas,suka rubuta sunansa Admiral b.wanda akafu sani da Bilal,sosai na waro ido ina kallon hubbyna tsamo tsamo acikin Ƴan jarida yaran su kusan Ɗari,duk ƳaƳan talakawa ne,sosai naji daƊin ganin mijina ya,kasance me taimako na hura masa kiss ta tv Ɗin,sannan na ce"Allah ubangiji ya karemin kai yaya na". Na koma Ɗaki na na fara trying Ɗin number Ɗinsa,amman akashe na Ƙwanta tunaninsa ya cika zuciyata fal,daga wannan baccin na xarce,barcin daya zomin da Ƙalubale na rayuwa Ƙaddara ta,barcin daya kasance dana sani acikin rayuwata,wanda na yi kuka kamar zan mutu,barcin daya rabani da yaya Bilal,tsanar da ya yimin ta Ƙara ninkuwa sosai. tun ina bacci naji kamar ana Ɗauka ta a hoto,amman sai na Ɗauka ko mafarki na keyi,na cigaba da bacci na sai dai baccin babu daƊi don dai babu yadda zanyi ne,a yanzu na zama kamar kasa wajen bacci,sai in yini ina bacci idan babu skull. yaya Bilal ya kalli captain ya ce"kai nifa ka cikani da surutu banni in koma gida,saboda in koma wajen farin cikina khairat in ganta ko naji daƊi,wataƘil ma tasan na dawo,don waƊan nan Ƴan jaridan ba barin mutum za suyi ba,sai sun watsa duniya."Murmushi captain ya yi sannan ya ce"To nima dai ba tsayawa zanyi ba,don kasa ina da mata nima kuma ina sonta kamar yadda ka keson matanka,kai har dama nuna banbanci tunda ka sauka ka ke ta faman kiran khairat a bakinka,ita jidda ko oho ko?a dai ji tsoron Allah".ya faƊi hakan cikin xolaya don shi mutum ne mai raha sosai. Bilal bai tanka masa ba ya wuce motarsa yana dariya,sai dai tun akan hanya yaji gabansa na faƊuwa sosai,ya dai fara addu'ah acikin zuciyarsa,yana parcking y hango jidda ta fito daga sashensa,ta rungumesa har da kukanta ya ce"banji Ɗuriyar khairat ba lafiya dai ko?". "hmm to ni me zance Love tunda fa ka yi tafiya yarinyar nan take yawo, da kawo mutunen da ban yadda dasu ba." 1, *MU GANI A ƘASA...*🔥 _Ummu Affan_ 2, *ABIN CIKIN ƘWAI..*🥚 _Ummu Maher_ 3, *GUNTUN GORO..*💥 _Mom Islam_ 4, *GISHIRIN ZAMAN DUNIYA*🌎 Badi'at Ibrahim _Mrs Bukhari_ 5, *AUREN WATA TARA*👩‍❤️‍👨 _Miss Hajo_ Guda biyar 1k Guda huɗu N700 Guda uku N600 Guda biyu N500 Guda ɗaya N300

Table of Contents

Chapters

87 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87