Chapter 73
Chapter 73
shafawa a fuska da wuya kamar sau biyu a rana ya yi a kalla mintuna goma sha biyar kafin a wanke a kullum. 4)- Kodewar fata; a markada gurji sannan a zuba kindirmo da garin alkama cokula biyu sannan a kwaba a rika shafawa a inda fatar ta kode sakamakon kunar rana ko yawan shiga rana. A bari a fuska na tsawon mintuna goma sha biyar kafin a wanke. 5)- Yankunewar fata; a markada ruwan gurjin sannan a samu kwai a cire kwanduwar ayi amfani da farin ruwan a ciki sannan a matse lemun tsami a kwaba a rika shafawa a wajajen da fatar ta yankune. Sannan a bari na tsawon mintuna talatin kafin a wanke. Ana so a rika yin wannan hadin kamar sau biyu a rana a kullum. 6)- Domin samun gashi mai tsayi; a markada gurji da ruwa sannan a tsaga gashin kai a shafa a fatar har a cikin gashin kai ya ji sosai. Sannan a samu leda a rufe kan na tsawon mintuna talatin kafin a wanke da man wanke gashi. Yin hakan na dada tsayin gashi a kai. *Miss green ce* [23/09, 16:30] Miss Green🍀: 91. . . . . . .92 . . . . . . .nunawa na yi kamar bansan abinda suke ba,na yi wuce wata gaba zuwa wajsn masoyi na,fuskata Ɗauke da murmushi,wani irin kallo me cike da soyayya ya ke yimin yadda yaga na komar kamar Ƴar shekara goma yarinta na ta Ƙara fitowa sosai,ga wani irin mugun Ƙamshin dana ke fitarwa me gigita namiji,ai kuwa shahid ya gigice Ɗin sosai amman duk da haka hankalinsa na kan Bilal wanda ya Ɗaga iman sama yana yi mata wasa. Ya ce"hayatee wannan shine baban lovely children Ɗina"?.sosai gabana ya faƊi ahankali na ce"eh shine na manta ban faƊa maka ba,yaya ya ke gare ni".sai naga fuskarsa ta haƊe nan da nan,na lura shahid shima namijin kishi ne sosai,daman kuma ance larabawa sunfi kowa kishi. Ya ce"ayya kada ki damu don na tambaye ki ki yi haƘuri,amman wannan yayan na ki wata macece za ta ce bata sonshi?babu abinda Allah bai yi Masa ba,amman na yi mamakin rabuwarku,kuma kema khairat nasan ba zai so rabuwa da ke ba,sai dai Ƙaddara amman duk namijin daya sakeki khairat wallahi ya yi asara gaskiya". Murmushi kawai Na yi don bani da amsar da zan bashi,don kada yabi inda muke sai ya Ɗauki Ƴarsa suka yi gaba abinsu.Ina jinsa yana tambayarta Ƴan uwanta,sai kuwa iman ta ce"dady mamanmu ta Ƙara yi mana wani dadyn ka ganchi cen ma".ta fara nuno inda Muke.Bilal bai san lokacin da wasu hawaye masu zafi suka fara zubo masa ba ya yi saurin gogewa ya wuce. to ranar dai da Ƙer shahid ya barni na wuce gida na lura bai gajiya da kallona,idan na biye masa kuma sai muyi ta tsayuwa awajen,don haka na ce"habibee ni zan tafi gida fa mun daƊe".na faƊi hakan cikin shagwaƁa,sosai na burgesa ya ce"ah lallai baki so kije gida yanzu,ni wannan shagwaƁar taki tafi komai tafiya dani",yauwa khairat ki yi haƘuri ni dinner bata cikin tsarina sam,duk kuwa kuƊin da na ke dashi,amman mu al'adarmu a musulunce shine bayan anyi aure ana walima washe gari,to ni dai hakan yafi Ƙwantamin". murmushi na yi sannan na ce"kada Ka damu nima duk wannan bidi'ar bata gabana albarkar auren shi na keso".sosai na burgesa amman fa muna cikin zancen naji alert Ɗin kuƊi awayata na ce"habibee naga ka turomin kuƊi me zanyi dasu haka"?.murmushi ya yi sannan ya ce"ki yi wani abin dasu,amarya ta me sirrin kyau".ya faƊi hakan yana murmushi,bai bani damar Ƙara magana ba ya yi shigewarsa cikin mota ya yi gaba. Sosai na keson shahid,ba don kuƊinsa ko kyau ba,a'ah sai don tsare mutuncinsa,sam bai taƁa koda taƁa hannuna da sunan wasa ba,balle kuma wata maganar banza,muna mutunta kanmu mu duka,anan na ke jan hankalin Ƴan mata da zawarawa adinga riƘe mutunci da kyau,saboda ke mace duk abinda ki ka yi bai Ɓoyuwa namiji kuwa ko zai yi sau Ɗari ba'a Ganewa,kuma a musulunce ma hakan sam ba shida kyau kuma ma ba tarbiyya bace.kuma matuƘar ki ka sadaukar da mutuncinki ga wani to fa wannan mijin koda tare ku ka yi lalatar bazai taƁa ganin darajarki ba,balle kuma akaiga zancen mutuntawa,don shi aure anfison ayisa da ganin mutuncin juna. da kai na na ware kuƊi masu yawa aka sakewa hajiya kaka sabbin kayan Ɗaki aka yi mata sabon fenti,mama na itama aka sake yi mata furnitures duk da basu daƊe ba,sannan mama ta faƊawa babana duk kuƊin da shahid ya ke bani,baiyi mamaki ba ko kaƊan don yaron yasan tarihinsa tun farko har zuwa yanzu,mahaifiyarsa da mahaifinsa suna da kuƊi sosai kuƊi kuma masu mugun yawa,shi da kansa shahid a iya nigeria ma yana da company's sunfi ashirin,ga kuma na Ƙasashen waje,uwa uba kuma likita ne me zaman kansa me kuma lasisin kowacce Ƙasa,likitan zuciya ne shi,mahaifiyarshi kuma unguwar xoma ce.kuma ba Ƙaramin kuƊi suke samu ba. ranar daya rage saura Ƙwana biyu gidanmu ya cika Ɓam kamar auren budurwa,son hatta ankon biki,sai da shahid ya turomin kuƊi wai abawa kowa,wai su haka suke yi naƘi amsa sai gashi ya lallaƁa yaje wajen hajiya kaka,itama da farko taƘi amsa amman da taga ransa ya Ɓaci sai ta amsa,ai kuwa kowa sai daya samu ankon biki,ranar Ne kuma amminsa tazo gidanmu mata mai mutunci da sanin darajar mutane,ta Ɗakko wata mata wai za ta yimin gyaran jiki na larabawa. daga ganin matar ma balarabiya ce wataƘil Ɗakkota aka yi,,harda Ƙanwarta tazo ita ammin,duk suna da mutunci sosai naƘi fitowa wai ina jin kunyarsu ta ce"a'ah khairat mufa bama jin wannan kunyar gwarama tun yanzu ki saba don shahid ba shida kunya wallahi".murmushi kawai na yi ai kuwa aranar aka fara yimin gyaran jikin,wowo hmm wai ko tsagar gida ma hanani fita matar ta yi sai dai ina Ɗaki ina shan a/c,Mutanen gidanmu suka dinga zuwa ganin ammin shahid,shima tun daga ranar ammin ta hanashi xuwa saboda gudun saƁawa Allah don taga yadda Ƙirar khairat Ɗin take,ba kowani namiji ne xai iya kallonta ya kyale ba,duk da ta yarda da Ɗanta mutum ne me kana kansa sosai,da tsantsae tsoron Allah,,shiyasa a kullum take godewa Allah da kyautar da ya yi mata na samun Ɗa kamar shahid,daman kuma ba yawan yara akeso ba albarkarsu ake nema. kullum muna maƘale awaya ni da shahid ana zuba soyayya na lura su larabawa mayun soyayya ne,kamar laila majnun. Baba na ya saka aka kirawo masa Bilal ya ce"Bilal kasan me yasa nasa ka aka kirawomin kai?".girgiza kawai ya yi,idanuwansa sunyi ciki duk ya rame abin tausayi ya ce"ina son ka yarda da Ƙaddara me kyau ko mara kyau,ka cire komai aranka kamar ma ba'ayi ba,kai Ɗinnan dai yayan khairat ne kuma uban ƳaƳanta har huƊu,to kaga aƘwau akaƘa me Ƙarfi a tsakaninku,don haka yanzu ma na kiraka ne don ka zamo waliyyin khairat,don ance babban wa uba koda ace yanzu mu faƊi mu mutu kai ne babansu su duka". sosai wata zufa ta shiga tsattsafo masa,ya goge ta cikin dauriya da Ƙarfin hali ya ce"ba bu komai baba na gode da bani shawara da ka yi."baba yaji daƊi sosai suka cigaba da hirarsu amman can cikin zuciyarsa yana jin
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87