Skip to content

Chapter 76

Chapter 76

Abin Cikin Kwai Book One Complete Hausa Novel 1,281 words 0 views Progress saved
Download Book

yana murmushi,bai bani damar Ƙara magana ba ya yi shigewarsa cikin mota ya yi gaba. Sosai na keson shahid,ba don kuƊinsa ko kyau ba,a'ah sai don tsare mutuncinsa,sam bai taƁa koda taƁa hannuna da sunan wasa ba,balle kuma wata maganar banza,muna mutunta kanmu mu duka,anan na ke jan hankalin Ƴan mata da zawarawa adinga riƘe mutunci da kyau,saboda ke mace duk abinda ki ka yi bai Ɓoyuwa namiji kuwa ko zai yi sau Ɗari ba'a Ganewa,kuma a musulunce ma hakan sam ba shida kyau kuma ma ba tarbiyya bace.kuma matuƘar ki ka sadaukar da mutuncinki ga wani to fa wannan mijin koda tare ku ka yi lalatar bazai taƁa ganin darajarki ba,balle kuma akaiga zancen mutuntawa,don shi aure anfison ayisa da ganin mutuncin juna. da kai na na ware kuƊi masu yawa aka sakewa hajiya kaka sabbin kayan Ɗaki aka yi mata sabon fenti,mama na itama aka sake yi mata furnitures duk da basu daƊe ba,sannan mama ta faƊawa babana duk kuƊin da shahid ya ke bani,baiyi mamaki ba ko kaƊan don yaron yasan tarihinsa tun farko har zuwa yanzu,mahaifiyarsa da mahaifinsa suna da kuƊi sosai kuƊi kuma masu mugun yawa,shi da kansa shahid a iya nigeria ma yana da company's sunfi ashirin,ga kuma na Ƙasashen waje,uwa uba kuma likita ne me zaman kansa me kuma lasisin kowacce Ƙasa,likitan zuciya ne shi,mahaifiyarshi kuma unguwar xoma ce.kuma ba Ƙaramin kuƊi suke samu ba. ranar daya rage saura Ƙwana biyu gidanmu ya cika Ɓam kamar auren budurwa,son hatta ankon biki,sai da shahid ya turomin kuƊi wai abawa kowa,wai su haka suke yi naƘi amsa sai gashi ya lallaƁa yaje wajen hajiya kaka,itama da farko taƘi amsa amman da taga ransa ya Ɓaci sai ta amsa,ai kuwa kowa sai daya samu ankon biki,ranar Ne kuma amminsa tazo gidanmu mata mai mutunci da sanin darajar mutane,ta Ɗakko wata mata wai za ta yimin gyaran jiki na larabawa. daga ganin matar ma balarabiya ce wataƘil Ɗakkota aka yi,,harda Ƙanwarta tazo ita ammin,duk suna da mutunci sosai naƘi fitowa wai ina jin kunyarsu ta ce"a'ah khairat mufa bama jin wannan kunyar gwarama tun yanzu ki saba don shahid ba shida kunya wallahi".murmushi kawai na yi ai kuwa aranar aka fara yimin gyaran jikin,wowo hmm wai ko tsagar gida ma hanani fita matar ta yi sai dai ina Ɗaki ina shan a/c,Mutanen gidanmu suka dinga zuwa ganin ammin shahid,shima tun daga ranar ammin ta hanashi xuwa saboda gudun saƁawa Allah don taga yadda Ƙirar khairat Ɗin take,ba kowani namiji ne xai iya kallonta ya kyale ba,duk da ta yarda da Ɗanta mutum ne me kana kansa sosai,da tsantsae tsoron Allah,,shiyasa a kullum take godewa Allah da kyautar da ya yi mata na samun Ɗa kamar shahid,daman kuma ba yawan yara akeso ba albarkarsu ake nema. kullum muna maƘale awaya ni da shahid ana zuba soyayya na lura su larabawa mayun soyayya ne,kamar laila majnun. Baba na ya saka aka kirawo masa Bilal ya ce"Bilal kasan me yasa nasa ka aka kirawomin kai?".girgiza kawai ya yi,idanuwansa sunyi ciki duk ya rame abin tausayi ya ce"ina son ka yarda da Ƙaddara me kyau ko mara kyau,ka cire komai aranka kamar ma ba'ayi ba,kai Ɗinnan dai yayan khairat ne kuma uban ƳaƳanta har huƊu,to kaga aƘwau akaƘa me Ƙarfi a tsakaninku,don haka yanzu ma na kiraka ne don ka zamo waliyyin khairat,don ance babban wa uba koda ace yanzu mu faƊi mu mutu kai ne babansu su duka". sosai wata zufa ta shiga tsattsafo masa,ya goge ta cikin dauriya da Ƙarfin hali ya ce"ba bu komai baba na gode da bani shawara da ka yi."baba yaji daƊi sosai suka cigaba da hirarsu amman can cikin zuciyarsa yana jin wani abu yana yi masa yawo sosai,ranar dai Bilal kusan Ƙwanan zaune ya yi,saboda tsananin tashin hankali,gobe khairat Ɗinsa xa ta Ɗaura aure?da wani ba shi ba?za ta tafi gidan wani?yanzu shikkenan sun rabu har abadan?tuni ya dinga kuka kamar ba shi ba,tabbas yanzu yaga illar rashin yin bincike kafin Ɗaukar mataki,kuma yanzu yaga illar yin saki har uku,da Ɗaya ya yi mata ko biyu da yanzu suna nan zamansu gwanin sha'awa. Anan nake jan hankalin maza akan mu kula mu daina yanke hukunci cikin fushi,an sani kuma an yarda ita rayuwar aure tana zuwa da Ƙalubale daban daban kuma sai anyi haƘuri sannan ake samun abinda ake so,don haka mu kasance masu haƘuri ako ina kuma aduk halin da muka tsinci kanmu. to nima anawa Ɓangaren hakan ta kasance amman tsaƁanin tunaninmu ba Ɗaya bane da Bilal ni da Shahid ci ke muke da zumuƊi da son kasancewa da juna,na tuna gobe iyanzu ina rungume jikin mijina abin alfaharina,ina matuƘar son shahid son da bai ko na yaya Bilal ba,don sai yanzu na gane ashe lokacin ban san ma wani so ba,sai yanzu nasan so don shahid ya shayar dani madarar soyayya. ****** Washe gari na chaƁa adona cikin wata doguwar riga wadda shahid ya kawomin me shegen kyau,kalar skye blue ta tasha kwalliya har ya gaji,kowa sai bina da kallo ya ke kamar wata acikin zarah,gidanmu ya cika Ɓam,Ƴan huƊu ma sunsha Ƙwalliya sosai da skye blue Ɗin shadda aka dinga yi mana hotuna dasu,don tun sassafe ya aiko da wani me hoto wanda ya Ƙware yasan kuma aikinsa,kuma baƘar fata ne amman ya iya hoto sosai yasan kuma aikinsa,don duk wanda aka yiwa hoton sai ya yi murna saboda hotunan suna fita tarwal sosai. iyaye na guda 12 duk anyi mana hotuna dasu gwanin sha'awa ga Ƴan huƊu agaba suma sunyi kyau. Ɗaki na ya cika da Ƙawaye sosai,Mukaji shigowar angwaye bayan an Ɗaura aure,da sauri nadiya ta ce"khairat tashi ki leƘa kiga angonki sai jin kunya ya ke". Ai banji kunyar ba kuwa na tashi ta saman bene ina hangosa,don daman baba na ya bamu mukulli muka haye saman,babu hayaniya babu komai...... .✍🏿 07068606171 *GAWURTATTU BIYAR, TAFIYAR TA MUSAMMAMN CE. 👯‍♀️👎👇👇* 1, *MU GANI A ƘASA...*🔥 _Ummu Affan_ 2, *ABIN CIKIN ƘWAI..*🥚 _Ummu Maher_ 3, *GUNTUN GORO..*💥 _Mom Islam_ 4, *GISHIRIN ZAMAN DUNIYA*🌎 _Mrs Bukhari_ 5, *AUREN WATA TARA*👩‍❤️‍👨 _Miss Hajo_ Guda biyar 1k Guda huɗu N700 Guda uku N600 Guda biyu N500 Guda ɗaya N300 *DOMIN TURA KUƊIN KAI TSAYE*👇 0037219728 Fatima Rabiu Sunusi StanbicIBTC Bank. Domin tura shaidar biya👇 0810 433 5144 Masu tura katin MTN👇 0814 179 9224 Ƴan Ƙasar Niger zasu tura nasu anan.👇 0817 952 3215 Guda biyar 1000f Guda huɗu 700f Guda uku 600f Guda biyu 500f Guda ɗaya 300f *TEAM GAWURTATTU BIYAR TAKUN FARKO TAFIYA TA MUSAMMAN.* 🔥🥚💥🌎👩‍❤️‍👨 _*Miss green ce*_🤙🏿 [23/09, 16:30] Miss Green🍀: *🏮ABIN CIKIN ƘWAI🏮* littafi na 3 *by✍🏿* Ummu maher(miss green)🍀 Wattpad user name Rabiatu333 Arewabooks rabiattu0444 *SIRRINKI👂🏻* ƳAR UWATA ANASO BAYAN KIN GAMA AL'ADA KIDINGA TSARKI DA GANYEN MAGARYA,YANA CIRE INFECTION DA SAURAN ƘARNIN JINI👏🏻. DAGA DR UMMU MAHER. 93. . . . . . . 94 . . . . .kasa sakin labulen na yi ina kallon shahid yadda ya yi wani irin mugun kyau kamar ka ɗaukesa.aƙwai abokansa sosai baƙar fata.amman farar fatar sunfi yawa Nadiya ta ce"inye kaji amarya mara kunya?kin kasa daina kallonsa".su Khalisat dasu iman har dama Rashida da maryam duk suna zzzaune suka saka dariya.iman wacce ke sakawa ƴarta pampas ta ce"a'ah fa Nadiya barta ta kalli abinta.Allah ne ya

Table of Contents

Chapters

87 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87