Chapter 10
Chapter 10
me ye amfanin auren."? "Khairat kenan ita fa wannan tsohuwar haka take ni wallahi har Allah Allah na dingayi mu taho saboda yadda tsohuwar nan ta sakani a gaba wai sau na auri yaya mohd,kuma ni wallahi na fi son har inyi jami'a kafin inyi aure." da fa kafaɗarta na yi sannan na ce"ki yi haƙuri don Allah Rashida akan wannan maganar ki cigaba da addu'a kinga dai yadda kaka ta dage yaya Mohd zaki aura shima kuma ya dage ke ya ke so,to kinga addu'a ita ce mafita don kinga duk su Baba da abinda kaka ta faɗa musu suke amfani don haka kawai sai dai ki yi haƙuri." "Khairat ni fa wallahi bana sonshi wallahi,ke kin sani idan yaya Mohd yana da ƙyau yana da kuɗi amman ni wallahi matsalar mahaifiyarsa ita ce kawai za ta takuramin ko da bayan anyi auran ne?. "Tabbas matar Baba tijjani tana da babbar matsala sosai don ko yaya sulaiman babban ɗanta daya auri ƴar gidan Baba Bashir haka ta takura mata zagin yau na gobe daban,don ma kaka tana ta ka mata burki da abin sai ya ɓaci sosai." "to kin gani khairat to a haka zan auri Yaya Mohd daman kuma duk ƴaƴanta ta fi sonshi sai kawai ace shi zan aura in auri masifa,Allah ni fa bazan aureshi ba gaskiyar magana".tana faɗar hakan ta tashi ta bar wajen. Na bita da kallo ita sonta ma ake ina ga kuma ni da ba son na wa ake ba shisshigina kawai na ke,yadda yaya Bilal ya tsane ni kamar mutuwarsa,ni kuma na nace sai shi,tabbas idan ban auri yaya Bilal ba to wallahi ni nasan ko da wani ya aure ni to gangar jikina ya aura don bazan taɓa sonsa ba zuciyata da komai na wa yana ga yaya Bilal,ina ma zai soni ko da bai kai yadda na ke sonshi ba,da ranar har azumi sai na yi saboda jin daɗin hakan. Mun fara exam ɗin second time wacce zamu tafi hutu sannan mu dawo zana jarrabawar waec da neco,muna ta karatu sosai ba mu da lokacin kanmu sam sai na karatu muna dawowa daga class zamu yi bitar haddarmu ayanzu muna izu hamsin da biyar baƙara ce kawai bamuyi ba itama kuma mun iyata. Rannan malamarmu bata da lafiya mai koya mana karatun qur'ani da asuba aka turo wai inzo zan ƙarawa wasu hadda,abin mamakin ko da nazo su sai naga ƴan ajin su Nadiya ne gabana yana ta faɗuwa na zauna har na ɗakko qur'anin sai na ji Nadiya na ce wa"Hmm wai arasa wacce za ta ƙara mana karatun sai wannan tuban muzurun har yanzu fa wasu daga dangin uwarta basu musulunta ba,adanginsu uwarta ce kawai ta fara musulunta sai manyan arna kakanninta suma suka musulunta kakanta fa babban fasto ne sai ace kuma wai ita ce za ta koya mana karatu?". wasu zafafan hawaye ne suka fara zubomin ba tare da na yi tunanin tare su ba saboda hawayen daman na ke son yi ɗin,dariya sosai suke min big girl oganniyar cikinsu ta ce"au shine kullum ake wani yawo da ƙaton hijab na munafunci?to yau sai mun buɗe hijab ɗin munga abinda ake ɓoye mana?. ban san ta zo kaina ta tsaya ba,ɗaga kan da zanyi naga big girl akaina tana neman ciremin hijabij jikina,da sauri na tashi na matsa lungu idona ya yi jawur ta ƙara matsowa tana ce wa,ai yau Khairat baki da wajen guduwa a hostel ɗinnan muradina na shekaru kusan biyar yau saina cika sa akanki." tana faɗar hakan ta riƙe hannun da na riƙe hijabin ta yi wa su Nadiya fito da sauri suka taho suka rirriƙeni ni kuwa sai kuka na ke ina ihu,wani wawan mari big girl ta yimin sannan ta ce"duk ihunki da wani fizge fizgenki yau wallahi sai na wulaƙanta ki a skull ɗinnan don daman haushinki na keji sosai na karɓemin saurayin da ki ka yi sir Kamil don haka yau sai na rabaki da abinda ki ke tutiya dashi. Sosai na ke kuka ina roƙonta da ta yi haƙuri amman sai naga kamar zugata na ke ita dasu Iman duk sun yayyaga min hijabina ya yi kaca kaca dashi bakina duk ya fashe saboda tsabar shan bugun da ya yi,amman har yanzu ban daina kukan ba,sunyi nasarar cire min hijabina na riƙe rigata sukayi sukayi duk yawansu su cire amman suka kasa wani ƙaton abu Nadiya ta ɗakko tana ce wa"tunda kin ƙi ta daɗi bari muyi miki mai gaba ki ɗaya. Saukar abu na ji akaina,nan da nan na fara ganin wani iri duk sun komamin bibbiyu,ana cikin haka wata secutyn skull ɗin tazo wucewa ta hango duk abinda ke faruwa da dauri ta kaɗa ƙararrawa sai ga duk securityn sun bayyana suka biyota cikin ajin don ganin abinda ke faruwa. Da sauri suka sakeni suna wani wiƙi wiƙi da idanuwa alamun rashin gaskiya,ai kuwa suka cafkesu alokacin ni tuni na yi suman wahala don ban san inda kaina ya ke ba,duk sun yayyaga min rigata,da sauri ɗaya daga cikinsu ta cire hijabin da ta saka ta rufemin sutura ta,don samana duk a buɗe ya ke har hawaye sai da matar ta yi don ba ƙaramin ba ta tausayi na yi ba. Daman sun daɗe suna jin labarin yaran da kuma ta'asar da sukeyi na lalata ƴaƴan mutane amman aka ƙi ɗauƙar mataki akansu ana tunanin sharri ake musu. A ruɗe Rashida da Hasiya suka fito daga Hostel ɗinmu,daman duk sun damu da rashin dawowa ta da wuri don har sunyi mana abincin karyawa amman ban dawo ba. Alokacin an fito dani kamar matacciya zuwa ƙaramin asibitin da ke cikin skull ɗin na mu,su kuma su Nadiya aka wuce dasu ɗakin hukumar makaranta.ɗalibai kowa ya yi cirko cirko masu saurin kuka sai yi suke. Rashida kuwa har bakin ƙofar da aka shiga dani ta shiga tana ta kuka tana ce wa"shikkenan sun kashe khairat wallahi nima bazan taɓa barinku ba nima sai na kashe ku".haka take ta maganar kamar ta ɓaɓɓaɓiya. Hukumar makaranta suka kirawo Abbanmu a waya daman duk shine ya sakamu a skull ɗin don haka hankalinsa a tashe yaje ya tashi yayansa ya ke faɗa masa anyi masa kiran gaggawa daga makarantarsu Khairat. Shima hankalinsa atashe suka fito a hanya suka haɗu da Baba tijjani da Baba Auwalu suka shaida musu abinda ya ke faruwa,suma ka sa tafiya aikin sukayi suka ce zasu bisu makarantar don suma hankalinsu duk a tashe ya ke. Bilal ya fito daga shi sai wandon aikinsa na sojoji da ƴar fal maram itama ta sojojin ce,sunyi masa ƙyau kayan kamar don shi aka yi su,saukarsa kenan awajen iyayen na sa duk yaji abinda ke faruwa don haka kai tsaye ya bisu ko ajje kayansa baiyi ba. Anyi min allurar bacci wani baccin wahala ya ɗaukeni,duk inda naji ciwo kuma an daka plasta an mannesa. Ko da su Nadiya sukayi ido huɗu da yaya Bilal au fitsari sai da sukayi ga shi belt ɗin jibga na jikinsa,ai kuwa ko da yaji abinda ya faru jijiyoyin kansa har wani tashi suke idanuwansa sunyi jawur kamar gauta. Baba Tijjani kuka kawai ya fashe dashi jin ƴaƴansa har guda uku acikin wannan mummanar rayuwar,Baba na ma da ya ke mai dauriyar
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87