Skip to content

Chapter 30

Chapter 30

Abin Cikin Kwai Book One Complete Hausa Novel 1,303 words 0 views Progress saved
Download Book

kin ɗora mata lalurar dole?to wallahi sai na kashe ki na kashe banza". Amira ce da ta shigo ɗakin yanzu taji abinda ke faruwa ta sheƙa da gudu tana kiran mutane,sosai ɗakin ya cika da mutane kun san gidan yawa ɗuuu kowa ya shigo.wanda bai san abinda ya faru bama yanzu ya sani,hajiya kaka ma ta shigo don tana cen tana kukan abinda ya faru,mero ma ganin kakan tana kuka ita ma sai ta hau kukan sai yanzu ne da suka jiyo ihu suka firfito har mero. Da ƙer aka cire hannun mama daga wuyan hajiya iklima ta haɗa wata uwar zufa sosai,kamar wadda ta yi babban yaƙi,hannunta na kan wuyanta tana murzawa ta samu waje ta zauna a bakin gadonta,tana tarin wahala. Sosai hankalin kowa ya tashi da jin duk abubuwan da suka faru,wasun su sun yadda wasu kuma basu yadda ba,hajiya kaka tana kuka ta ce"kai gaskiya zulaiha inyamurai sunyi asara da suka haifo ki a matsayin ƴarsu,yanzu kuma bayan hanyar da ki ka saka ƴarki shine ki ka biyo kishiyarki har ɗaki zaki kashe ta?ah to wallahi ba agidan nan za'ayi kisan kai ba,zo ki fita cen garinku na ƴan obwa musho,kije cen ki yi,idan kinga da ma-ma ki shiga boko haram ko kuma ƴar kidnapping amman mu ba'a nan ba". Tana faɗar haka taja ƙeyar mama har ɗakinta tana tsaye ta ɗibi kayanta ta fito,sai dai me?sai ga yaya Aliyu ya shigo kallon mama sosai ya yi,sannan ya kalli hajiya kaka wacce fici-ficin idanuwanta suka kuma komawa ciki sosai,alamar rashin mutunci take ji ko kallon Aliyu ɗin ma bata yi ba. "Mama lafiya me ya faru?ya na ganki da aƙwati kuma?" Duk alokaci ɗaya ya jerowa mahaifiyar tasa tambayar,mama ta kallesa cikin tausayinsu sannan ta ce"Aliyu yau zamana agidanku ya ƙare,zan tafi da kewarku amman ga ƙanwarku nan,i'ta kaɗai ce mace acikinku don Allah ku kulamin da i'ta kamar ina nan?ga ƙaninku da ke makarantar ƙwana shima ku kulamin dashi don Allah". Kasa gane maganar mahaifiyar tasa ya yi,kansa ya yi masa nauyi sosai harshensa ya kasa furta komau har maman ta fita baki ɗaya daga cikin gidan,da sauri yabi mahaifiyar tasa,gudu ya ke sosai a motar sai dai yana zuwa titi yaga ta hau mota,da sauri yabi motar hankalinsa duk a tashe. A babbar tasha aka ajje ta,tana fitowa taga Aliyu ya biyota,ta gyara zaman mayafinta sannan ta ce"Aliyu yanzu sai da ka biyoni?da ka zauna kusa da ƙanwarka ka lallashe ta,don a yanzu tana buƙatar mai taimakonta akusa da ita,wanda zai share mata hawayenta bayan rashinta. "Mama wai me ya faru da khairat ɗin?wani abu ne ya faru da i'ta?". ɗan murmushi mama ta yi wanda ake ce wa yafi kuka ciwo,babu abinda ta ɓoye mishi tun farko har izuwa yanzu. I'danuwansa suka yi jawur alamar zuciyar Ali gadanga ta motsa bakinsa ya yi masa nauyi sosai,ya ma rasa wani irin mataki zai ɗauka akansu mama iklima?ko da kashesu ya yi ba zai daina jin baƙin cikin ɓatawa ƙanwarsa suna da aka yi ba,ƙanwarsa da ya ke so ya ke ƙauna fiye da kansa?don yana matuƙar jin tausayinta tunda i'ta kaɗai ce mace acikinsu. [03/09, 20:31] Ummu Maher(Miss Green): "Aliyu ba na faɗa maka bane don ka ɗauko mataki,a'a na faɗa maka ne don ka kula da ƙanwarka,kana da gida Allah ya hore maka don haka ka kai khairat gidanka,ban yarda daga yau ta ƙara ƙwana acikin gidan nan ba,saboda nasan abinda zai biyo baya,mahaifinku mutun ne mai matuƙae zuciya musamman idan abu ya fice masa aransa,don haka ka kula,kada ka ce don mun rabu wai zakajo haushinsa,a'a mahaifinka ne kuma shima yana da haƙƙi mai girma akanka don haka a ƙarshe ina ƙara jadda da maka ka kula da ƙannenka kai ne babba don Allah". Cikin kuka ya riƙe hannun mahaifiyar ta su sannan ya ce"haƙiƙa na yi baƙin cikin rabuwa da ke mamana,mahaifiya ta gari,mai son cigaban ƴaƴanta ako da yaushe,aduk inda ki ke ba zanyi ƙasa a guiwa wajen zuwa ba,insha Allag zaki sameni a mai yi miki biyayya ko da bakya nan." Sai ya ƙwantar da kansa a hannun mahaifiyar tasa abin tausayi,ako da yaushe idan ya shugo gidansu idan mahaifiyarsa bata nan sai yaji gidan tamkar kango ne,tafiyar wuni kenan?ina ga kuma tafiyar da mutum zai yi baki ɗaya izuwa wani gari na daban?.a dai dai nan Aliyu ya ƙara fashewa da wani irin kuka mai ciwo,tabbas uwa garkuwa ce a wajen ƴaƴanta,uwa ita ce tushen al'umma. Anan na ke janyo hankalinku ƴan uwa na,muso iyayenmu so na haƙiƙa ba wai son ƙarya ba,musamman ma uwa,uwa ita ce mau tattalin ƴaƴanta da son farin cikinsu a ko da yaushe,uwa ta ƙwammace da taci abinci bata bawa ɗanta ba gwara ta bawa ɗan yaci i'ta ta zauna a haka. Wa'iya zubillahi!a wannan lokacin namu na yanzu wasu sun mayar da iyayensu tamkar bayinsu,sun ƙwammace su farantawa ƴaƴansu da matayensu akansu,tabbas duk mutumin da bai gama da iyayensa lafiya ba,to wallahi ya yi asarar zaman duniya da kuma na lahira,Allah ya tsaremu aminya bamu damar gamawa dasy lafiya,waɗanda iyayensu suka rasu Allah yajiƙansu amin. [03/09, 20:40] Ummu Maher(Miss Green): Kuɗi sosai yaya Aliyu ya ciro a acc ɗinsa ya bawa mahaifiyarsa,yana tsaye har motarsu ta tashi sai Benin,asalin garin iyayen mamanmu. goge hawayen fuskarsa ya yi yana jin wani irin zafi acikin zuciyarsa. *** aranar na bar gidanmu tafiyar da ban taɓa tunanin zanyi irinta ba,ga shi mahaifiyata sanda ta tafi ban sani ba,na yi kuka har na gaji zan shiga sashen hajiya kaka don yi mata sallama,yaya Aliyu ya riƙe hannuwa na yana girgiza min kai alamar a'ah. Ina ji ina gani na shiga motar muka tafi,kewar mahaifiyat dana gidanmu suka taru suka yi min yawa,haƙiƙa bawa baya taɓa tsalla ke wa ƙaddararsa,Allah ya bamu ikon cinye dukkanin ƙaddarorinmu. Yaya Aliyu sai tarairaya ta ya ke tun acikin mota,ni kuwa sai kallonsa na ke ina kuma tausayinsa don nasan dannewa kawai ya ke don ya farantamin amman hankalinsa duk atashe ya ke,fiye da na wa nima. Muna isa gidan da kansa ya fitomin da kayana har cikin gidan na kallesa na yi murmushi idanuwa na da ƙer na ke ganinsu saboda kukan dana sha. "A.ah don Allah ku tsaya anan!ina zaka jemin da wannan gantalalliyar ƙanwar ta ka?". *miss green ce* [23/09, 16:19] Miss Green🍀: *🥚ABIN CIKIN ƘWAI* ummu maher(Miss green)🍀🍏 *sirrinmu* rarrashin mai gida ya yin fushi😃💋🤝 *haba mijina abin alfaharina,haƘiƘa fushinka agareni kanar garwashin huta ne,ka taimaka ka yafemin ko da zan samu sassauci,Allah yabarmu tare my hubby,sai ki shafa hannayensa a hankali* Wallahi ko shaiƊan ne shi sai ya sakko😃😒 *By miss green dr mata😃* 31🟨32 . . . ."haba wannan abu har ina?ƙanwar ka ta yi cikin shege har ta yi Ɓari,shine ni yanzu za a wani kawo min i'ta gida na?a to wallahi ku koma inda kuka fito amman wallahi ni dai ba dani ba". "Ke ce dai zaki bar min gida na,kuma idan naji kin Ƙara zagin Ƙanwata da mummunar kalma wallahi sai kin Ƙwammace baki zage ta ba,ya janyo hannuwa muka shiga gidan. kallonsa kawai take yi da mamaki don da zasu shiga na har bugeta ya yi,hankali na duk a tashe ya ke,wato kowa yasan abinda ya faru kenan?i'ta da take nan

Table of Contents

Chapters

87 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87