Chapter 77
Chapter 77
bata daga sama balarabe har gida,ashe muma zamu samu larabawa a zuri'armu?ai kuwa daga yauma zan fara proud ce wa muma fa mun haɗa dangi da larabawa". Dariya kowa ya saka Xuhra da ke danna wayarta alamar chart take ta ce"hmm ni fa wallahi abin har mamaki ya ke bani Khairat da auren balarabe?,gaskiya abin zai bada fasion sosai don wallahi sun dace.ammsn gaskiya yafi khairat kyau". Murmushi kawai na yi na buɗe wayata inda naga saƙon kiransa yafi sau 10.na riƙe baki na na ce"ya ilahi Hubby ya kirani har sau 10"?.duk sai na gigice na shiga neman number ɗinsa suka shiga yimin tsiya suna ce wa"matar balarabe uwar larabawa".murmushi kawai na yi na tashi alokacin da ya ɗauki wayar. Wani irin sanyi naji jin muryarsa me laushi da kuma daɗi ya ce"na yi fushi amaryata yau ko ɗaukar wayata ma an kasayi ko?.ba komai zan rama nima yau ba sai gobe ba".da sauri na fara magana cikin yana yin shagwaɓa na ce"yi haƙuri hubby wallahi abubuwane suka yimin yawa". Murmushi ya yi sannan ya ce"ok ki sakko me hoto zai yi mana,don na matsu wallahi inga amaryata".ya faɗi hakan cikin sigar tsokana.bayan munyi sallama na dawo me ƙwalliya ta ƴara gyaramin kwalliya ta sosai na ƙara kyau kamar wata acikin zarah. Doguwar rigar tawa najan ƙasa don irin me duxuzu ɗin nan ce daga ƙasa.daga sama kuma ta ɗan matse amman dogon hannu gare ta.sai mayafin na ta net ne amman kuma yasha ƙwalliya sosai da wasu irin stones,sai goggoro na kalar arsh wanda shima yasha stones ɗin sosai,ammsn goggoron irin me laushin nan ne,ba me tauri ba don haka sai yabi kaina sosai kamar akan nawa aka dasa shi. Takalmina me tsini ne sosai kalar ash ɗin shima wanda ya gaji da haɗuwa,amman aƙwai ɗan stones kaɗan kalar kayana skye blue,sai pos ɗina ma arsh kalar goggoro na takalmi da ɗan kunne da sarƙa na. Sosai na yi wani irin mugun kyau kamar ka ɗaukeni,saboda yadda fatata take wani irin kyalli kamar ka ɗaukeni uwa uba ƙwalliyar dana sha wadda ta kasance simple make up ce,wacce ba'a cika abubuwa a fuskar ba,daga ja gira sa eyeslashes,sai lipstick me golden sai eyes shadow.shikkenan amman fa irin wannan kwalliyar tafi kyau.don duk abinda ba'a cika saba yafi kyau. Mutum huɗune suka rakoni,Amira ƙanwata,Maryam,sai Xainab,Sai Nusaiba,duk sunyi ankon lashi kalar arsh me masifar kyau da kuma jan kuɗi,su kuma goggoronsu kalar daek blue.sosai abin ya burge da yawa daga cikin abokan Shahid,yadda muka fito mutum biyu agabana biyu a baya ni kuma tsakiya Nusaiba da Xainab,suna riƙe da bayan riga ta wadda ke jan ƙasa. Sosai ya ke kallo na da mayun idanuwansa masu mugun tafiya dani,ganin hakan yasa na kallesa kallon cikin ido na hararesa murmushi ya yi min yana huromin iska,ni kuwa na saka hannuwa na biyu na kama iskar na saka dai dai zuciyata.tuni abokansa suka saka dariya ashe duk sunga abinda ke faruwa,kunya duk ta isheni shi kuwa ko ajikinsa. Anyi mana kyawawan hotuna masu matuƙar kyau ni ina kusa da Shahid ya saƙalo hannunsa ni kuma na riƙe nasa.sai Zainab dasu Amira suna kusa dani,shi kuma abokansa suna kusa dashi,sosai hotunan suka yi kyau,abokan Shahid sai tsiya suke masa wai ya yi musu wayo ya samo baƙar fara me kyau. Dai dai nan Yaya Bilal suka shigo da goron ɗaurin aure da su Baba usman,ganin hakan yasa Baba Usman ya ce su ƙarasa ayi hotunan dasu.Bilal kamar ya nitse a ƙasa saboda takaici da baƙin ciki,da farko ance ya zama waliyyi ya yarda,kuma yanzu ace wai za'a ɗauki hoto?tuni yaji zuciyara babu daɗi ya goge wata ƙwallar da ta taru a idonsa.hango khairat da Shahid suna ta dariyarsu abinsu,basu da wata damuwa ko kaɗan. haushi da kuma nadamar dawowarsa nigeria suka kasa hallaka sa.babu yadda ya iya haka ya shiga aka yi hoton dashi,da sauri ya yi hanyar ɓangarensu,sai gasu haidar sun taho sun ƙara cin kwalliyarsu da shadda ruwan ash irinta babansu. suka riƙe hannunsa irfan ya ce"dady jo muje ayi mana oto da mamanmu".ya faɗi hakan cikin shagwaɓa shi daman bai da magani ko kaɗan iri babanshi,wata irin harara na ɓallawa irfan na yi wuce wata sashenmu tunda su shahid sun tafi. Yana ganin na wuce sai gashi ya biyo ni ya ce"mamy don Allah kixo a ɗaukemu oto da dadynmu".?banza na yi masa kamar ban san me ya ke ce wa ba,sai kuwa ya fara kuka yana ce wa"momy me yasa bakya son dadynmu?nima idan baki sonshi nima bana sonki". Da sauri na kalli yaron na ce"get out of my room,mara kunyar banza irfan shekararka nawa yanzu just 3 years shine ka ke faɗamun haka?to ka daina sona ɗin mana".na faɗi hakan cikin fushi Duk Rashida najin abinda na ke faɗa ɗakin kowa ya yi shiru babu bakin magana. Rashida ta kamo hannunsa ta fito dashi waje,itama duk ranta a ɓace,nima suna fita na taso na koma ɗakin mama na faɗa kan gadonta na saki kuka,kamar ƙaramar yarinya sosai na ke kuka,mama ta shigo ta ce"subhanalillahi Khairat me ya faru kuma?wani abin ne ya faru?." Duk alokaci ɗaya ta yimin wannan tambayar,babu abinda ba ɓoyewa mama na abinda ya faru tsakanina da ɗana irfan.na ƙara da ce wa"mama wallahi Bilal ke zugamin yara,yanxu meye amfanin abinda yaron nan ya yimin kamar ba mahaifiyarsa ba?yanzu nan gaba yana son yara na suji tausayi na?".na faɗi hakan ina kuka. Sosai mama ke rarrashi na,ta haɗamin ruwa me ɗan ɗumi a banɗaki na shiga wanka ta ɗakkomin kayan da zan saka ina fitowa na shafe jiki na da mai lotion me ƙamshi da sanyin ƙamshi,banyi wata ƙwalliya ba na shafa hoda da ƙwalli da lipstick na zauna na yi ɗauri na me hawa-hawa,na yi kyau sosai atamfa ce amman super ƴar ubansu,ta ajin ƙarshs na yi kyau sosai,mama ta dinga yimin nasiha sannan na fito na shiga sashen babanmu. Anty halisa ina zuwa na tarar tazo ta ce"amaryar balarabe tunda nazo na ke ta jiranki amman shiru?ko dai angon ne ya ɓoye mana ke"?.ta faɗi hakan tana murmushi.na ce"wallahi kai na ke yimin ciwo amman yanzu da sauƙi." Sannu ta yimin anan take tsokanata wai na yi mugun kyau kamar wata acikin zarah.murmushi kawai na yi na zauna duk jikina ya yi sanyi saboda abinda irfan ya faɗa min. Sosai na ƙaru da nasihar da anty halisa ta yimin.tare da bani wasu sirrika na musamman,sannan ta bani dubu ɗari wai inji captain Ahmad,ita kuma ta kawomin wasu manyan followers masu shegen kyau.wanda kuɗinsu ya haura dubu hamsin ma da kuma wani flask ne gudu baƙwai me mugun kyau.abin dai gwanin sha'awa su Rashida dasu maryam ma kowanne ya kawomin gudun mawarsa dai dai gwargwado. Daman shahid yace su al'adarsu ba'a yi wa mace kayan ɗaki miji ke yi wa mace komai.babu yadda baba na baiyi ba akan akawo min kaya amman ya ce a'a su abin kunya ne ayiwa mace kayan ɗaki daga gidansu.don haka shi za yi ba komai. Amman nasai kayan kitchen masu natuƙar yawa.da kuma tsada abin dai sai wanda ya gani. Shahid da kansa yazo da yamma ɗaukar amaryarsa khairat.kamar su haidar sun sani suka maƙal ƙale ni.amman abinda ya bani mamaki kuma ya ƙonamin rai shine bai wuce yadda irfan
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87