Chapter 7
Chapter 7
FARKO TAFIYA TA MUSAMMAN.* 🔥🥚💥🌎👩❤️👨 *YADDA AKE BUƊE ACCOUNT A AREWABOOKS* Bayan kaje play store ka ɗakko ya sauka a kan wayarka. Za'a cike Form ɗin kamar haka: - *Enter your name:* (Cikakken sunanki) *Enter your mail:* (Email ɗinki) *Enter an username* (Sunanki) *Enter your password:* ( misali 12341234) *Confirm password:* (misali 12341234) Sai a taɓa *Sign Up* shikenan an buɗe account a ArewaBooks💃🏻😂. *Continue with Google* - Idan kana da gmail/email akan wayarka kawai Continue with Google za'a taɓa zata buɗe maka account a ArewaBooks kaitsaye. *Register* - Shine cike form domin buɗe account a ArewaBooks. *_AREWABOOKS LINK kai tsaye_* https://arewabooks.com/book?id=620032232dff83519bbad5a3 Masu iPhone Zaku iya bibiyar shafinmu https://arewabooks.com *miss green ce* [23/09, 16:15] Miss Green🍀: _*🥚ABIN CIKIN ƘWAI...!*_ 📃Littafi na 1 By🪶 *Ummu maher(Miss green)🍏* *GAWURTATTU 5* --------------------- *Wattpad user name* https://www.wattpad.com/user/Rabiatu333 --------------- *Arewa book user name* https://arewabooks.com/u/rabiattu0444 ------------- *Sirrinmu* manzon Allah(S.A.W)ya hanemu da saka turare idan zamu tafi don yaɗa xinar idone,don haka mu kiyaye. ------------------------ 7🟩8 . . . .Tun ka fin ta ƙarasa bakin gate ɗin taga duk babu motocin gidan,ta ce"oh mu dai Allah ya tsaremu da mugayen mata yanzu tsabar baƙin ciku don zanje nemawa jikata ƴanci shine za a ƙwashe motocin gidan a ɓoye." Ammar ta hango ɗan gidan Baba ƙasim me bin baba auwalu,da sauri ya fara neman wajen Ɓuya tunda yasan halin kakar ta su,da sauri ta ce"Zo nan Ammaru ko Ƙasimu ubanka bai isa ina masa magana ya ƙi zuwa ba,saboda uwarka ƴar borno tasha ruwan babur na baƙin hali shine ina magana zaka ɓoye?". ɗan shafa kansa ya yi sannan ya ce"haba kaka wane ni na'isa kina magana in ɓuya,ai ban isa ba yanzu dai me ki ke so?". "ayyo to na ɗauka rashin mutuncinne ta motsa tunda kasha nonon babur ƴan maiduguri".kallon kakar ta sa ya yi sannan ya ce"wai ke kaka me yasa kullum sai kin zagar mana iyaye sannan ki ke jin daɗi ne?don Allah ki daina yadda ki keson ƴaƴanki muma haka mukeson na mu".ta ɓe baki Hajiya kaka ta yi sannan ta ce"to rasai ai dole inyi zagi tunda kasha nonon rashin kunya,yanzu dai ni dai ina duka motocin ƴaƴana aka kaisu"?. kallon ɓangaren da Bilal ya ke Ammar ya yi yana jingine a jikin gate ɗin yana kallonda dramar da kakar ta sa ta ke yi,Ammar ya ce"to kaka ni kuma da ba ma hawa motar na ke ba Dady ya hanani ta ina kuma zan san wanda ya fita da motar ni motar Hajiyata kawai na ke hawa a gidannan". "to me Hajiya tunda dai bakasan inda motocin suke ba shikkenan ba sai ka gaya min kai ɗan hajiya bane,tunda ni dai ba ƴar hajiyar ba ce to shikkenan,bari inje in hau motar haya in tafi abuna ni dai yau babu me hanani zuwa ƙwatarwa jika ta ƴanci duk baƙin cikin mutum ma sai dai ya yi don ya yi ta banzar. Tana fitowa waje ta dinga tsare adaidaita amman suna ƙin tsayawa,cen ta hango Bilal yana ɗaga mata hannu cikin motarsa ya yi gaba abinsa. "Kai amman yau muguntar fulanin bauchi ta tashi ai Bilal kasha a maman ruƘayya uwarka dole ka Ɗagomin hannu a mota,yau zanga wanda ya Ɗaure maka gindi a gidan,cikin gidan ta koma tana ta banbaminta ta wuce saahen Mahaifiyar Bilal tana zuwa kuwa ta sameta a farlo tana cike wasu takaddu,da sauri ta ajje aikin da ta ke Rashida da Nusaiba suna tayata aikin da sauri suka kalli kakar ta su don sunsan aƙwai abinda ya kawota. "Yanzu Ruƙƙaya ke ce kika bawa ɗanki Bilal damar wulaƙantani a idon duniya ko?ki ka sakashi ya ƙwashe motocin gidan ya ɓoyesu don kada inje in karɓarwa jikata ƴancin ta ko?". "haba Umma ta yaya zance ya aikata hakan?wallahi ban san komai a game da hakan ba,don Allah ki yi haƙuri idan ya dawo zan samesa muyi maganar". "ikon Allah ki ma samesa kuyi maganar ba ma ki hukuntasa akan ɓata min ɗin da ya yi ba ko Ruƙayya?tunda shi Bilal ɗin shine ya haifeki ba ke ce ki ka haifesa ba ko? to shikkenan idan shi Abdullahi ɗin ya dawo ya yi masa faɗan tunda ke tsoronsa ki ke ji?". tana faɗar hakan ta yi tahowarta,Rashida ta ce"ni fa daman nasan ba alkhairi ya kawo wannan tsohuwar ɓangarenmu ba?ke dai umma kada ki yi magana don wallahi idan ki ka ce wa yaya Bilal hajiya kaka tazo nan kin san zuwa zaiyi suyi ta ɗauki babu daɗi don haka kawai ki saka musu idanu,idan ba haka ba wa ke shiga tsakanin kaka da Yaya Bilal?. shiru dai Hajiya Ruƙayya ta yi kanta na yi mata ciwo ta ce"Nusaiba ɗakkomin paracetamol insha kaina ciwo ya ke".da sauri nusaiba ta ɗakko mata a wani ƙaramin kid tasha sannan ta haɗa kayan ta koma ɗaki. Nusaiba na ganin mahaifiyar ta su ta tashi ta ce"Anty Rashida gaskiya kaka ba ta ƙyautawa wallahi kawai daga abu ya haɗota da Yaya Bilal sai ta ƙare akan Mama ai bai kamata ba wallahi,ki ga fa abinda ta kewa mamansu Khairat kulli yaumin sai ta goranta mata wai ita tuba ce?ai bai kamata ba tunda har ta musulunta." "hmm ke dai bari nusy wallahi matar nan ta tsayamin a ƙahon zuciya jira kawai na ke wataran ta taɓoni tasan ta taɓoni don abinda ta kewa iyayenmu ya isheni wallahi". "hmm Anty Rashida gwara dai abi a sannu mu rabu lafiya tunda ta kusa sheƙawa ma kowa ta huta wallahi da jarabar mafaɗaciyar tsohuwa,ai Yaya Bilal ɗin shine dai dai ita kaf gidannan,yanzu ba ta ce wai za ta faɗawa Baba ba wallahi muna nan da ke baza ta faɗa masa ba,don ni nasan irin son da takewa Yaya Bilal,suna cikin hirar ya shigo don haka suka tsuke bakinsu suna yi mai sannu da zuwa,yasha mur ya ce"ina Mama take?".da sauri nusaiba ta ce"tana ɗakinta yanzu ta shiga don kanta na ciwo". Shigewa ɗakin mahaifiyar ta sa ya yi ya barsu anan,Nusaiba ta ce"Anty wai me yasa Yaya Bilal ya fimu ƙyau ne?shiyasa magana ma sai ya ga dama ya ke mana mu dai sai fari kamar zabaya amman kuma ya fimu ƙyau." "Ke ni dai rabani da maganar wannan bawan Allah kinfi kowa sanin kunnensa yanzu ya iya dawowa ya ɓata mana rai don haka ni dai ki bar maganar". hajiya kaka ranar har kuka ta yi wai Soja ya hanata fita a gidan don yasan shi soja ne,duk wanda ya shigo ɓangarenta sai ta faɗa masa ai soja ya wulaƙanta ta. An sallomoni daga asibiti na yi garau dani kamar ba ni ba,Baba kuma ya kafa musu tsauraran sharuɗa akaina don haka kowacce ta kama mutuncinta arabu lafiya. Sanda aka sallamo ni Yaya Bilal ya koma da daddare na nufi sashensu ina zuwa na tarara da Abba da Hajiya na gaishesu na wayance na shige wajen Rashida har ta fara bacci na tasheta tana mitar waye ya tashe ta sai ta ganni ta ce"gaskiya Khairat ba ki da mutunci kinsan yau yini na yi aiki sai da wannan ɗan wahalar ya tafi sannan muka huta". mamaki ne sosai kam fuskata na ce"waye kuma ɗan wahala Rashida?".banza ta yi min ta shiga banɗaki ta fito tare da ɗauro alwala ta kalleni sannan ta ce"wa ye
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87