Chapter 50
Chapter 50
ke ɗakuna uku ne a ɓangare na,ɗakina sai nasa sai kuma ɗakin baƙi sai tsore da kitchen,sai banɗaku na har guda uku. Ni abin ma mamaki ya ke bani da kuma ɗaure kai,mutumin da ko inuwa ɗaya baya san haɗawa dani,amman wai yau shine harda wani zuwa inda na ke,nafi awa ɗaya zaune awajen har dai na gaji na ɗan leƙa ɗakin nasa,na hangosa yana shirya kayansa akan wadrope. Mamaki sosai abin fa ya ke bani,kamar wani wanda daman jinnu ne ajikinsa,to ko dai yana dasu ne?ko kuma asiri aka yi masa?tunda dai daman Anty Halisa ta ce mata wannan turaren yana karya asiri. Ɗakina na shiga,na ɗakko wayata na kira Anty Halisa tana ɗauka ban bari ta fara magana ba na gaishe ta,don yanzu ganinta na ke kamar wata uwata,don wallahi matar ta gama min komai tunda ta dawo min da hankalin miji na gare ni. Ta ce"khairat kada ki godemin ki godewa Allah,don wallahi Khairat asiri aka yi wa Bilal,don wallahi ni nasan halin Bilal,miskili ne shi sosai don yana zuwa wajen mijina kuma nasan halinsa,ke ban taɓa gani ya yi dariya ba sai dai murmushi shima sai ta kama,wannan turaren dana baki khairat yana karya duk wani asiri,abinda zan gaya miki ki ƙara tashi sosai akan addu'ah kifi ƙarfin mahassada,don na lura idan ki ka zauna sakaci abin bazai yi kyau ba,zanzo gobe insha Allah". Godiya na yi mata na yi shiru ina tuno labarin da hajiya kaka tasha bani,Gaskiyar zancen Anty Halisa aƙwai lauje cikin naɗi ko kuma saran ɓoye acikin wannan maganar tata. Abinda khairat bata sani ba shine,Bilal yana matuƙar sonta alokacin da tana ƙarama sosai,don tun haihuwarta ya ke cewa maman khairat idan ta girma zata bashi ita ya aura.sai dai kowa ya yi tayi mai dariya ana ganin ƙuruciya ce. A ƙalla Bilal ya bawa khairat kusan shekara 15,don sanda aka haifi khairat ɗin yafi shekara 14 tun tana ƙarama ya ke masifar sonta,don shifa acewarsa bazai auri mace fara ba,don shi ya gaji da ganin fararen don duk ƴan gidansu farare ne ƙal,khairat ita kaɗaice ta fita zakka,baƙa ce kalar mahaifiyarta amman baƙinta mai kyau ne,gashi tun tana ƙarama tana matuƙar burgesa sosai,bata yadda da kowa sai Bilal da kuma Hajiya kaka,sai su yini asashen Hajiya kaka,idan suna hira yakan tambayi hajiya kaka ce wa,idan khairat ɗina ta girma ita zan aura,kaka zaki bani ita?Hajiya kaka sai dai ta yi dariya tana jin daɗin hakan har cikin ranta,ta kance masa haba Bilal me zai hana kuwa?ai ko uwarta inya mura bata isa ta hana afkuwar hakan ba. Ganin irin sonda Bilal ke yi wa khairat,yasa su mama iklima baƙin ciki sosai,su ga nasu ƴaƴan ko kallonsu Bilal baiyi sai wata khairat,yarinyar ma baƙa wacce ƴaƴansu suka fita komai.daman kuma su Nadiya sun girmi khairat amman da watanni wata baƙwai nr tsakaninsu,Rashida da khairat kuma wata uku ne,Rashida ta girmi khairat,acikinsu dai Khairat ce ƙarama,don bayan maman khairat ta haifi Salim sai da ta yi shekara 8 sannan ta haihu harma ana tunanin ta gama kenan,to cikin ikon Allah sai ta haifi khairat,bayan khairat ɗinma ta sake haihuwa ta haifi maher tsakaninsu da Maher shekara uku ne. To su mama iklima fa ba suyi ƙasa aguiwa ba suka wuce wajen boka,don araba khairat da kuma Bilal,ya tsane ta tsana mai yawa wacce ko inuwa ɗaya baya son su haɗa. Ai kuwa hakanne ya faru,Bilal ya fara canjawa khairat,kunsan abin yaro ta saba dashi tana ganinsa za tayo wajensa shi kuma,ya ture ta ya tashi daga wajen,har Hajiya kaka ta gane hakan,tun daga nan ta hana khairat zuwa wajensa,ko tana kuka wai akaita gunsa sai Hajiya kaka ta hana ta,to wannan shine musabbabin tsanar khairat da Bilal ya yi. Wanka na shiga,wankan da atarihi na ina tunanin ban taɓa yin irin saba,na gurzu sosai sai da na yi kusan awa ɗaya cikin bathtube wanda na cika masa turaren wanka,daman gama haila na kenan na yi wankan tsarki,na haɗa ganyen magarya na yi tsarki dashi na wanke jikina fes,gashina na wankesa na busar dashi,sannan na fito ɗaure da tawul ina goge kaina wanda na wanke yanzu. Turus naja na tsaya ganin mutum a bakin gadona daga shi sai boxer sai singlet,jikin mutuniyarku fa ya fara rawa,mamaki,ruɗu,duk suka cika ni,tuni wannan ƙwarjinin ya bayyana akan fuskarsa,gashin ƙirjinsa dana ke gani ba ƙaramin haukata lissafina ya yi ba. Na murɗa ƙofar banɗakin zan koma sai kuwa ya ce"a'ah ina zakije? dawo mana,ke da ɗakinki,ni tafiya ma zanyi".ya faɗi hakan yana tashi. Turo ɗan ƙaramin baki na na yi sannan a hankali na fara tafiya,don tawul ɗin dana saka very small ne,ya yi guntu don da ƙer ya rufe ni,na koma gaban madubi ina wani muxurai,sai na hangosa ta cikin madubin yana tsaye yana kallona,tsoronsa sosai naji yadda na hango sa kamar wani ɗan rastling,duk jikinsa awani mummurɗe,da sauri na sumkuyar da kaina. Ya ce"mara kunyar ƙarya kawai".yana faɗar hakan ya fita,na dafa ƙirjina wanda ya ke kai kawo,anya kuwa xan iya wani jan aji yanzu,wallahi dana gansa sai naji duk ƴar nutsuwata ta shige,da ƙer na yi control ɗin kaina na shirya cikin wata doguwar riga amman ta atamfa,koda na kalli kaina sai da na yaba,saboda yadda ta amshe sosai komai a mulallinsa,na zauna na shirya ɗaurina,Xahra buhari ya yi min kyau sosai na shafa hoda na gyara girata na shafa lipstick leɓena ya yi kyau sosai daman gani da ɗan ƙaramin baki. Na samu wani ta kalmi na high hill me igiyoyi wanda ya ke kalar kayan green da kuma ja,na feshe jikina da turaren Anty Halisa,tuni na fara wani irin ƙamshi mai daɗin daɗaɗawa. Tun kafin in iso ƙamshina ya iso wajen,ya buɗe idanuwansa manya ya tsuraminsu,tuni naji ina neman gurɗewa saboda takalmin dana saka. Wow na ce azuciyata shima wanka ya buga da wata ɗanyar shadda ruwan skye blue ta yi masa matuƙar kyau,kamar ka ɗaukesa don gaskiya Yaya Bilal babu laifi ya haɗu. Bansan ina kallonsa ba sai dana ji ya ce"Yi a hankali dai kada ki faɗi?ki wani zuro min ido,da wasu ficicin idanuwanki".hararsa na yo na murguɗa mai baki na wuce dining inda na shirya abinci na,na buɗe na zuba a plate na fara cin abinci na cikin nutsuwa. Sosai ya ƙuramin ido har na tsargu na ɗago na kallesa sai kuwa ya ce"ni baza a bani abincin ba"?. A hankali na fara zuba masa ko kafin in ƙarasa zuba masa ɗin ma har ya iso inda na ke.sosai numfashinmu ya haɗu waje ɗaya,ya tsugunna agaba ya ɗakko plate ɗin abincin ya ɗebo loma ya miƙomin,na kauda kaina gefe ina wani ɓata rai.ya ƙara ɗebowa na kauce. Ajje abincin ya yi,banyo tsammani ba kawai naji anyi sama dani,sai babba ɗako wato Ɗakin Yaya Bilal,sai wani shure shure na ke amman shi ko ajikinsa shi rashin kunyar khairat ma sha'awa take basa,ai kuwa na ƙulla araina sai rafka masa rashin mutunci. Ba'azo inda na keso azo ɗin ba,aƙwai dai lokaci,amman yanzu zan nuna masa duk abinda ya baka tsoro wataran shi zai baka dariya. *Kamar yadda kuka sani na yi muku alƙawarin koya muku abubuwa a wannan book ɗin* To yanzu zan fara da maganin ƙuraje ko wani iri. *Sirrinki🌈👂🏻* 1 *Yadda ake maganin ƙurajen fuska.* Daga ummu maher Asamu garin
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87