Chapter 52
Chapter 52
khairat,sau tari yarinyar yana saka ta acikin munana,amman tabbas yarinyar kyakkyawa ce sosai sai yau ya yadda da hakan. Ganin tana kiɗanta tana rawar tane yasa jidda ta ce"oh wai ni Bilal wani salon wulaƙancin ka koyo ne?da ina ta yi maka abinda zai sakaka farin ciki amman kai hankalinka yana wani wajen cen daban".? "Jidda!".da ƙarfi Bilal ya faɗi sunanta sannan ya ce"ki shiga hankalinki sam ni ba lusarin namiji bane,wanda mace za ta yi ta faɗa masa magana yadda take so ya kyale taba,ki shiga tai tayinki".ya faɗi hakan yana nuna ta da yatsa,tasan halin Bilal ƙwarai da gaske,idan zuciyarsa ta hau yana iya aika tawa mutum ba dai dai ba,ta zauna kan kujera tana rufe bakinta da ƙarfi ta firfirto da idanuwanta waje,ba komai yasa ta yin hakan ba,bai wuce yadda Bilal ya yi mata ba,a iya saninta Bilal bai taɓa koda yi mata kallon banza ba,ko da ma ace ita ce da laifi to shine ke bata haƙuri. **** "Wai Aliyu me yasa kullum ka ke yimin wulaƙanci duk akan matarka Maryam?idan ka gaji dani ne ka sake ni mana?amman irin wannan cin fuska da me ya yi kama?".khadija ce ke faɗin hakan tana kuka. Ya kalle ta sosai cikin nutsuwa ya fara mata magana"khadija ban tsane ki ba?ina sonki sosai kamar yadda na keson Maryam,harma fiye da ita saboda ke ƴar uwa ta ce,duk da babu hadisin daya zo akan idan kana da ƴar uwa ka aure ta,kafi sonta akan waccen saboda ita wannan ƴar uwarka ce,amman ki sani Khadija an halacci zuciya abisa son wanda ya ke kyautata mata,sannan kuma tana ƙin duk wanda ya ke munana mata,to kinga abinda ya ke tsakaninki da Maryam kenan". "Ai daman nasan haka zaka ce ita tafi kyautata maka,ni dana ke gutsirar naman jikinka ina nama dashi ai sai ka yi ta zagina,tunda wannan matar taka ta shanye min miji".ta faɗi hakan tana kuka. Aliyu mutum ne mai sanyin hali sosai,matuƙar mace tasan kan na miji da gudu zata iya dashi,don sam bai da zafi sosai sai dai idan ka ƙure shi,Salim ne ɗan zafin kai irinsu Bilal. A hankali ya ƙaraso har gabanta,wani wari ya bugesa kamar ya toshe hanci,amman sanin hakan zai ƙara janyo wani hargitsin sai ya share,ya tsugunna agabanta ya kamo hannuwanta duka biyu ya manna musu wani irin hot kiss,tuni jikin Khadija ya yi mugun sanyi don yadda ya yi mata kiss ɗin. Ya kalle ta sosai ya kashe mata ido ɗaya,ai tuni khadija ta sallama masa,ya yi murmushin cin nasara sannan ya ce"ummu khairat ina alfahari dake sosai,inason ki yi min wasu alƙawarurruka har guda biyar?". Da sauri ta ce"insha Allah zan riƙe maka alƙawari mijina,Abban Khairat".ta faɗi hakan ita ma tana kashe masa ido ɗaya. Yauwa alƙawari na farko shine,kada ki dinga saka damuwar Maryam akanki har ta yi miki illa don kin san halin da ki ke ciki yanzu,ɗan cikinki yana buƙatar kulawarki sosai don haka don Allah ki daina damuwa.sannan abu na biyu ina son ki kasance mai tsafta da kula da kanki da ƴarki khairat,abu na uku ina son ki dinga tausasa zancenki wajen yi min magana,sannan abu na huɗu ki dinga yimin girki kullum a ƙalla sau biyu matuƙar ina sashenki,sannan abu na biyar ina son ki dinga riƙe min sirrina,tare da yimin ƙwalliya da kula dani". Ya faɗi hakan yana yi mata mugun smile ɗinsa mai tafiya da ita,ta hango asalin kama da mahaifinta akan fuskar Aliyunta,ta magantu ta ce"insha Allah mijina daga yau zaka same ni a mai kula da kai,ta yadda zaka yi alfahari da ni." Sosai Aliyu yaji farin ciki ya mamayesa,ya rungume ta sosai,da kansa ranar ya yi mata wanka fes suka haɗu suka yi aikin ɓangarenta dashi,zuciyarta fal farin ciki. Maryam ma da ta gama aikinta nan ɗin tazo,sai dai khadija taƘi bada fuskar yin hakan,kuma ranar Aliyu a ɓangaren maryam ɗin ya ke,sai bayan magrib sannan ya shigo,Maryam ta amshe sa kamar wani abu ma bai faru ba,ya kalle ta sosai ganin kawai dauriya take,ammsn sauran kaɗan ta fashe da kuka. Da ya ke yasan kan abinsa tuni ya bi da ita yadda ya keso.kafin wani ɗan lokaci ta saki jikinta sosai suka faɗa hirarsu gwanin sha'awa. ***** To fa tun daga wannan ranar ne na buɗe shafi salo salo,sai na lura yana guest ɗinsa yana shan iska zanzo in wuce wata,ina shawagi na ko kallonsa banyi,sai in fake da motsa jiki,ai kuwa sosai ya ke shagala da wannan ɗin,amman girman kai ya saka shi wani jan aji. Yauma kamar kullum na fito daga ni sai tree quater ɗin wando baƙi,wanda yabi jikina irin me bin jiki ɗin nan,sannsn na saka wata riga t shart wanda ta ɗameni sosai na ɗakko ruwan gora mai ɗan sanyi,na ƙulle gashin kaina ma'ana na saka ribom ai kuwa ba ƙaramin kyau hakan ya ƙaramin ba,da ya ka irin gashina mai taushi ne wanda ake kiransa roba roba,kuma sai ya yi kamar na yi doughnut ɗinsa ya yi cukus,kamar black american,na saka konbus ɗina mai kyau,irin na mata na fito abina ina ɗan gudu kaɗan,ai baki ɗaya ya shagala da kallona ina kallonsa,na cigaba da bubbuɗawa kamar yadda na saba yi masa. Sai ga jidda nan ta fito,ganin abinda ke faruwa yasa ta kusa daskarewa awajen,ta kalleni taga harkar gabana na ke,ta kalli mijinta taga shi kuma aikin kallo na ya ke. Kawai ganinta na yi agabana tana wani muzurai cikin fushi ta ce"dalla malama koma ɓangarenki zaki fito kina wani muskutawa,kina neman ki haukata mutum". Dariya sosai na yi kamar na mayar da ita mahaukaciya sannan na ce"oh ikon Allah jidda ki ke kowa?don Allah ki matsa daga kusa dani banda lokacinki,saboda ni dai ina da abinyi,kuma don Allah kiɗan matsa don wallahi wari ki ke kamar mushe?". . .✍🏿 07068606171 *GAWURTATTU BIYAR, TAFIYAR TA MUSAMMAMN CE. 👯♀️👎👇👇* 1, *MU GANI A ƘASA...*🔥 _Ummu Affan_ 2, *ABIN CIKIN ƘWAI..*🥚 _Ummu Maher_ 3, *GUNTUN GORO..*💥 _Mom Islam_ 4, *GISHIRIN ZAMAN DUNIYA*🌎 _Mrs Bukhari_ 5, *AUREN WATA TARA*👩❤️👨 _Miss Hajo_ Guda biyar 1k Guda huɗu N700 Guda uku N600 Guda biyu N500 Guda ɗaya N300 *DOMIN TURA KUƊIN KAI TSAYE*👇 0037219728 Fatima Rabiu Sunusi StanbicIBTC Bank. Domin tura shaidar biya👇 0810 433 5144 Masu tura katin MTN👇 0814 179 9224 Ƴan Ƙasar Niger zasu tura nasu anan.👇 0817 952 3215 Guda biyar 1000f Guda huɗu 700f Guda uku 600f Guda biyu 500f Guda ɗaya 300f *TEAM GAWURTATTU BIYAR TAKUN FARKO TAFIYA TA MUSAMMAN.* 🔥🥚💥🌎👩❤️👨 _*Miss green ce*_🤙🏿 [23/09, 16:24] Miss Green🍀: *_🪺ABIN CIKIN ƘWAI🪺_* 📃LITTAFI NA 2 UMMU MAHER(MISS GREEN🍀) Wattpad user name Rabiatu333 Arewabooks rabiattu0444 *Matso kiji*👂🏻 Kada ki kasance mai yawan yiwa mijinki musu wallahi yin hakan yana dakushe ki a wajen mijinki don haka a kiyaye,ba da faƊa ko fushi miji ya ke saka ya soki ba,A'ah da rarrashi da kissa ake mallake miji. ------------------------- 59. . . . .60 . . .bai ajje ni a ko'ina ba sai kan kyakkyawan gadonsa,da sauri na tashi cikin tsiwa na ce"haba mlm saboda me zaka wani ɗauke ni kamar ƴar tsana?don Allah ni ka daina shiga harka ta". Murmushi ya yi irin na gefen baki sannan ya ce"a'ah nifa ban shiga harkarki ba,kece ki ke shiga harka ta ni yanzu ma fitar min
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87