Chapter 66
Chapter 66
ta dafe Ƙirjinta ta ce"yau na shiga Ɗaka ban fito ba ni Ramatu,kai Bilalu me ka yi mata?da sauri ya kalli hajiya kaka ya ce"kaka don Allah ki taya ni bawa khairat haƘuri ta yafemin don Allah".da sauri hajiya kaka ta ce"a'ah badani ba?kai sunduƘi ne da baza ka iya bata haƘuri ba?to ni dai babu ruwa na Allah,Kuma kazo ka fitar min aƊaki tunda ba Ɗakin RuƘayya bane,ba kuma da kuƊinta muka haƊa muka siya ba,itama dai cin arziƘi take ko?to maza yi hanyar waje,indai na kallon wannan koƊaƊƊiyar fatar ta ka". Sosai maganar hajiya kaka ta basa haushi ya fita fuuu,hajiya kaka ta ce"uwarka RuƘayya ita ka kewa wannan haushin kamar kare amman fa ba Ramatu ba."ta faƊi hakan tana hararata ta ce"yauwa sauran kuma wataran yazo ya yi miki daƊin baki ki sakar masa fuska,tunda bakisan inda ke yi miki zafi ba,kema sai kin rama duk Ɗibar albarkar da akayi miki,ni Ɗinnan zan baki goyon baya ki luguiguitamin shi ya yi liss,wannan Ɗaga kan nasa duk sai ya daina sa." ni haushi ma kalaman kaka suka bani na ce"ni don Allah kema ki fita ki barni ni kaƊai,kuma ni ce miki na yi zan kulasa,ni dashi har abadan wallahi,sai dai ya nemi wata matar ya aura amman ni na tsanesa wallahi".ƙuri hajiya kaka ta yimin da ido na magantu na ce"a'ah lafiya kuma ki ke kallo na?". Sai kuwa ta fara magana cikin fushi"wato kin tsanesa ko?to ki kashe sa mana?Ai kanki ki ka yiwa asara ba Ramatu ko RuƘayya ba,ko kuma Abdullahi bawan Allah ba,Ɗanki ki ka yiwa asara don shine zai taso maraya,don kinga nidai ina da ƳaƳa da jikoki da yawa kinga don na rasa Ɗaya bazanyi hauka ba".Ta faƊi hakan tana harara ta,ranar faƊa sai da mukayi faƊa da hajiya kaka don kuwa ko girki ma da kaina na tashi na yi danaji uwar yunwar dana keji tana neman kassara ni,don har yanzu ban daina wannan mugun cin ba,da za'aajjemin indomie huƊu tas zan cinye,ai kuwa bayan na daga jallop Ɗin taliya me ruwa ruwa wadda taji nama sosai taji attaruhu,na baje a falonta na zauna ina ci,ciki na kuwa ya yi kamar tulu idan zan tashi da Ƙer na ke tashi yanzu sai da dabara. Taliya Ɗaya na dafa na zauna ina ci hajiya kaka ta harare ni sai kuwa ta fara magana kamar za tayi kuka ta ce"ni dai wallahi Bilalu ya cuce ni daya sakeki ki ka zo kina cinye min abinci na,jiya ma fa taliya biyu ki ka cinye gaba khairat,wannan wani irin cine haka?ni wallahi ina tsoro ko ƳaƳan aljanune suke cinye wannan abincin da ki ke ci"?.da sauri na kalleta ina lomar taliya ta na ce"Allah ya tsare ni wallahi,ni ki daina yimin wannan fatan gaskiya,kaf ƳaƳanki da jikokinki babu ƳaƳan aljanu,kawai ni kuma sai ki wani ce ƳaƳan aljanu ke ciki na?". Da sauri ta ce"a'ah fa khairat dole inyi magana gaskiya,barni in faƊi gaskiya wallahi,ga cin nama kamar kura sai ki cika min naman miya acin girkinki,ni wallahi ina zargin ma kina cinye kilo biyu kullum,nima naga ai ba kullum ake kawo min naman miyan ba".da sauri na kalle ta na ce"kaka nifa wallahi ki barni tunda dai aƘwai abincin ki barni inci haka kawai in zauna da yunwa".muna cikin wannan fafatawar yaya Aliyu da babanmu suka shigo,na yi yunƘurin tashi sai naji na kasa dole ne na zauna na gaishesu,babs ya kalleni cikin tausayi na ya ce"ya jikin na ki khairat"?. "Da sauƘi baba". Murmushi ya yi sannan ya ce"kina zuwa asibiti kuwa"?.kunya duk ta isheni sai na ce"a'ah Baba bantaƁa xuwa ba".da tsoro ya ke kallona sannan ya ce"haba khairat yaya mace me ciki zata zauna bata zuwa asibiti?ai bazai yiwu ba ko".?da sauri hajiya kaka ta ce"yauwa gaya mata dai,kaima da ka ke namiji kasan dai dai ba?amman wannan yarinyar sai binta na ke akan taje asibiti amman fafur ta Ƙi zuwa,koda ya ke dacen ma fa cewa ta yi wai zubar da cikin za ta yi?." Da sauri Baba da yaya Aliyu suka haƊa baki wajen ce wa zubar da ciki kuma?".Hajiya kaka ta ce"eh Ƙwarai kuwa ai yanzu wannan khairat Ɗin da kuke gani ba irin tada bace,ta yanzu sai fitsara abu kaƊan ta hauka da rashin kunya ko kuma musu,ga taurin kai kamar ubanta lokacin yana yarinta". ta kalli babanmu tana hararata,Baba kunya ta ishesa ya ce"kai amman khairat abin ya bani mamaki,ina iliminki na addini?ina wayewarki take?ai ko jahili bazai zubar da ciki ba.amman ke da hankalinki".nan dai Baba ya dinga yimin nasiha sosai,na fashe da kuka na ce"kuyi haƘuri insha Allah bazan Ƙara ba,nima ba laifi na bane laifin zuciyata ne,sai inji wani lokacin duk haushin kai na ma nake ji,balle kuma wani shiyasa duk na ke hakan". Baba ya ce"babu komai a halin da ki ke ciki ai ya kamata ayi miki uzuri,don haka idan har ki kaji kina jin hakan ki dinga addu'ah sosai".na Ɗaga masa kaina yana Ƙasa,sai kuwa kaka ta ce"yauwa malik kada kaga abincin da ka ke kawowa yana saurin Ƙarewa.To ba wani ke cinyesa ba sai wannan buhun simintin Ƴarka,wallahi taliya biyu take cinyewa kullum,biredi Ɗan Ɗari uku cinyesa take,naman da kuke siyomin wallahi idan aka siyomin na sati Ɗaya yadda ake da,to fa wannan aƘwana biyu take cinyewa". sosai abin ya bawa su Baba dariya,yaya Aliyu ya ce"caƁƁijan ki ce nima in Ƙaro kuƊin da na ke Baki ko?".da sauri ta ce"ai kuwa dai don Ƙanwarka rumbu ce yanzu,shima Bilalu bari yazo sai ya dinga ajjemin kayan abinci buhu buhu".dariya muke ta yi hardani Ɗin amman tana ce wa Bilalu sai naji duk zuciyata ta yi Ƙunci. Baba ya ce mu shirya zamuje duba Baba Abdullahi daga nan sai a duba lafiya ta,haka kuwa aka yi doguwar riga na saka buba me buƊewa saboda yanzu duk kayana sunyi min kaƊan sosai,ai kuwa ciki na ya Ƙara tsini sosai,hijabi na saka har Ƙasa,ruwan coffie wanda ya haskani sosai,daman gashi na yi mugun fari. muna fitowa hajiya RuƘayya ma ta fito har da Bilal,ya hangoni naga yana yimi kallon tsaf,murna fal zuciyarsa yadda yaga khairat na tafiya da Ƙer sai abin ya basa tausayi sosai,yana so ya taimaka mata amman kuma yana tsoron abinda zai biyo baya,motar yaya Aliyu muka shiga da ya ke jip ce,kusan mazaunanta 14 ne,hajiya RuƘayya sai wani nan nan take dani,ni dai kallon kowa kawai na ke,nidai hankalina yanzu yana kan cikina in haihu lafiya in basu Ɗansu don ni yanzu hankalina ya koma kan karatuna don ma su zainab na taya ni wasu abubuwan . jikin Baba Abdullahi ya yi sauƘi sosai don ranar ma yana zaune ana ta hirar yadda abin ya faru,yaya Aliyu ya ce"kai gaskiya Ƙasar nan tamu aƘwai gyara,yanzu fa babu yadda za'ayi ace gwamnati bata san abinda damas ya ke ba,amman anyi shiru an zuba masa ido,yana Ɗibar yaran mutane kamar awakai".wani tunani ne ya faƊomin azuciyata na ce to Allah ya cika min burina,amman tabbas ina son kawo Ƙarshen zaluncin damass. hajiya kaka na ganin duk an taru ta ce"yauwa Bilalu riƘe jakar khairat ka rakata Ɓangaren masu ciki don a binciki lafiyarta".ai kuwa da sauri ya ce"to. . .to kaka bari in rakata".ya faɗi hakan cikin zumuɗi. Wata muguwar
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87