Skip to content

Chapter 39

Chapter 39

Abin Cikin Kwai Book One Complete Hausa Novel 1,303 words 0 views Progress saved
Download Book

dubu ɗari biyar haka ta bayar wai duk don ta dawo budurwa. Sosai iyayenta suke tuhumarta akan kashe kuɗinta,amman da ya ke tana musu ƙarya da Bilal sai suka daina tuhumarta ta cigaba da wandaƘarta da kuƊaƊa,sosai ta ware kuƊi don siyan wasu kayan kitchen da sauran abubuwa. Alhaji damas ys samu yadda ya keso,don haka yanzu wani kallon tara saura Ƙwata ya kewa Bilal,gani ya ke tamkar fankonsa ya ke ganinsa,tunda wadda ya bawa amanarsa,ya Ɗauketa matsayin mai tarbiyya to fa ta watsar da komai ga Alhaji damas,ta bashi komai ta yadda shi Bilal Ɗin ko alfarmar riƘe hannunta bai samu ba. sosai wannan abu yake masa daƊi saboda ko ayanzu ya gama da Bilal, gamawar har ya mutu bazai taƁa mantata ba. **** koda aka tashi yin dinner babu yadda Rashida bata yi dani ba,akan inje dinner Ɗin naƘi zuwa tunda dai ni ba sona ake ba,to kuma me zanje inyi?Don yaya Bilak bazai ji kunyar wulaƘanta ni awajen mutane ba. Da Rashida tarasa yadda za tayi dani sai taje ta sanu yaya Aliyu ta gaya masa komai,yazo ya yi min faƊa akan inje,kuma su yaya salim ma duk zasuyi idan har banje ba baza suji daƊi ba,haka dai na haƘura amman can cikin zuciyata tsoro fal. Ana cikin maganar hajiya kaka ta fito daga kinta baya sun gama faɗa da mero.sai kuwa ta ce"kai Aliyu rabu da ƴar banza,ina cewa nan naji kina gayyatar ƙawayenki fatin?sai yanzu za'a wani zo ana wani rarrashinki akan kije?to yasin kada kije ni daman haka zanso sai in hakimce akan kujerarki ince ni ce uwargida. Duk wanda ke wajen sai da ya yi dariya sosai,ni kuwa kallonsu kawai na ke,ɗaurin aurena da za'ayi da Yaya Bilal shine kawai ya tsayamin aƙoƙon zuciyata,ko wani irin zama zanyi dashi oho?. Ƙwalliya aka yimin sosai wacce ni da kaina sai da na yaba kaina,wani farin les ne wanda ya gaji da haɗuwa gashi yaji ruwan stones sai walƙiya ya ke,kamar ka ɗaukeni,ƴar pos ɗina da kuma takalmi na duk ash ne suma sunji ruwan stone,diri na sosai ya fito da ya ke ni dirarriyar macece,sai na haska na yi wani irin bajajjan ƙyau wanda ya amsa sunansa aƙyau,head ɗina ma arsh ne sai net golden shima sai walƙiya ya ke,aka yafamin shi akaina. "Wow gaskiya amaryarmu kinyi ƙyau sosai,gaskiya yaya na zaiyi santin kyaun nan".cewar Rashida wacce ke ta faman ɗauka ta a hoto kamar babu gobe. Bansan lokacin da naji wani hawaye yana zubomin ba,da gudu na tafi naje na rungume mahaifiyata tsam kamar wani zai ƙwacemin ita,i'tama ɗin rungume ni ta yi tana ɗan buga bayana tana rarrashina,har cikin zuciyarta take jin babu daɗi arabuwa da tilon ƴarta mace da zata yi. Su mero ana gefe ansha ƙwalliya sai ka rantse ba meron hajiya kaka bace,ganin khairat na kuka dai yasa duk jikinta itama ya yi sanyi sosai,ta koma gefe ta rakuɓe tana kallon uwarta hansai wacce ke ta shirinta cikin haɗaɗɗiyar atamfarta super wacce Hajiya kaka ta bata. Itama da gudu taje ta rungume hansai tana ta kuka,Hajiya kaka ta ce"kai ku ganemin wani shashanci,don kunga iyayenku na wajen suna ƙefta muka idanuwa ku taso kuyi kuka shine zaku faramin kuka kamar gidan mutuwa?to wallahi ba dani ba,duk shegiyar da ta ƙaramin kuka yasin sai na saka jikana fasa aurenta". dukkanmu juyowa mukayi muna kallon hajiya kaka,wacce ta yi mirsisi kamar ba ita ce ta yi maganar ba,ta ɓantari guntun goronta ta saka abakinta tana tauna,ganin duk muna kallonta sai kuwa ta ce"meye ne kuma kuke kallona?To wallahi kuruwa ta kurr akanku,ina ƙwanannan aka samu wata shegiyar ta yi min asiri cikin matan ƴaƴana?duk da ban yarda da hakanba,don ni dai naci dubu sai ceto,mai dambu kafin ta mutu ta barmin tsari ajikina.kunga kuwa kuma sai dai kuci kanku".ta faɗi hakan tana zare fici-ficin idanuwanta. Dariya mero ta tintsire da ita sosai sannan ta ce"ah to mudai ma idan mayun ne ai sai dai kece kika shafamin?Tunda nidai Babana ƙaninki ne,ita kuma khairat kece ki ka haifi Babanta,kinga kuwa sai dai daga kene wannan matsalar". Hawaye kaka ta farayi sannan ta ce"Allah ya isa na mero da wannan zagin da ki kayimin,kuma wallahi ki yi asannu,don ba ƙaramin aikina bane in saka jikana ya fasa aurenki". Dariya sosai mero ta yi sannan ta tashi taɗan riƙe doguwar rigarta mai kalar blue da fari da ƙaton takalminta me tsini kalar blue,ta tashi a hankali don takalmin shirin faɗar da ita ya ke,a kunnen hajiya kaka taje ta raɗa mata wani abu,ai da gudu ta fita Hajiya kaka tana ce wa"wallahi uwarki hansai ki ka faɗawa magana bani ba,ƴar banzar yarinya mara kunya".ta faɗi hakan tana fashewa da kuka. Kunsan me mero ta raɗawa hajiya kaka?Hmm ku matso kunnuwanku kuma kuji,cewa ta yi to idan ya fasa aurena ke zai aura ki haifa masa yara. kun san kuwa dole maganar ta yiwa hajiya kaka zafi,har aka fara tayi party ɗin bani da niyyar tashi,mama sai rarrashina take amman kukan ƙara bulbulowa ya ke tamkar dai an buɗe famfo. Itama hajiya kaka na bata tausayi sosai,ta rungumeni tana bubbuga bayana sosai da ƙer dai hawayen ya tsaya.Rashida tana tsaye itama kukan take tana sharewa. Tabbas dole ne khairat ta yi kuka,saboda ko ba don komai ba sai abinda ya faru da ita,tasan halin yayanta tsaf yana da zargi sosai,bazai taɓa amsarta amatsayin matarsa ba,musamman yadda taga mahaifiyarsu na nunawa akan auren yaya Bilal da khairat,ta kasa gane cewa komai muƙaddari ne daga Allah,Daman Allah ya ƙaddara khairat matar Yaya Bilal ce babu yadda kuma za'ayi don Allah ya ƙaddara faruwar hakan. Da gudu Rashida ta taho ta rungume khairat,ta bayanta tana ta kuka itama,tuni suka fara bawa Hajiya kaka haushi ta ce"Innalillahi gaskiya nidai ku fitarmin daga ɗakina tunda babu wanda ya mutu balle ku sakani agaba kuna kuka,kamar za'a kaita inda za'a dinga figar namanta ana miya dashi?Haba abinnan ya yi yawa wallahi,duk kowa ya tafi wajen partyn har wannan uwar rawar kan mero ta tafi amman ke kina zaune kina aikin kuka." Mama ce ta rarrashemu mu duka har bakin motar da zata ɗaukemu sai da ta kaimu sannan muka shiga ita kuma ta dawo,ƴan uwanta da sukazo tare muka tafi,don ita ta ce baza ta jeba,don haryanzu zuciyarta bata mata daɗi idan ta kalli gidan mijinta da ta bari abisa sharrin da aka laƙabawa ƴarta,shi kuma Malik ba tare da binciken komai ba ya ɗora mata laifi,bayan wannan ma har da tukuicin saki,ta goge hawayen da suka zubo mata. Hajiya kaka na kallonta tausayin ta duk ya cika mata zuciyarta,ita fa har yanzu bata yadda da abinda aka faɗa akan khairat ba,tabbas aƙwai saran ɓoye acikin lamarin. **** wani irin mummunan bugawa naji gabana ya yi,hango Jidda wacce ta gaji da haɗuwa wajen yin ado da ƙwalliya,ga gogan A.D a kusa da ita,ta saƙalo hannunta ta bayansa ana musu hotuna,na kalli kujera ta babu kowa akai,na rasa tudun dafawa na tsaya kawai,ganin abinda ke faruwa yasa Rashida zuwa wajena,ta riƙemin hannuna ta kalleni sosai cikin dakiya ta ce"khairat ki nutsu fa,kada ki diririce yadda ki ke aduk sanda kiga yaya Bilal,muje ki zauna".ta riƙe hannuna har kan kujera ta. Na zauna duk jikina a sanyaye,ina kallonsu ta gefe,ko ƙura ta basu

Table of Contents

Chapters

87 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87