Chapter 8
Chapter 8
kika fara zuwa har Mabrookah ta hanaki shiga" Sai a sannan Ummy ta shedata tad'anyi murmushi tace "Na tuna" Dattijuwar tace "Sunana talatu, tun ranar dana ganki naji kin kwanta min a rai ganin sauk'in kanki da kuma tarbiyarki. Lallai kin chanchanci aikin da aka saki" Laurat tace "Mama Talatu anma Hajiyar nan batada hankali ina aka tab'a ba yar aiki gyaran d'akin miji" "Kull 'yar nan, kinsan dai irin gidan da kike. Ki kama bakinki kisa masa lunzami" Turo baki Laurat tayi ta cigaba da aikinta, Mama talatu ta kalli Ummy tace "Wannan wani aiki neh babba Ummy, ki kula ki tsare gaskiya. Kinsan zuciya batada k'ashi, kiyi taka tsantsan da duk wani abu da kika gani, kada ki zama mai yawan bincike. Ki tsaya a matsayinki inda aka ajeki, banda shishigi akan alamuran gidan nan kinaji" Kai Ummy ta gyad'a tace "Nagode Mama Talatu Insha Allahu zan kiyaye" Mama talatu tace "Sannan duk abinda baki ganeh ba ki tambayeni, ni ina b'angaren masu share share neh kinji" Ummy ta k'ara gyad'a kai, Mama talatu ta masu sallama tabar wajan. Laurat ta aje wuk'art hannunta tace "Aike Ummy kakarki ta yanke sak'a, kinsan su masu kud'in nan wani lokacin mantawa suke da kud'i idan suka aje" Ta juya ta kalli gabas da yanma ta waigo tana kallan Ummyn "Karki dai manta dani, idan kin samu ina nan" Dariya Ummy tayi ta mik'e tace "Laurat kenan kinada matsala, barin dawo zamuyi magana" Sama ta haura b'angaren d'akinsu Hajiya, d'akuna ne wajan guda shidda, biyun farko na Hajiya ne da Mabrookah, k'ugu ta rik'e tana kallan d'akunan, na kusada na Hajiyan ta hannun hagu ta saka keyn, murd'awa taitayi yakiyi ta zare tareda murd'a kofan d'akin, take ya bud'e tad'an tab'e baki ta tura ta shiga. Wani sanyi neh da k'anshi ya dakan mata hanci, a hankali ta shiga tana b'in d'akin da kallo, sosai d'akin ya burgeta komai na d'akin blue hatta labulen d'akin blue neh, d'aga ido da zatayi ta hango mutum zaune kan wheell chair yana facing windown d'akin. Ummy Abduol✍🏻 [3/12, 8:23 AM] +234 806 215 4020: ♠♠♠♠♠♠♠♠ ♠♠♠♠ *JAMALUDEEN* ♠♠♠♠ ♠♠♠♠♠♠♠♠ By *Ummy Abduol* Dedicated to My *Late Siblings* Page 11 A rud'e tabar dak'in jikinta na rawa, bak'in k'ofan ta tsaya tana kallan cikin d'akin, har lokacin yana kallan windown bai juyo bah. Jim tayi wani zufa ya karyo mata, sad'af sad'af ta k'ara shiga d'akin jikinta na cigaba da rawa, ta zagaya gabanshi tana kallan fuskarsa. Kyakyyawan saurayi ne wanda a k'alla zaikai shekara ashirin da biyar ko fi, fari ne daidai misali dan baya sahun bak'ake, kuma baza'a kirashi wankan tarwad'a bah dan yanada haske. Gashin kansa nada yawa mai tsayi yayi curl sai shek'i yake. Saje ne kwance kan kyakyawar fuskrsa wanda ya k'ara masa kyau da kwarjini. Idanunsa yan madaidaita masu kyawun gaske, hancinsa ma ba dogo baneh sosai saidai yayi daidai cikin 'yar fuskarsa mai d'an tsayi. Bakinsa irin light red d'in nan neh madaidaici cikin fuskar tasa. Lumshe ido Ummy tayi ta bud'e tana cigaba da kallanshi, har lokacin idanunshi na kallan windown ko kyaftawa baiyi ba balle yasan da mutum a wajan. Hannu tasa tad'anyi motsi wajan idanunsa anma ko gezau beyi bah, kurrri tamai gabanta na cigaba da fad'uwa anya wannan mutum nada rai kuwa. Jim tad'anyi na wani lokaci sannan ta fita daga d'akin tana waiwayonsa. Sosai alamarinsa yabata mamaki, a sanyaye ta bibi duka sauran d'akunan tasa keyn anma beyi bah, k'asa ta koma ta samu Laurat tana aikace aikacenta, zama tayi duk jikinta a mace, Laurat ta matso tana kallanta "Yadai Ummy meh aka samo mana neh" Maganan Laurat dariya ya bata tad'anyi murmushi tace "Laurat knan, maganarki yana bani mamaki, rik'on amana na d'aya daga cikin abinda ke sa a k'ara yarda da kuma san mutum." Ta mik'e tana murmushi tareda dafa Laurat "Banida ra'ayin abinda kike fad'i, burina na kasance mai kiyaye duk wani doka da aka shimfid'a min, banasan wuce gona da iri akan lamuran dabai shafeni bah" Laurat tayi jim tana gyad'a kai "Gaskiya kika fad'a Ummy" Taja hannunta suka zauna ta kalli Ummy tace "Ni y'ar garin kaduna ce a anguwar tudunwada, na taso bansan iyayena bah ina hannun kakata wacce itama ta tsufa. Na tashi cikin talauci da matsin rayuwa saboda itama kakar tawa batada k'arfi, Iyayena y'an garin kano neh so d'aya ta tab'a kaini wajansu, suma basuda k'arfin da zamu iya rik'eni. Hawaye ne suka gangaro mata tasa bayan hannu ta share tace "Wanchan shekaran kakar tawa ta rasu, nan na koma hannun wata dilalliya dake nan mak'otan mu saboda banida kowa, shine ta d'auko ni ta kawoni nan, yanxu kimanin watana takwas knan a nan" Ummy ta tausaya mata sosai, tasa hannu tana share mata hawaye "Ki daina kuka Allah yana tare dake, insha Allahu rayuwarki zan inganta nan gaba" Gyad'a kai Laurat tayi ta mik'e ta cigaba da aikinta, Ummy tace "Banfa gyara d'akin bah" "Meyasa?" Laurat ta tambayeta Ummy ta sauke ajiyar zuciya tace "Ni duk d'akunan dake sama ba wanda ban sa keyn ba baiyi bah, kinma san wani abu kuwa?" "Aa meya faru?" Laurat ta tambaya, Ummy tace "Wani d'aki na shiga naga wani mutum zaune a kujeran guragu gashin nan dai kamar baida rai" Murmushi Laurat tayi tace "Sau d'aya na tab'a ganinshi tunda nazo gidan nan, nima yanda kika ganshi haka na ganshi" Da damuwa Ummy tace "Tho shi wanene?" Laurat tace "Ance d'an su Hajiya neh" Kai Ummy ta gyad'a ta kauda maganan. Hajiya bata dawo gidan ba sai bayan magriba, bayan ta huta Ummy ta sameta a falo ta gaidata tareda shida mata bata gane d'akin bah. Murmushi Hajiya tayi tace "Ummy kenan, ba a nan b'angaren d'akin Alhaji yake bah, b'angaren dake kusada nan nan neh b'angarensa, bakiga makullin falo baneh" Sai a sannan Ummy ta duba tagani, Hajiya tace "Gobe in Allah ya kaimu ki tabbatar kin gyara" "Tho" Ummy tace ta mik'e ta mata saida safe ta tafi d'akinta. Washe gari kamar kullum tana gama gyara d'akin Hajiya dana Mabrookah ta wuce b'angaren Alhaji, Sakin baki tayi ganin Aljannar duniya, nesa ba kusaba b'angaren Alhaji yafi nasu Hajiya kyau duk da suma nasu ba baya yake ba. Gyara tayi sosai dan b'angaren yayi datti dayawa. Haka kullum take aikinta, ta gyara d'akin Hajiya dana Mabrooka ta kuma gyara na Alhaji, tun daga ranar bata k'ara ganin mara lafiyan nan ba duk da kullum idan ta hau sama gyara saita kalli d'akin, yanzu ta gane abinda likitocin nan keyi kullum a gidan. Yau wankin Inner wears d'in Mabrookahn ta kwaso dan ta mayarda ita kamar jaka. wankin kayanta itace duk da akwai washing machine dake gidan, Guga, da duk wasu sauran ayuka duk ita take mata. K'asa ta sauka zuwa bayan gidan inda ta saba wankin itada Laurat suna hira, Tsohon nan maiba flower ruwa ne ya k'araso wajan yazo cire tiyo daga jikin famfo, Gaidashi Ummy tayi ya amsa da fara'a dan yanzu sun saba dashi sosai, so dayawa idan tazo wanki sukan had'u wani lokacin suyita hira dashi. Itama Laurat ta gaidashi ya amsa yana cewa " 'yata wanki akeyi neh" "Eh Baba, ya aiki" Ya amsa da lapia lau, har zai wuce
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82