Skip to content

Chapter 74

Chapter 74

Jamaluddeen Book One Complete Hausa Novels 1,200 words 0 views Progress saved
Download Book

kallo d'aya ya mata ya kauda kai gefe, Ledan Takeaway da sukayo ya aje mata nan falon ya haura sama, binsa da harara tayi tare dajan tsaki ta mik'e ta d'au ledan tana dubawa. K'amshi ne ya masa sallama yana haurawa Falon, jin motsinta a kitchen yasa ya k'arasa cikin sand'a, tuwon semo ya samu tana tuk'awa tana haki kamar wacce tayi gudu. Tausayinta ne ya kamasa ya k'arasa ya zagaye k'ugunta da hannunsa yana mata sannu, murmushi ta masa tana cigaba da aikinta. Tayata ya soma yi har suka gama, ta had'a komai a tray ta mik'a masa tana turo baki "Dan Allah kakai ma Abba, naji baici wani abinci bah" Farinciki ne ya lullub'esa mara lissaltuwa, ya amsa Trayn "Thank uh so..." Tayi saurin rufe masa baki tana girgiza masa kai, a sanyaye ya fito daga kitchen d'in ya koma side d'in Abban, Ammi na ganin Abincin ta soma hawayen farinciki "Son Allah ya maka Albarka, ka samu mace ta gari. Allah ya baku zuri'a ta gari" A hankali yace Ameen Sosai Abba yaci abincin dan ya masa dad'i sosai, Saida ya gama sannan ya wanke hannu, Hannu yasa a aljihun Rigansa ya ciro tsabar kud'i masu yawa ya mik'a ma Jamal d'in "Gashi kaba surukata, Allah ya mata albarkah" Ya amsa yana murmushi tare da godiya. Koda ya koma ya samu tayi wanka ta kwanta tana bacci, sosai yayi mamakin Saurin baccin Ummy kwana biyun nan. Gefenta ya kwanta ya shige jikinta shima nan da nan bacci ya d'aukesa. Ba ita ta farka ba sai bayan la'asar, salati tayi ta mik'e ta shiga toilet tayi wanka ta fito tare dayin sallah. Ranar gaba d'aya hidima tayi da sirrukanta, har Mamaki Abba da Ammi suke na irin karramasu da Ummyn keyi. Albarka ko tasha shi wajan Iyayen mijin nata dashi kansa Jamal d'in. Washe gari Areefah ta diro garin zaria itada da drivern su Abban, k'arfe sha d'aya na safe a gidan ta musu tare da taimakon Jamal dayayi tama Drivern kwatance. Sosai tayi murnan ganin iyayen nata, bayan ta huta Ammi ta umarceta data je side d'insu Ummy ta gaishe su, hakan ko akayi, a falon k'asa ta had'u da Mabrookah ta gaisheta, dakyar ta amsa tana yatsine fuska. Areefah ta tabe baki dan a rayuwarta babu abnda ta tsana kamar wulak'anci, Sama ta haura a falo ta had'u da Ummy itama kwance kan kujera Ummy najin sallamanta ta mik'e zaune tana mata murmushi, ta k'arasa ta zauna tare da gaisheta Da fara'a Ummyn ta amsa tana ta kallanta ganin tsantsar kamar da suke da Jamal kamar an tsaga kara harma tafi kama da Jamal fiye da Areef, Ummy ta mik'e tana cewa "Barin samo miki wani abu" Tayi saurin cewa "No Aunty Thank uh. I'm Ok" Ummy tayi kitchen tana cewa "Aa wallahi ai bazai yuwu kixo wajena bakici komai bah" Ya shiga kicin ta kawo mata drinks da 'yan kayan motsa baki. Yanda Ummyn ta tarbeta yasa ta saki jiki ta soma mata hira, Areefah akwai Barkwanci. Daga k'asa Mabrookah keta jin dariyansu, ranta ya k'ara b'aci lallai idan tayi wasa sai Ummy ta kwace mata mutane. Taja dogon tsaki ta shige d'akinta. Tare da Ummy sukayi Sallah, Da taimakon Areefahn ta had'a ma su Ammi abinci a Warmers Areefah ta taimaka mata suka kai. Ammi da Abba sai albarka suke saka mata. Bayan ta fita Areefah ta zauna kan dinning tace "Abba nan gidan wanene?" Ammi ta bud'e baki zatayi magana Jamal da Areef suka shigo falon da sallama, kurrrri tama Jamal tana kallansa, ganin yana kama da Areef, ya k'araso wajan ya tsugunna ya gaida iyayensa. Abba da Ammi suka amsa da fara'a, Itama ta gaidasa ya amsa cikin fara'a yana cewa "Uh welcome sister" Murmushin yak'e ta masa ta d'au spoon d'in gabanta ta saka cikin abincin tana kallansa k'asa k'asa. Ganin sun zauna kan dinning d'in shida Areef dake ta hararanta yasa tad'an kalli Ammi cikin rad'a tac "Ammi wanene wannan" "Just eat" Ammi tace mata. Kasa sakewa tayi sai kallan Jamal take dake ta hira dasu Ammi suna cin abinci. Bayan sun gama Abba ya mik'e ya koma falo, Areefah na ganin haka ta mik'e dasauri ta bisa, Kusa dashi ta zauna tana tura baki "Abba were are we? And hu is he" Ta nuna Jamal dake tahowa shida Areef, Murmushi kawai Abba yayi, saida duk suka zazzauna sannan Abba ya soma ba Areefah labarin duk abinda ya faru da kuma abinda ya faru sanda aka kamasa. Batayi wani mamaki bah ganin tsantsar kamar da yake da 'yan gidansu, Hamdala tayi da k'arfi har saida duka suka juya suna kallanta, ta d'aga Hannu sama tana cewa "Alhamdulillah Thank uh Allah for accepting my Prayers" Sosai ta basu mamaki, ta kalli Areef dake ta kallanta tace "Kullum ina Addu'a Allah bani wani Bro gashi ya bani" Ta nuna Areef fuska a had'e "Mugu to daga yau uh are no more my Bro" Gaba d'aya dariya sukayi banda Areef da ransa ya gama b'aci "Dama ke wake k'anwa dake, jibeki k'azama kawai" Ba shiri ta fashe da kuka "Abba kajishi koh" Ammi ta k'arbe da cewa "Kun had'u zaku fara koh, da baku tare kwana biyu har bakina yayi shiru" Abba yace "Karka sake cema Babyna k'azama, kaga nan k'azami" Jamal sai kallansu yake da sha'awa tare da farinciki. Yace "Zo kiji" Ba musu ta dawo kusa dashi ta zauna, ya goge mata hawayen fuskanta yana murmushi "I'm now ur Bro ki kyalle Areef babu ruwanmu dashi" Gwalo tama Areef ya mik'e "Allah kikayi wasa saina mangareki" "Iyeh!" Cewar Abba "Tho Mangaretan" Ya fita daga falon yana huci, Jamal yace "He's ur brother ki daina masa rashin kunya kinji" Ta tura baki tana shagwab'a "To bashi ke tsokanata bah" Yanda take shagwab'a ta tuna masa da Wife d'insa "How old are you?" "17yrs" tace Jamal yayi dariya "Woaw! Ashe big gal ce" Tayi dariya tana cewa "Bro su waye wanda na gani a wanchan side d'in" Murmushi yayi batare da ya bata amsa bah, Ammi tace "Matansa ne" Baki bud'e tace "Duka biyu" Ya sake sakin murmushi, tab'e baki tayi tace "Nidai Faran tafi kirki, b'akan batada kirki bab...." Ammi tayi saurin cewa "Kull! Karna sake ji" Ta tura baki, Jamal ya mik'e yana cewa "Abba barinje naga Mifzal coz gobe za'a koma court" Abba yace "Eh yakamata, muma ana fitowa daga Court d'in zamu koma" Gabansa ya fad'i baice komai bah ya fita daga falon. Bai samu shiga side d'inshi bah ya wuce station d'in. A office d'in ya had'u da Ram, bayan su gaisa Mifzal yace "Komai dai zaizo k'arshe gobe insha Allahu" Jamal yayi murmushi yace "Pls ko zan iya ganin su Mamin" Dogon tsaki Ram ya saki "Wani me matar nan ta maka neh kabi ka damu da ita haka?" "Ko ba komai ta raine ni ta rik'eni kamar d'anta" Mifzal yayi saurin cewa "Anma ba tsakani da Allah bah koh" Ram ya d'aura da cewa "Wadda ta iya sa a kashe mijinta, kai ko ba mijinta ba ma mutum fah" Ran Jamal idan yayi dubu ya b'aci, ya mik'e yace "Banasan cin fuska idan bazaku taimaka min ba ku bari" Fuuu zai bar office d'in Ram yayi

Table of Contents

Chapters

82 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82