Chapter 23
Chapter 23
ba ta sauko ta fita haraban gidan, nan ma ba kowa ta dawo, harta gota d'akin Ummy sai ta juyo muryan mutane a d'akin, a hankali ta dawo ta murd'a kofan. Jamal ta gani da Twins da Ummy sunata hira. Tsawa ta dakama Twins suka fito daga d'akin dasauri, ta hararai Jamal tace "Ka fito inasan ganinka" Tana tafe yana binta a baya har d'akinta, gefen gado ta zauna shi kuma yaja stool ya zauna "Jamal wannan shine zai zama magana ta k'arshe da zan maka akan yarinyan nan Ummy, wallahi ka fita idona na rufe" Ya duk'ar dakai k'asa "Wai mai kakeso ka zama ne Jamal, baso d'aya ba baso biyu ba na fad'ama banasan ganinka da yarinyan nan" "Mami kiyi hak'uri" "Duk ba wannan ba, ya maganan da mukayi dakai na Mabrookah" Dam! Gabansa ya fad'i "Mami pls kiyi hak'uri, wallahi i have no feelings for her" Da Mamaki tace "Me kake nufi knan" Ya sake duk'ar dakai "Yanzu Jamal bazaka iya cikama yayata burinta ba, yarta d'aya Mabrookah, batada burin daya wuce taga tayi aure." Ta turo baki yana jujuya kai "Alhaji zai kiraku ya tambayeku idan kunasan juna, inaso ka amsa kana santa. Hakan ne kad'ai xai sani farinciki" Ya gyad'a kai yace "To shikenan Mami" Tayi murmushi tace "Allah ya maka albarka" Ya mik'e yabar d'akin yana gungunai. Bacci ne ya gagari idon Jamal, shi gaskiya harga Allah bazai Iya auren Mabrookah ba dan baya santa. Wuraren sha biyu ya mik'e kamar wanda aka tsikara ya sauko k'asa, d'akin Ummy yayi knocking a hankali ya shiga, dan yau so yake ayita ta k'are. Ummy Abduol✍🏻 [3/12, 8:41 PM] +234 703 981 8283: ♠♠♠♠♠♠♠♠ ♠♠♠♠ *JAMALUDEEN* ♠♠♠♠ ♠♠♠♠♠♠♠♠ By *Ummy Abduol* Dedicated to My *Late Siblings* Page 27 D'akin Ummy yayi knocking a hankali ya shiga, dan yau so yake ayita ta k'are. Tsaye ya sameta kan sallaya tana sallah, gefen gadon ya zauna yana kallan yanda take ganawa da ubangijinta cikin natsuwa. Ji yayi ta k'ara birgeshi, ya sauke ajiyar zuciya yana cigaba da kallanta. Tana idarwa ko addu'a bata tsaya yi ba ta juyo dasauri tana kallansa da mamaki "Lapia Ya Jamal meya kawoka d'akina da daran nan" "Nazo ne muyi wani magana" "Magana? Ka bari mana sai gobe yanzu dare yayi" Baice komai ba ya mik'e ya k'araso inda take zaune shima ya zauna yana cigaba da kallanta "Bazan iya hak'uri har sai gobe bah, maganar nada mahimmanci sosai" Ta gyara zama tana facing d'inshi "Ina jinka, saidai kayi sauri saboda dare kuma ina sallah neh" Ya sauke dogon ajiyar zuciya yana kallanta "Nayi tunanin na b'oye abinda ke raina game dake, wani abu yana neman yazo min wanda bana so" Kurrri Ummyn tayi tana kallanshi, dan sam bata san inda maganar tasa ta dosa bah. "Ina sanki Ummy, wallahi i so much love uh" Ba shiri ta mik'e a zabure tana kallansa da mamaki "Ki yarda ki aureni banasan Mabrookah, na miki alkawarin zan miki duk abinda kikeso pls" Hawaye suka soma gangaro mata a fuska tana girgiza kao tana kallanshi "So kuma? Haba Ya Jamal, dan Allah ka daina wannan wasan" Ya mik'e tsaye "Tun ranar dana fara ganinki naji ina sanki, ina sanki badan komai naki ba, komae.... "Ya isa! Ya isa!! Banaso inji" Hannayenta biyu tasa ta toshe kunnuwanta tana kuka sosai "Abinda yasa kenan kaje ka gyara mana gida, ka siyan mana kayan alatu dan ka siya iyayena...." "No! Ummy ki fahimceni, wallahi ko kad'an badan wani abu nayi haka...." Tayi saurin katseshi cikin muryan kuka "Ka makara, inada wanda nakeso, koda banida shi bazan tab'a sanka bah Ya Jamal. Tun bayan warkewanka nake cikin k'unci da hantara a gidan nan. Talauci bah hauka baneh, indai haka ake k'udi kada Allah ya bani" "No pls Ummy, ki tsaya ki saurareni" Cikin d'aga murya tace "Bazan ji bah, Ya Jamal ka fitar min daga d'aki banasan ji! Ka fita" Kallo ya bita dashi cikin tashin hankali ya fita ya haura zuwa d'akinsa. Ranar daga Ummy har Jamal babu wanda ya runtsa. Washe gari yana kan dinning yana breakfast tazo ta wuce idanunta a kukumbure, hakan ya tabbatar masa da cewa tayi kuka daran jiya. Wani tausayinta neh ya k'ara shiga ranshi, harga Allah yanasan Ummy, so na tsakani da Allah. Dan shi a shirye yake dayayi komai a kanta. Kamar wanda aka tsikara ya mik'e dasauri ya nufi side d'in Abba, saidai kash yana zuwa ya samu Mami a falon, k'eya ya sosa ya juya Abba yace "Yaya dai Jamal, akwai wani abu neh?" Yayi saurin cewa "Aa ba komai" Da sauri ya fita daga falon ya shiga motarshi yabar gidan. Saida Abba ya fita dan ranar zaiyi tafiya, sannan Mami ta fito daga side d'in ta dawo nata, Mabrookah ce ta soma saukowa tana murmushi "Mami dan Allah kiban kud'in, yau nakeso muje nida k'awayena mu fitar da ankon" Sosai maganan Mabrookah yaba Mami dariya, saida tayi mai isarta sannan tace "Mabrookah kenan! Ke kin tab'a ganin inda aka fitar da anko ba'a sa rana bah" Baki ta turo gaba "Mami ai ba sai ansaka rana bah, already Abba ya bashi ni, haka an bani shi. Kuma Mommy ce tace na fitar yanzu" Kai Mami ta girgiza zata haura ta d'auko handbag d'inta ta fita aiki. Ranar sukuku Ummy ta wuni, har lokacin maganan Jamal ne a ranta, harga Allah bazata iya san Ya Jamal ba dan har yanzu bata gasgata maganan rasuwan Bilal bah, har lokacin tana nan rik'e da alkawarin data masa na bazata tab'a auren kowa ba sa shi. ***** Wuraren k'arfe tara da rabi, Ummy na d'aki tana sallan isha'i dan tayi lattin sallan saboda aikin da Aunty Faty keta sata. Muryan Aunty Faty ta jiyo tana salati tana cewa "Maimuna! Maimunatu!! Ina kike an sace min sark'a" Mami dake falon k'asa itada Mabrookah sukayi saurin mik'ewa "Sark'a kuma? Wane irin sark'a" Cewar Mami "Sark'an nan dana siya mana danaje Dubai, Million d'aya da dubu d'ari shidda shi na nema ban gani bah" "Toooh!" Cewar Mabrookah tana rik'e da hab'a Mami tace "Aa bafa zai tab'a yuwuwa bah, dan gidan nan ba'a sata. Yaya Faty kidai k'ara dubawa" "Bafa inda ban duba ba, sark'an nan d'auka akayi" "Mudai je mu sake dubawa" Duka suka haura sama zuwa d'akin Aunty Fatyn, batsa batsa sukayi da d'akin suna nema anma bah sarka. Mabrookah ta rik'e k'ugu tana bin d'akin da kallo "Gaskiya abin nan da mamaki yake, kuma nasan dai masu aiki basa haurowa nan saman" Aunty Faty tai saurin cewa "Saidai Ummy ai ita ke shigowa tana gyare gyare, dan babu wanda zai d'au sark'an nan saboda ke Maimuna da Mabrookah kunfi k'arfin wannan" "Aa Yaya Faty, bana tunanin Ummy zata d'au sark'an nan. Dan duk abin yarinyan nan bata sata" "Maimuna! Lallai baki san talaka ba har yanzu, nidai gaskiya bazan yarda. Million d'aya harda dubu d'ari shidda ba k'aramin kud'i baneh. Gaskiya ban yarda ba sai anyi chaje kuma masu aikin nan za'a duba" Mabrookah tai saurin cewa "Gaskiya ne Mommy, dan tunda nazo gidan nan ba'a tab'a sata ba sai yau" Itadai Mami batace komai bah, Aunty Faty da Mabrookah suka sauko k'asa zuwa d'akin Ummy, ganin Haka yasa Mami ta biyosu
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82