Skip to content

Chapter 76

Chapter 76

Jamaluddeen Book One Complete Hausa Novels 1,202 words 0 views Progress saved
Download Book

baice komai saboda b'acin rai, ji yake kamar ya kashe Mabrookah ya huta, hannayensa ya saka a aljihu tare da sakin huci mai zafi. Areefah ta zumb'uro baki "Ai wallahi bazan yarda bah, wallahi ta k'ara maimaita makamancin haka dukan tsiya zan mata" Ran Abba ya b'aci, ya daka ma Areefah tsawa abinda bai tab'a yi bah "Karna k'ara ji" Ta sake shagwab'e fuska ta kauda kai. Suna nan har ta farka daga baccin, sunata mata sannu har abin ya bata kunya ganin harda Abba a wajan da kuma yanda gaba d'aya suka nuna damuwarsu a kanta. Ba kunya Jamal ya zauna kusa da ita ya d'an rab'ata da jikinsa sai k'okarin k'wacewa take ta kasa, shiko gogan ko a jikinsa. Ammi na ganin haka ta mik'e daga kan kujeran datake, "To bari muje gida mudai" Ummy najin haka ta tura baki tana kallan Jamal "Nifa ba inda kemin ciwo dan Allah a sallameni" Bai iya mata musu ba ya mik'e yace ma su Ammi yana zuwa, wajan likitan yaje ya rok'esa ya sallamesu, X-ray aka rubuta musu da kuwa wasu magunguna sannan yace su bari drip d'in dake jikinta ya k'are. Godiya yayi ya koma, yana zuwa ya samu su Ammi sun wuce sai Areefah dake d'akin tanata ma Ummyn hira itako sai dariya take cike da nishad'i, Yanda ta damu da Wife d'insa yasa ta sake samun gurbi a zuciyarsa, ya k'araso ya shaida musu yanda sukayi da likitan. A b'angaren Mabrookah kuwa tana ganin su Ammi sun fita ta fashe da wani matsanancin kuka, sai lokacin kalmar Jamal dayake anbata mata kalmar saki ya dawo mata k'wakwalwarta. Ta sake rushewa da kuka, chan kuma ta mik'e kamar wacce aka tsikara, ta goge hawayenta ta nufi bedroom d'inta dasauri. Drip d'in na k'arewa aka sallamesu suka dawo gida, Ammi dake falon tana jiransu tana jin shigowan motan ta fito dasauri ta rungume Ummyn tana mata sannu, Hannunta ta kama tana cewa "Banasan wani tashin tashina, zo muje d'akina" Jamal ya turo baki gama harda doka k'afa d'aya a k'asa sam ba haka yaso bah, Areefah dake kallansa ta kyalkkyale da dariya ya galla mata harara, ciki sukayi yana binsu a baya har lokacin bai maida bakin bah. Ganin sun haura sama yasa ya zauna a falo yana cika yana batsewa, Kan gado Ammi ta zaunar da ita tana cigaba da mata sannu "Kiyi Hak'uri Jaleelah kinji" Murmushi kawai tayi ta duk'ar dakai k'asa, Ammi ta shiga toilet ta had'a mata ruwa mai d'an zafi ta umarceta taje tayi wanka. Cikin daran nan nan nan da Ummyn Ammi ta dunga yi sai dataga tayi bacci hankalinta ya kwanta. Tana saukowa ta samu Jamal kwance kan 2seater bacci ya d'aukesa, murmushi tayi ta k'arasa ta tab'asa tana cewa "Jamaludeen a nan kake bacci, maza tashi kaje ka kwanta" Ya bud'e ido dakyar "Ammi ina Wife" Duka ta d'aka masa ya bud'e ido dakyau yana muzurai "Maza je ka kwanta, karna dawo na sameka a nan" Ta haura sama ta barshi nan. Da Asubah Abba ya sauko dan tashin Areef zuwa masallaci, a d'akin ya samu Jamal kwance kan Tiles yana bacci abinsa hankali kwance, Mamaki ne k'arara a fuskanshi ya k'arasa ya soma tashinsu, Areef ma yayi mamakin Ganin Jamal d'in a d'akin. Tare suka tafi masallacin su uku. K'arfe takwas na safe duk sun hallara a falon before ayi breakfast, Ummy na zaune k'asa kan carpet kusada k'afar Ammi itada Areefah, Haka Jamal shima zaune kusada Abba, Abba yayi gyaran murya ya soma da cewa "Wannan zaman yakamata ayishi da d'ayar matarka, saidai kafin tazo inaso nayi magana akan abinda ya faru Jiya" Jamal ya duk'ar dakai dan yasan dashi za'ayi, Abba ya juya garesa fusaka ba yabo ba fallasa yace "Da Mabrookah da Jaleelah duk matanka neh, duk sadaki ka biya ka aurosu koh?" Jamal dake gefe ya gyad'a kai kamar kad'angare kansa k'asa "Sam banji dad'in abinda ya faru bah jiya, idan rai ya b'aci bai kamata hankali ya gushe bah. Yakamata ka tsaya kayi alk'alanci kafin ka zartar da hukunci. Anma zartar da hukunci cikin fushi babu abinda yake haifarwa sai danasani" Ya numfasa yace "Baka kyauta ba sam Jamaludeen" Ammi dake gefe tace "Saki nawa ka mata?" Kansa k'asa yace "Biyu!" "What!" Cewar Abba ransa a b'ace "A haka kakesan mu zauna a nan gidan" Ya d'ago idanunsa cike da kwalla yace "Abba dan Allah kayi hak'uri!" Abba ya sauke ajiyar zuciya yace "Areefah jeki kiramin Mabrookahn" Ta mik'e tana zunguro baki ta fita, Side din ta shiga ga mamakinta yanda falon yake jiya haka ta samesa, ta tab'e baki "Sai shegen k'azanta" Knocking ta soma a k'ofar bedroom d'in shiru ba amsa tafi minti goma a tsaye taja tsaki ta banko k'ofan ta shiga. Batsa batsa ta samu d'akin kayan wardrobe duk a k'asa da sauran tarkace. Ta taka tana yatsine fuska har Toilet d'in nan ma ta dunga bugawa ba amsa. Har zata fito idanunta suka sauka kan wani Farin takarda mai d'auke da rubutu da aka d'aurama Kwalbar humra. D'auka tayi ta soma karantawa _Kayi ma iyayena k'azafi hankalinka bai kwanta bah, ka..._ Tayi saurin dakatar da karatun ta fita dasauri zuwa d'ayan side d'in. Tana shiga tace "Abba ban ganta ba saidai naga wannan takardan" Ta mik'a masa ya duka na 'yan mintina sannan ya mik'ama Areef yace ya karanta kowa yaji _Kayi ma iyayena k'azafi Hankalinka bai kwanta bah, ka d'auko wasu mutane dan suci dukiyar Abba wai kai Iyayenka, to ka sani alhakin Iyayena bazai tab'a barinka bah. Sannan indai Ummy ce wallahi baku isa ku zauna lafiya bah, badai saboda ita ka sakeni bah? To wallahi baku ba samun Farinciki indai ina raye. Na tafi na bar muku waje ku shak'ata saidai ku jirayi dawowata.A_ Daga Matarka abar sonka Mabrookah. Areef na gama karantawa yaja dogon tsaki "Abba kagani koh? Ni dama wallahi tunda na ganta sam batamin bah" Kasa cewa komai Abba yayi Ammi tace "Areefa kuje keda Ummy sama kuyi breakfast sannan kuyi sauri dan 10 za'a shiga Court gashi 9 yanzu" Ta kama hannun Ummyn suka haura sama zuwa d'akin Ammin, suna shiga Ummy ta zauna bakin gado ta fashe da kuka, Areefah ta zauna kusada ita dasauri tare da dafa kafad'arta "Haba Aunty Ummy ki daina kuka, insha Allahu babu abinda Mabrookah ta isa ta miki wanda Allah bai miki bah" Ta saki murmushin takaici "Nasan Halin Mabrookah sarai akan abinda takeso tana iya komai Areefah" Areefah ta soma share mata hawaye "Oh! Stop crying Allah ya fita" Bata sake cewa komai ba sai kukan data cigaba, Breakfast d'insu Areefah ta d'auko musu, ba yanda batayi akan Ummyn taci ba taki, saima kwanciya datayi wani mugun zazzab'i ja neman rufeta. A falo kuwa su Areefah na haurawa Ammi tace "Gaskiya Alhaji inasan rayuwar d'ana dana matarsa. Banasan abinda zai tab'asu, cikin biyu gaskiya za'a zabi d'aya ko mu zauna dasu ko mu koma gaba d'aya abujan tare" Jamal ya karb'e da cewa "Abba Ammi dan Allah ku gafarceni ku yafemin abinda na muku". Abba yace "Babu komai anma kada hakan ta k'ara faruwa" Shiru ne ya biyo baya, Ammi ta sake cewa "Alhaji bakace komai bah har yanzu" "Ammi dama inso idan kun amince

Table of Contents

Chapters

82 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82