Skip to content

Chapter 37

Chapter 37

Jamaluddeen Book One Complete Hausa Novels 1,199 words 0 views Progress saved
Download Book

fiyeda sau uku. Fizgewa tayi da k'arfi ta mik'e tana goge hawayen dake fuskanta tana turo baki. Murmushi ya mata ya shafa cikinsa "Yunwa nakeji sosai Wife" Ta turo baki tana kauda kai "Yana dinning" Ya mik'e yana k'okarin k'arasowa inda take, ta matsa dasauri tana masa dariya had'e da turo baki. K'wafa yayi ya shafa gefen fuskanta "Barinyi wanka ina zuwa" Ya fita zuwa d'akinsa dan yin wanka. Mabrookah kuwa dakyar ta tashi a wajan tana kuka sosai, side d'in Abba ta shiga dan tasan by now Mami na chan. A bakin k'ofa sukayi kicibus da Abba yana sauri zaije masallaci, k'asa ta zube gabansa ta fashe da kuka "Mabrookah mai kuma ya faru" Mami dake cikin falon ta fito dasauri tana tambayan lafiya "Ya Jamal ne ya dukeni kawai dan naje wajansa na samesa da Ummy" Ran Mami idan yayi dubu ya b'aci "Alhaji kaga abinda nake fad'a maka koh, gaba d'aya yarinyan nan tanaso ta d'auke mana hankalin Jamal, gashi tun ba'aje ko inaba har an fara duka" Saida yayi Jim sannan yace "Bari na dawo masallaci" Mami taja Hannun Mabrookah suka shiga ciki. Waya ta d'auka ta soma neman layinshi anma bai d'auka bah. Shiko gogan, wanka ya fesa ya saka bak'in singlet da 3quarter irin na sojoji, D'akin Ummy ya nufa sukayi kicibus a bakin k'ofa tana k'okarin fitowa, hannunta yaja har zuwa dinning d'in yaja kujera ya zaunar da ita sannan shima yaja ya zauna. Sunkuyar dakai tayi k'asa tana wasa da zoben hannunta "Banasan kunyan nan Wife, ki saki jikinki" Ta mik'e ta bud'e kullan ta d'au leda d'aya ta saka masa a plate sannan ta bud'e na miyan shima ta zuba. Tunda ta bud'e kulan tuwon ya turo baki gaba har ta jere masa komai a gabansa, ya shagwab'e fuska yace "Nidai gaskiya Wife banacin tuwo" "Saboda meh?" Ya sake tura baki yace "Ni banacin tuwo haka nake" Kurrri tamasa ko k'iftawa batayi, shiko ya tura mata abincin ya rungume hannu kamar k'aramin yaro "Kafa ce yunwa kakeji" Ya d'anyi murmushin mugunta yace "Saidai idan kin yarda zaki bani a baki, to zan daure naci" Ta zaro ido baki na rawa "Aaaa..A baki? Uhummm" "Oh bazaki bani bah" Tayi shiru ta gaza ce masa komai. Ya saci kallanta ya rik'e cikinsa "Ouch! Ni yunwa nakeji" "Pls ki bani naci" Yanda yayi maganan a shagwab'e sai ya bata tausayi, anma ita harga Allah bata tunanin zata iya basa abinci a baki. Shiru ba wanda ya sake magana ya mik'e yana rik'e da cikinsa zai bar wajan "Dan Allah kai hak'uri to zauna na baka" Har a ransa yaji dad'i anma yad'an basar yace "Nidai kawai ki bashi tunda bazaki bani bah" Ta langwabar dakai idonta cike da kwalla, sai a lokacin ya lura da fuskanta inda Mabrookah ta mareta har yad'an tashi. Wani takaici yaji a zuciyarshi, shi bada dan Mami ta matsa ba mai zai kaishi auran Mabrookah. Wajan ya shafa "I'm sorry nasan laifina neh, saboda ban gyara gidana bah har hakan ta faru" Ta girgiza masa kai a hankali, kan kujeran ya koma ya zauna. Nan suka shiga daru wajan cin abincin, dakyar ta yarda ta basa haka shima ya ciyar da ita gwanin sha'awa. A tare sukayi sallan isha'i, tambayoyi ya mata na karatun da Lesson teachern ta na d'azu ya koya mata ta basa amsa har yana mamaki. Bayan sun gama ya d'au basket d'inda Tasa Abincin Abba a ciki tana binshi a baya zuwa side d'in Abban. A nan falonsa ya had'u da Mami da Mabrookahn suna zaune, shi sai yanzu yama tuna abinda ya faru tsakaninsu d'azu. Mami ko sai galla ma Ummy harara take har suka k'araso suka zauna, cikin girmamawa Ummy ta gaida Mamin, ta kauda kai gefe tak'i amsawa. Ana cikin haka Abba ya shigo falon, Ummy da Jamal suka gaida shi cikin fara'a ya amsa tareda k'arasowa ya zauna. Basket d'in Jamal ya tura masa yace "Abba gashi inji Ummy" Da fara'a yace "Ah to madallah, Allah ya saka" "Haba Alhaji, kazo kayi shiru bakace komai bah. Duka fa Jamal ya mata akan wannan" Ta nuna Ummy dake zaune k'asa kamar marainiya "Ka kyauta Jamal, ai gwara daka nuna yanzu na gani tun kamin ku je naku gidan" "Komai binsa ake a hankali, shi yakamata ki tambaya kiji mai ya had'asu" "Ga Algunguman data had'asu nan. Wallahi kinyi kad'an ki wargaza min 'yayana" "Maimuna kimin shiru, banasan na k'ara jin bakinki a nan" Mami ta turo baki tareda kauda kai "Jamal meya faru tsakanin ka da Mabrookah" Nan ya kwace duk abinda ya faru ta fad'ama Abban, Abba ya juya ga Mabrookah yace "Haka akayi ko ba haka akayi bah" Baki ta zunguro gaba tace "Hakaneh" Nan Abba ya bata rashin gaskiya, had'asu duka su ukun yayi ya musu nasiha, Mami dake gefe tace "Fad'a Alhaji yakamata kama Jamal, dan Wallahi yana tauye yarinyan nan, kwata kwata baya shiga d'akinta, baya shiga harkanta. Duk kuma saboda Wannan muguwar yarinyar" Kuka Ummy keyi mara sauti, duk hankalin Jamal na kanta ganin tana kuka. Abba ya b'ata rai yace "Ku tashi kuje" Hannun Ummy ya kama ya jata suka bar falon dasauri, Mami ko fad'i take "Kagani ko Alhaji, ga 'yar uwarsa baiko kalleta ba ya kama waccan sun wuce. Gaskiya dole na tashi tsaye dan da alama shanye min shi akayi" Rai b'ace Abba ya kalli Mabrookah "Tashi ki koma d'akinki" Ba musu ta mik'e ta fita. Ya juyo zuwaga Mami kacha kacha ya mata ya mik'e ya haura d'akinsa dan ta soma kaisa bango. Ummy Abduol✍🏻 [3/22, 5:21 AM] 0mmer Farouk: ♠♠♠♠♠♠♠♠ ♠♠♠♠ *JAMALUDEEN* ♠♠♠♠ ♠♠♠♠♠♠♠♠ By *Ummy Abduol* Dedicated to My *Late Siblings* Page 41 Kuka Mabrookah ta fashe dashi mara sauti wacce ke tsaye bakin k'ofar d'akin tana lek'en su ta ramin makulli tana kallo da kuma sauraran abin da ke faruwa, Dasauri ta sauka k'asa zuwa d'akinta ta sake rushewa da kuka. Jamal kuwa rungumo Ummy ya sakeyi yana jin wani farinciki na ratsa sa, bakinsa yakai saitin kunnenta ya rad'a mata "Ke nake saurare wife, fad'amin me kikeso" Tayi saurin girgiza kai a kunyace saboda yanda ya rungumota har numfashin su na had'uwa. Batayi aune ba ya d'auketa chak ya direta kan fado yana murmushi, ganin haka yasa ta mik'e a tsorace tana zaro ido kamar tayi k'arya. Murmushi yayi ya hayo kan gadon yana kallanta, matsawa tayi dasauri tana cigaba da kwalalo ido. Ya kamo hannunta ya had'a da nashi yana murzawa a hankali "I love uh so much Wife, da ban aureki ba bansan ya zanyi bah" Ta rausayar da kai k'asa tana 'yar murmushi tareda lumshe idonta alamar bacci. "Ya Jamal baccciiii.." Ta fad'a a hankali da sanyaiyar muryanta, ya shafa gefen kumatun ta da murmushi "Na lura ke ragguwa ce, nida kwanan nan nakeso naga kin fara tafiya da k'yar" Ba shiri ta bud'e idanunta a tsorace tana kallansa, dariya ya soma mata ganin yanda ta tsorata lokaci guda "Ni dai dan Allah ka fita bacci nakeji" Yanda tayi maganar a shagwab'e sosai ya burgeshi ya d'an rungumota jikinsa ya rad'a mata "Wife bakya san mu kwana tare" Kai ta girgiza alamar eh idanunta lumshe sboda kunyarsa. Peck ya mata a kumatu da goshi

Table of Contents

Chapters

82 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82