Chapter 37
Chapter 37
fiyeda sau uku. Fizgewa tayi da k'arfi ta mik'e tana goge hawayen dake fuskanta tana turo baki. Murmushi ya mata ya shafa cikinsa "Yunwa nakeji sosai Wife" Ta turo baki tana kauda kai "Yana dinning" Ya mik'e yana k'okarin k'arasowa inda take, ta matsa dasauri tana masa dariya had'e da turo baki. K'wafa yayi ya shafa gefen fuskanta "Barinyi wanka ina zuwa" Ya fita zuwa d'akinsa dan yin wanka. Mabrookah kuwa dakyar ta tashi a wajan tana kuka sosai, side d'in Abba ta shiga dan tasan by now Mami na chan. A bakin k'ofa sukayi kicibus da Abba yana sauri zaije masallaci, k'asa ta zube gabansa ta fashe da kuka "Mabrookah mai kuma ya faru" Mami dake cikin falon ta fito dasauri tana tambayan lafiya "Ya Jamal ne ya dukeni kawai dan naje wajansa na samesa da Ummy" Ran Mami idan yayi dubu ya b'aci "Alhaji kaga abinda nake fad'a maka koh, gaba d'aya yarinyan nan tanaso ta d'auke mana hankalin Jamal, gashi tun ba'aje ko inaba har an fara duka" Saida yayi Jim sannan yace "Bari na dawo masallaci" Mami taja Hannun Mabrookah suka shiga ciki. Waya ta d'auka ta soma neman layinshi anma bai d'auka bah. Shiko gogan, wanka ya fesa ya saka bak'in singlet da 3quarter irin na sojoji, D'akin Ummy ya nufa sukayi kicibus a bakin k'ofa tana k'okarin fitowa, hannunta yaja har zuwa dinning d'in yaja kujera ya zaunar da ita sannan shima yaja ya zauna. Sunkuyar dakai tayi k'asa tana wasa da zoben hannunta "Banasan kunyan nan Wife, ki saki jikinki" Ta mik'e ta bud'e kullan ta d'au leda d'aya ta saka masa a plate sannan ta bud'e na miyan shima ta zuba. Tunda ta bud'e kulan tuwon ya turo baki gaba har ta jere masa komai a gabansa, ya shagwab'e fuska yace "Nidai gaskiya Wife banacin tuwo" "Saboda meh?" Ya sake tura baki yace "Ni banacin tuwo haka nake" Kurrri tamasa ko k'iftawa batayi, shiko ya tura mata abincin ya rungume hannu kamar k'aramin yaro "Kafa ce yunwa kakeji" Ya d'anyi murmushin mugunta yace "Saidai idan kin yarda zaki bani a baki, to zan daure naci" Ta zaro ido baki na rawa "Aaaa..A baki? Uhummm" "Oh bazaki bani bah" Tayi shiru ta gaza ce masa komai. Ya saci kallanta ya rik'e cikinsa "Ouch! Ni yunwa nakeji" "Pls ki bani naci" Yanda yayi maganan a shagwab'e sai ya bata tausayi, anma ita harga Allah bata tunanin zata iya basa abinci a baki. Shiru ba wanda ya sake magana ya mik'e yana rik'e da cikinsa zai bar wajan "Dan Allah kai hak'uri to zauna na baka" Har a ransa yaji dad'i anma yad'an basar yace "Nidai kawai ki bashi tunda bazaki bani bah" Ta langwabar dakai idonta cike da kwalla, sai a lokacin ya lura da fuskanta inda Mabrookah ta mareta har yad'an tashi. Wani takaici yaji a zuciyarshi, shi bada dan Mami ta matsa ba mai zai kaishi auran Mabrookah. Wajan ya shafa "I'm sorry nasan laifina neh, saboda ban gyara gidana bah har hakan ta faru" Ta girgiza masa kai a hankali, kan kujeran ya koma ya zauna. Nan suka shiga daru wajan cin abincin, dakyar ta yarda ta basa haka shima ya ciyar da ita gwanin sha'awa. A tare sukayi sallan isha'i, tambayoyi ya mata na karatun da Lesson teachern ta na d'azu ya koya mata ta basa amsa har yana mamaki. Bayan sun gama ya d'au basket d'inda Tasa Abincin Abba a ciki tana binshi a baya zuwa side d'in Abban. A nan falonsa ya had'u da Mami da Mabrookahn suna zaune, shi sai yanzu yama tuna abinda ya faru tsakaninsu d'azu. Mami ko sai galla ma Ummy harara take har suka k'araso suka zauna, cikin girmamawa Ummy ta gaida Mamin, ta kauda kai gefe tak'i amsawa. Ana cikin haka Abba ya shigo falon, Ummy da Jamal suka gaida shi cikin fara'a ya amsa tareda k'arasowa ya zauna. Basket d'in Jamal ya tura masa yace "Abba gashi inji Ummy" Da fara'a yace "Ah to madallah, Allah ya saka" "Haba Alhaji, kazo kayi shiru bakace komai bah. Duka fa Jamal ya mata akan wannan" Ta nuna Ummy dake zaune k'asa kamar marainiya "Ka kyauta Jamal, ai gwara daka nuna yanzu na gani tun kamin ku je naku gidan" "Komai binsa ake a hankali, shi yakamata ki tambaya kiji mai ya had'asu" "Ga Algunguman data had'asu nan. Wallahi kinyi kad'an ki wargaza min 'yayana" "Maimuna kimin shiru, banasan na k'ara jin bakinki a nan" Mami ta turo baki tareda kauda kai "Jamal meya faru tsakanin ka da Mabrookah" Nan ya kwace duk abinda ya faru ta fad'ama Abban, Abba ya juya ga Mabrookah yace "Haka akayi ko ba haka akayi bah" Baki ta zunguro gaba tace "Hakaneh" Nan Abba ya bata rashin gaskiya, had'asu duka su ukun yayi ya musu nasiha, Mami dake gefe tace "Fad'a Alhaji yakamata kama Jamal, dan Wallahi yana tauye yarinyan nan, kwata kwata baya shiga d'akinta, baya shiga harkanta. Duk kuma saboda Wannan muguwar yarinyar" Kuka Ummy keyi mara sauti, duk hankalin Jamal na kanta ganin tana kuka. Abba ya b'ata rai yace "Ku tashi kuje" Hannun Ummy ya kama ya jata suka bar falon dasauri, Mami ko fad'i take "Kagani ko Alhaji, ga 'yar uwarsa baiko kalleta ba ya kama waccan sun wuce. Gaskiya dole na tashi tsaye dan da alama shanye min shi akayi" Rai b'ace Abba ya kalli Mabrookah "Tashi ki koma d'akinki" Ba musu ta mik'e ta fita. Ya juyo zuwaga Mami kacha kacha ya mata ya mik'e ya haura d'akinsa dan ta soma kaisa bango. Ummy Abduol✍🏻 [3/22, 5:21 AM] 0mmer Farouk: ♠♠♠♠♠♠♠♠ ♠♠♠♠ *JAMALUDEEN* ♠♠♠♠ ♠♠♠♠♠♠♠♠ By *Ummy Abduol* Dedicated to My *Late Siblings* Page 41 Kuka Mabrookah ta fashe dashi mara sauti wacce ke tsaye bakin k'ofar d'akin tana lek'en su ta ramin makulli tana kallo da kuma sauraran abin da ke faruwa, Dasauri ta sauka k'asa zuwa d'akinta ta sake rushewa da kuka. Jamal kuwa rungumo Ummy ya sakeyi yana jin wani farinciki na ratsa sa, bakinsa yakai saitin kunnenta ya rad'a mata "Ke nake saurare wife, fad'amin me kikeso" Tayi saurin girgiza kai a kunyace saboda yanda ya rungumota har numfashin su na had'uwa. Batayi aune ba ya d'auketa chak ya direta kan fado yana murmushi, ganin haka yasa ta mik'e a tsorace tana zaro ido kamar tayi k'arya. Murmushi yayi ya hayo kan gadon yana kallanta, matsawa tayi dasauri tana cigaba da kwalalo ido. Ya kamo hannunta ya had'a da nashi yana murzawa a hankali "I love uh so much Wife, da ban aureki ba bansan ya zanyi bah" Ta rausayar da kai k'asa tana 'yar murmushi tareda lumshe idonta alamar bacci. "Ya Jamal baccciiii.." Ta fad'a a hankali da sanyaiyar muryanta, ya shafa gefen kumatun ta da murmushi "Na lura ke ragguwa ce, nida kwanan nan nakeso naga kin fara tafiya da k'yar" Ba shiri ta bud'e idanunta a tsorace tana kallansa, dariya ya soma mata ganin yanda ta tsorata lokaci guda "Ni dai dan Allah ka fita bacci nakeji" Yanda tayi maganar a shagwab'e sosai ya burgeshi ya d'an rungumota jikinsa ya rad'a mata "Wife bakya san mu kwana tare" Kai ta girgiza alamar eh idanunta lumshe sboda kunyarsa. Peck ya mata a kumatu da goshi
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82