Skip to content

Chapter 32

Chapter 32

Jamaluddeen Book One Complete Hausa Novels 1,200 words 0 views Progress saved
Download Book

Mifzal ne zai d'aukemu ita kuma kai da kanka zaka je ka d'auketa" Juyowa yayi ya watsa mata mummunan kallo "Saboda ita Matata ce, hakk'inta tun sati hud'u da suka wuce ya dawo wuyana" "Wannan ai ba adalci bah, kamar yanda take matarka haka nima nake matarka" Ya tako zuwa gabanta yana cigaba da kallanta "Har yau ke ba matata bace, saboda ba'a daura bah. Idan kuma na k'arajin wani magana sai na fasa auren muga tsiya" Ya nuna mata k'ofa "Fitar min daga d'aki" Fuuuuu tabar d'akin rai b'ace kamar ta fashe da kuka. Wayansa dake kan bedside ne ya soma ruri, ganin numbern Najma yasa ya saki murmushi ya fito ya samu abokan nasa. Shi da Ram ne suka nufi gidansu Ummy, da kuma wasu daga cikin abokansa dan d'aukan sauran k'awayen Ummyn. Mifzal kuma dasu Taseem zasu d'au Mabrookah da k'awayenta. Daidai k'ofar gidan Inna sukayi Parking, numbern Najma ya soma kira ta d'auka tana cewa "Haba Ya Jamal tun fa d'azu muke jiranku" Saida yayi dariya sannan yace ku fito muna k'ofar gida. Najma ta gyara ma Ummy head d'in kanta tareda rik'o hannunta "To ku muje suna k'ofar gida." Ummy tad'an zaro ido tana kallan Laurat tana yatsine fuska "Ni fa wallahi wannan dogon takalmin ya isheni" "Haba karki badamu mana" Cewar Najwa. Najma na rik'e da hannunta har suka fito daga gidan, sauran k'awayen na take musu baya. Ram ya fito dasauri ya bud'e mata baya inda Jamal ke ciki, ba musu ta shiga ta sadda kanta k'asa ganin Jamal a cikin motan. Laurat ce ta shiga gaba, su Najma kuma suka shiga sauran motocin suka d'au hanyan Hall d'in da za'ayi dinnern. Tunda Ummy ta shiga ba abinda Jamal keyi sai aikin kallanta yana murmushi, kunya ne ya lullub'eta ta k'ara sadda kai k'asa tana wasa da clutch d'in hannunta. Hannunta ya kamo ya had'a da nashi ya d'an matse kad'an, kokarin k'wacewa ta soma yi. Yasa d'ayan Hannunshi ya d'ago fuskanta. Dasauri ta runtse ido saboda kunyarshi da taji tana ji sosai, motsowa ya sake yi har suna gugan juna, yakai bakinsa saitin kunnenta ya rad'a mata "Kinyi kyau sosai Pearl" Ta saki d'an murmushi har lokacin idanunta a lumshe. D'agowan da zaiyi suka had'a ido da Ram dake kallansu ta mirrown gaban motan "Ka kalli gabanka dai banasan gulma" Dariya Ram kawai yayi ya cigaba da driving suna hira da Laurat. Wayan Jamal ne yayi k'ara yasa hannu ya ciro, ganin Mifzal ne yasa ya d'auka ya kara a kunne "Mifzal ya akayi" Daga chan b'angaren yace "Wai kuna ina neh, muna fa nan k'ofar hall d'in tun d'azu muna jira, ga kuma Amaryar ka nan sai masifa take dan Allah kuyi sauri" Tsaki yaja sannan yace "Ba sai taita yi bah, ko so take muyi tsintsu muzo" Ya kashe wayan tareda sassauta rik'on dayama Ummyn, tana ganin haka ta zame dasauri ta matsa gefe. Su Aunty Faty dasu Mami da Aunty Zainab da sauran 'yan uwa da abokan arziki duk suna cikin Hall d'in da za'ayi Dinnern. Jin har lokacin Jamal bai tso ba yasa Aunty Faty ta had'e rai kamar zatayi bindiga, Mami ma ranta ya b'aci sosai da jin Jamal d'in ne da kansa yaje d'auko Ummyn. Basu iso wajan ba sai k'arfe bakwai da rabi lokacin har Mabrookah dake cikin mota ta gaji da jira. Ram na parking ya fito, Laurat ma ta fito. Najma ce ta bud'e side d'in da Jamal d'in ke ciki, Taseem kuma ya bud'e na amarya. A tare suka fito, Ummy kanta a k'asa kunya sosai ya rufeta musamman ganin Flash lights d'in cameras daban daban dake ta d'aukan su hoto. Laurat tayi saurin rik'e mata hannu ta jata zuwa inda Jamal d'in ke tsaye, Mabrookah ma ta fito itada k'awayenta, A tare suka soma jerawa Ummy na'a gefen damansa, shi yana tsakiya Mabrookah na gefen hagunsa. A bayansu K'awayen Mabrookah ne da abokan Ango sai su Najwa da Laurat. Nan da nan wajan ya d'au tafi, wajan zamansu da aka tanada dominsu suka zauna. Sosai Couples d'in sukayi kyau su duka, bama kamar Jamal da Ummy duk wanda ya kallesu sai ya k'ara kallansu. 'Yan jarida da masu hoto sai d'aukansu suke, hakan ba k'aramin bak'anta ran Mabrookah yayi bah. Bayan anci ansha aka umarci Amare da ango su taso su d'an taka. Wuf Mabrookah ta mik'e Ummy ko kasa tashi, Jamal ya rik'o hannunta ya d'agata, kanta ta sauke k'asa duk jinta take a takure a wajan. Hannunta ya kama sannan ya juya ya fizgo na Mabrookah suka sauko daga step d'in dake wajan. Wak'an su Psquare bank alert ke tashi, Mabrookah ta zage sai rama take, itako Ummy tsaye ta tsaya dan ita bata iya rawa bah koma ta iya bazata iyayi a gaban mutane bah. Jamal na yana d'an rausaya wa a hankali yana bin wakan dan yana san wakan sosai. Hannun Ummy ya kamo ya matso da ita sosai kusada shi, hannayenshi biyu yasa a k'ugunta ya zagaye yana cigaba bin wak'an yana murmushi. Ba k'aramin burge mutane sukayi bah, kan kace me wajan ya cika da 'yan lik'i sai ruwan nerori ake musu. Ran Mabrookah idan yayi dubu ya b'aci, dakyar Ummyn ta iya sa hannu ta ciro kud'in daya basa ta masa lik'i saboda kunya. Sanda akazo yanka cake ma saida Mabrookah tasha haushi. Anci ansha tareda raba kyaututuka masu yawa sannan kowa ya kama gabansa. Kamar wanchan lokacin Jamal da Ram ne suka maida Ummy gida da k'awayenta. Ita kuma Mabrookah Taseem ya maida ta gida. Washe gari kuma kamu, shima Anyi shagali kamar ba gobe, anyi taro lafiya an tashi lafiya duk da su Aunty Faty ransu a b'ace yake da ganin rashin kunyan da Jamal keyi k'iri k'iri yana nuna banbanci tsakanin Ummy da Mabrookah. Bayan an dawo Kamu su Ummy suka koma gidansu dan washe gari za'a kaita. Sai a lokacin Ummyn kejin Abba yace ya d'auke musu yi mata kayan d'aki shi zai yi mata komai. Tun a ranar ta soma kukan rabuwa da Mamanta da kuma Sahibinta Bilal. A ranar sati duban jama'a suka shaida d'aurin auren Jamaludeen Surajo da Amaryar sa Mabrookah Ismail a bisa sadaki dubu d'ari. Ango yayi kyau cikin farar shadda d'an daidai shi, rigan iya guiwa dan yace shi baya isa saka babban riga. Fuskan shi ba yabo ba fallasa, sai dai ta wani b'angaren yana farinciki mara misaltuwa idan ya tuna da Ummyn shi. Bayan an d'aura aure akayi k'asaitaciyar walima a nan harabar gidan. Sannan kowa ya kama gabansa. Bayan Magriba ana shirye shiryen d'auko Amarya Ummy Abba ya kira Jamal d'akinsa. "Jamaludeen!" Ya d'ago ya kalli Abba tareda amsa wah "Yanzu ka shiga wani rayuwa na daban, ka zama babban mutum, inaso ka kasance mutum mai adalci tsakanin Iyalinka. Karka zama mai yawan sa ido, sannan kada ka fifita d'aya ka bar d'aya" Kan Jamal k'asa yace "Insha Allahu" Key Abba ya mik'a mai da takardu yace "Wannan keyn gidan ka ne na baka halak malak, saidai inaso ku fara zama a nan gidan saboda naga kamin ludayin zaman naku" Godiya sosai Jamal yayi masa kansa k'asa. Abba ya nisa yace "Akwai wani sirri dayake cikin zuciyata wanda nake son sanar

Table of Contents

Chapters

82 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82