Skip to content

Chapter 11

Chapter 11

Jamaluddeen Book One Complete Hausa Novels 1,198 words 0 views Progress saved
Download Book

mata kai "Allah sarki Mama ya take? Ya jikin Baba" "Dasauki" Ummy ta bata amsa. A tare suka gama gyaran alaiyahun, sannan suka wuce d'akin Ummy, tsaraban ta ciro mata na kayan ciye ciye da Mama ta bata ta kawo mata, su goruba da tsamiyar biri dadai sauransu, sosai Laurat taji dad'i tayi godiya sosai. Sannan tace "Kinsan meke faruwa a gidan nan kuwa?" Ummy ta girgiza kai alamar A'a, Laurat tace "Nima d'azu muna hira da Mama Talatu take cemin wad'an nan turawan masu kula da Jamaludeen zasu koma k'asarsu gobe da safe" Ummy ta zaro ido dasauri "Kai dan Allah dagaske?" Laurat ta gyad'a kai "Wallahi kuwa, wai an kirasu a k'asarau, dama ma'aikatan asibiti neh" Jikin Ummy neh yayi sanyi tace "Tho yanzu wazai cigaba da kula dashi?" "K'ila zasu samo wasu neh ina ganin" Shiru Ummy tayi duk saitaji hiran ta gunduretah. Haka ta yini jugum ranta bai mata dad'i, tausayin Jamal ne ya cikata. Da safe bayan ta idar da sallan asubah tana zaune kan sallayabtaba lazumi aka banko k'ofan d'akin, Mabrookah ta gani tsaye tana yatsine yatsine tana bin d'akin da kallo "Ki fito Mami da Abba na kiranki a falo" Ta sake banko k'ofan ta fita daga d'akin. Girgiza kai Ummy tayi cikeda takaici, saida ta gyara hijabin jikinta sannan ta fito zuwa falon, bataga kowa ba dan haka ta haura zuwa falon sama, hangosu tayi zaune jugum jugum ta shiga da sallama ta samu guri k'asan carpet chan nesa dasu ta zauna, d'aya bayan d'aya ta gaishe su, Abba ya kalli Mami yace "Itace yarinyar" Mami tace "Itace, kuma nasan zata iya" Gaban Ummy ya yanke ya fad'i, tad'an d'ago kai tana kallan Mami, Abba yace "Ki kwantar da hankalinki, ba wani abu baneh. Nasan kinsan d'ana Jamaludeen" Ummy tace "Eh" Abba ya cigaba da cewa "Kuma nasan kinsan lalurar dayake tattare dashi" Nan ma ta sake gyad'a kai "Akwai turawa wad'anda suke lura dashi dangane ga abincinsa da kuma maganinsa dadai sauran yan abubuwa da suka shafe shi, tho yanzu wa'adin da suka d'iba ya cika kuma sunce bazasu k'ara kwanaki bah. Dan haka shine nake neman wanda zai cigaba da aikinsu" Ya nuna Mami yace "Shine Hajiya tacemin zaki iya" Shiru tayi kanta a k'asa. Hajiya tace "Bakice komai ba Ummy" Abba yace "Karki damu indai maganan albashi neh zan ninka miki akan abinda ake biyanki, zan rink'a biyanki dubu d'ari duk wata" Da mamaki Ummy ta d'ago ta kalleshi, ya gyad'a mata kai tace "Zan Iya Alhaji, saidai kud'in yayi yawa" Mami tayi murmushi tace "Karki damu buk'atarmu dai ki yarda, sanin halinki da k'wazon ki yasa na amince dake akan aikin" Shiru ta sakeyi anya kuwa zata iya wannan aikin? Ummy Abduol✍🏻 [3/12, 8:26 AM] ‪+234 806 215 4020‬: ♠♠♠♠♠♠♠♠ ♠♠♠♠ *JAMALUDEEN* ♠♠♠♠ ♠♠♠♠♠♠♠♠ By *Ummy Abduol* Dedicated to My *Late Siblings* Page 14 Shiru ta sakeyi anya kuwa zata iya wannan aikin "Ke muke jira har yanzu bakice komai bah" Mabrookah ta tab'e baki tace "Mami dama kun kyaleta, wannan ba iyawa zatayi bah" Mami ta galla mata harara, ta kauda kai gefe tana turo baki. Ummy tad'an d'ago tace "Zan iya saidai ban iya bashi abinci bah" "Indai wannan neh karki damu, za'a nuna miki komai" cewar Hajiya Abba yace "Tho Alhamdulillah tunda kin amince, sannan aikin bawai zaki dauwama dayi baneh, nad'an wani lokaci ne zuwa sanda za'a samo wad'anda zasu cigaba" Ummy ta gyad'a kai, Mami ta sallameta ta tashi ta koma d'akinta tana tunani. Ranar Mami bataje aiki ba saboda tafiyan turawan nan, an musu sha tara ta arziki (abunku da gidan mai naira) har airport aka kaisu suka hau jirgin lagos dan tachan zasu tashi. A ranar Mami ta koya ma Ummy yanda ake feeding d'insa, da kuma nuna mata rosters abincinsa da magugunansa. Sosai ta fahimta kuma a ranar Mami tace zata fara aikin, Saidai abinda Mamin bata sani bah shine Ummyn bata iya karatu ba dan bata iya karanta abinda ke jikin rostern abincin Jamal d'in. Wureren k'arfe sha biyu ta shiga kitchen ta samu Laurat tana yankan albasa, murmushi ta mata bayan ta k'araso wajanta "Taimako zakimin Laurat" Laurat ta d'ago tana kallanta "Taimakon meh fah" Nan ta fad'a mata aikin da Mami ta bata na kula da Jamal, da mamaki Laurat tace "Anya kuwa zaki iya Ummy?" Hararan wasa Ummy tai mata tana cewa "Mai zai hana, wannan ai wani dama ce na samu na samun lada, kinsan kula da mara lafiya akwai lada sosai" Laurat ta gyad'a kai "Tho Allah ya bada sa'a" "Ameen, ni kinsan ma menene Laurat" Laurat ta girgiza kai "Wallahi ni rubutun kayan abincin nasa neh bana ganeh wa, dan Allah ko zaki karanta min" Papern ta mik'a ma Laurat ta duba tareda zaiyane mata duk abinda ke cikin takardan. Godiya ta mata ta amsa tana cewa "Oh Ikon Allah kenan, jidai duk dukiya irin na mahaifinsa anma ya koma shan kunun gero da dawa" Cikeda alhini Laurat tace "Allah kai mana rowan ciwo dai" Ummy ta amsa da Ameen. Sallama tama Laurat ta haura sama zuwa d'akin Jamal d'in dan lokacin bashi abincin rana yayi, kunun tamba dake flask ta d'iba tasa madara da sugar kad'an sannan tad'au syringe ta soma zuk'a tana d'uramai ta bakin NG tube d'in dake hancinsa. Tana gamawa ta dama maganinsa shima ta basa. Zama tayi kusada shi tana kallanshi fuskanta d'auke da Murmushi, duk da hali dayake ciki na rashin lapia, ko kad'an baida rama a jikinsa koh alamar wahala sai ma wani k'ara haske dayakeyi. Idanunshi kamar kullum yana nan kyam a wuri d'aya baya kyaftawa. A haka Ummy ta cigaba da aikinta a gidan har batada lokacin kanta, kullum da sassafe take tashi ta soma gyara d'akinta sannan ta haura nasu Mami ta gyara da side d'in Alhaji. Kula kuwa da Jamal ba'a magana, ta d'aukema masu gyara masa d'akin da wankin kayansa, kullum ita take masa a washing machine dan Mami ta hanata wankin hannu tasa an koya mata yanda ake anfani da machine d'in kuma ta iya, duk weekend tana zuwa wajan iyayenta. Wani lokaci ta shiga gidansu Bilal wata rana kuma bata samun shiga. Kimanin wata Ummy biyu kenan a gidan, Mami da Abba najin dad'in yanda take kula musu da d'an nasu, kyautatawa na abubuwa da dama tana samu daga wajan Mami da Abba, Mabrookah kuwa har yau ba abinda ya chanza daga halaiyarda take nunawa Ummy. Yau bayan ta gama duk ayukanta, feeding d'in Jamal take tana kallan kyakyyawar fuskarsa harta gama sannan ta basa maganinsa. Zama tayi kusa dashi kamar kullum tana kallansa, wani dabara ce ta fad'o mata ta mik'e dasauri ta sakamai belt d'in dake wajan hannuwansa, ta saka masa na k'afa ta gunguroshi ta fito dashi daga d'akin. Dakyar ta sauko dashi k'asa ta fita dashi waje zuwa chan garden d'in dake bayan gidan, ma'aikata sai kallanta sukeyi dan yawancin su basusan ita ke kula dashi bah. Garden d'in ta kaisa ta ajeshi, kneel down tai a gabansa ta sa hannunta ta d'ago fuskanshi tana murmushi "Yau kaima ka fito kasha iska kaga haske" Dariya tayi hawaye cike a idonta tana kok'arin yin kuka "Jamal! Yaushe zakayi magana? Insan jin maganarka. Inasan naga ka warke"

Table of Contents

Chapters

82 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82