Chapter 33
Chapter 33
dakai tun ba yau bah, nasan...." Mami ta shigo falon a fusace tama cewa "Wallahi abinda kakemin Alhaji banajin dad'in shi" Ummy Abduol✍🏻 ♠♠♠♠♠♠♠♠ ♠♠♠♠ *JAMALUDEEN* ♠♠♠♠ ♠♠♠♠♠♠♠♠ By *Ummy Abduol* Dedicated to My *Late Siblings* *Miss Eshaa* na baki wannan shafin kyautah Page 37 n 38 "Wallahi abinda kakemin Alhaji banajin dad'in shi" Abba da Jamal suka d'ago suna kallanta, kusada Abba ta zauna ta cigaba da cewa "Haba Alhaji, meyasa kake zartar da hukunci ba tareda ka tambayi ta bakina bah, kamar yanda kake da iko da Yaran nan naka nima tunda ni ce uwarsa" "To me kuma akayi Maimuna" "Meyasa zakace bazasu zauna a sabon gidasu bah sai a nan" Abba yayi murmushi yace "Uwargida sarautar Mata, to maida wuk'ar, ai ba wani abu nace bah. Inaso ne naga kamun ludayin zaman nasu sannan sai su koma nasu gidan" Shiru tayi tana turo baki Jamal ya mik'a mata takardun gidan da Abba ya basa harda makulle yana cewa "Mamina ki tayani farinciki, Abba ya bani gida" Nan da nan b'acin ran Mami ya kau ta soma murna tana "Ah! Lallai Allah ya saka da alkhairi ya k'ara bud'i" Takardan ta amsa tana dubawa tana farinciki. Abba ya kalli Jamal dake durk'ushe har lokacin yace "B'angaren chan na k'arshe a nan zaku zauna, komai na buk'ata akwai. Sannan ita Ummy tana sama tunda itace Uwargida, ita kuma Mabrookah tana k'asa" Kanshi k'asa ya amsa tareda godiya. Mami ta mik'a masa takardun ya mik'e ya fita. Wayanshi ya ciro a aljihu dan yana silent, nan yaga missed calls d'insu Ram dayawa. Murmushi yayi ya fita haraban gidan, nan fa suka masa cha, shidai baice komai bah saima Taseem daya kalla yana cewa "Yanzu dan iskanci ace har k'arfe takwas baku je d'auko min amarya ta bah" "Kuji mana wannan guy d'in, tun d'azu fah muke jiranka a nan ka bamu go ahead" cewar Mifzal. "To shikenan kuje, Anma Ram nasan kai ba hankali ka cika bah, ka d'auko min matana a hankali banasan tafiyar ganganci" Tunda ya fara magana Ram ya saki baki yana kallansa har ya gama. K'wafa yayi ya shiga motarsa, sauran ma duk suka shishiga suka d'au hanyan gidansu Ummy. Tun bayan la'asar Ummyn ta dawo gidansu tana kukan rabuwa da Mamanta. Wani sabon kuka ta saki lokacin da aka kaita gaban Maman nata dan ta mata fad'a. Kuka ne ke k'okarin kufce ma Maman, dakyar ta daure ta mata nasiha mai ratsa jiki, gidansu Bilal aka kaita, Itama Inna ta mata nasiha sosai sannan aka fito da ita. Suna shiga cikin gida su Ram suka iso k'ofar gidan. Wani sabon kuka Ummy ta kece dashi tana kokarin turjewa daga rik'on da Inna ta mata, da k'arfi ka kwace ta shiga ta rungume Mama tana kuka sosai "Mama idan na tafi wa zai kula dake, dan Allah kar ki bari a tafi dani" Duk dauriya irin ta Mama saida tayi k'walla tana shafan k'an 'yar nata "Allah na tare dani Ummy. Darajar Mace gidan mijinta, ki tafi gidanki. Ina miki fatan Alheri Ummy" Ummyn ta sake rushewa da kuka, dakyar aka samu aka b'anb'areta daga jikin Mama tanata kuka, Inna da kanta ta sakata a mota itama ta shiga dan Mama ta bata amanar 'yar nata tun bayan rasuwan Baba. Su Twins da Laurat duk motan Abdulhakam abokin Jamal suka bi da kuma sauran 'yan uwa da abokan arziki. A jere motocin suka shigo cikin gidan, wani malalacin murmushi Ram ya saki sanda ya hango Jamal tsaye chan wajan garden ya kasa ya tsare. A k'ofar side d'in Mami Ram yayi parking, Inna da kanta ta fito rik'e da hannun Ummy bayan ta gyara mata lulub'in dake kanta. Jagora Aunty Zainab ta musu har zuwa d'akin Mami. Bayan an gaisa Inna ta damk'a amanar Ummy a hannun Mamin, ba yabo ba falasa Mamin ta amshe su tareda adduan Allah basu zaman Lafiya. Suna fitowa aka musu jagora zuwa side d'in da zasu zauna, koda suka shiga sun samu mutane a ciki da alama an kai Mabrookah neh. Aunty Zainab ta musu jagora zuwa sama har d'akin Ummyn. 'yan kai amarya sai santin gidan suke dan Abba ya kashe kud'i sosai wajan k'awata musu b'angaren nasu da funitures masu kyau. Tareda kayan kicin masu tsada da kyan gaske. Da kuka Ummy ta rabu da Inna bayan ta k'ara mata nasiha sosai. Ya rage daga ita sai su Twins dan tunda aka kawo Ummyn Laurat ta sulale ta koma bakin aikinta. Hira Twins keta Jan Ummyn dashi anma hankalinta baya wajansu sai neman wayan Bilal take switch off. Takai awa d'aya tana kira baya zuwa, wani kuka ne ya kufce mata ta kife kan makeken gadonta tana kuka sosai. Najma ta soma lallashinta anma kamar k'ara zugata take. Suna cikin haka aka turo k'ofar d'akin, Najma da Najwa suka d'ago suna kallan k'ofan. Wasu 'yan mata ne suka shigo su uku suna bin d'akin da kallo tareda yatsine fuska, Najma uwar rashin hak'uri tace "Lapia malamai kuka shigo mana d'aki bah sallama" Ba wacce ta tanka ta sai zagayen d'akin da sukeyi suna cigaba da yatsine fuska, Ummy ta d'ago tana binsu da kallo har lokacin k'walla na gangara a idonta. "Warning mukazo mu baki, karki sake ki shiga harkan Mabroo dan ba sa'arki baneh" cewar d'aya daga cikinsu "Dalla malamai ku fitan mana daga d'aki, kun shigo sai warin gardi kuke ga wani shegen attachment sai d'oyi" Cewar Najma A harzuk'e d'aya daga cikinsu ta nufota tareda chakume mata gaban riga, ganin haka yasa Ummy sake rak'ubewa tana zubar da kwalla Ta cigaba da cewa "Ke kinsan mu waye da kike gaya mana magana" Najwa itama ta mik'e rai b'ace tace "Karuwai mana dan bakuda banbanci dasu, wallahi kiyi maza ki sakar min 'yar uwa idan ba haka ba nayi maganinki" D'aya daga cikinsu ta janye hannunta daga gaban rigan Najma tana cewa "Karki biyema wad'an nan yaran kuzo muje kawai" Ta kama hannunta da d'ayar suka bar d'akin rai b'ace. Najma tace "Lallai Wallahi Ummy sai kin dage" "Ni Wallahi tausayi ma ta soma bani" cewar Najwa tana kallan Ummy daketa zubar da k'walla. Suna nan zaune har wuraren k'arfe goma, da wayo suka sulale suka bar Ummyn tana sharb'ar Hawaye. A bangaren Ango Jamal kuwa yana falon side d'in Abba shida abokansa, lokaci lokaci yakan kalli Rolex d'in hannunsa yana d'an tsaki a hankali, duk abinda yake Abduolhakam abokinsa na lura dashi, shi ya fara mik'ewa yace "Kai ku tashi mukai angon nan dan naga alamun idan bamu kaisa ba za kai kansa neh" Ram yad'an b'ata fuska yace "Wajan wa za'a kaisa tho" Karaf Jamal yace "Wajan Baeby na mana, kasan itace uwargida tunda ita na fara aure" Dukansu suka saki baki suna kallansa da mamaki "Ya da kallo" Ya mik'e yad'au ledan dake kusada Mifzal yace "Dallah ku taso muje" Shine a gaba suna binsa a baya sai tsiya suke masa shi dai baice komai ba sai murmushin da yake. A hankali ya tura k'ofan d'akin ya shiga da sallama, wani sanyaiyar k'anshi ne ya musu sallama, Ya matsa dasauri Taseem ya soma shiga sannan Mifzal sai Jamal d'in da kuma sauran abokanan nasa. Tana kwance tana aikin kuka taji sallamansu, dasauri ta
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82