Chapter 34
Chapter 34
mik'e ta gyara zama tareda gyara zaman gyalenta. Ram na shiga ya baje k'asan tiles d'in d'akin "Wash! Nidai na kama gurin kwana" "Aina!" Jamal ya zaro ido daidai lokacin daya zauna kusada Ummyn "A nan mana" Harara ya wurga mai, Mifzal yace "Sannu amarya bah magana" Shiru batace komai ba sai sheshek'an kuka da yake a hankali "Taya amarya zata maka magana ba'a sayi baki bah" cewar Taseem yana kallansa. Mifzal yace "Au haka neh fah" Yasa hannu a aljihu ya ciro rafan y'an d'ari biyu ya aje mata a kan gadon. Duk da haka dai bata iya cewa komai ba har lokacin kuka take a hankali wanda Jamal d'in kawai ke jiyota. Shakiyancin sukayi tayi sannan suka musu sallama suka tafi. Har bakin motocin su Jamal ya rakasu sannan ya dawo. Harya haura sama ya dawo yana tab'e baki ya nufi d'akin Mabrookah. Kan gadonta ya sameta tana sanye da wasu fitinanun night wears. Gabansa na ya fad'i ya kauda kai tareda k'arasawa bakin gadon "Haba Mijina tun d'aku fa nake jiran shigowanka naji shiru kuma bayan naji hayaniyarku" Ta matso kusada shi tana san manna jikinta da nasa, dasauri ya janye jikinsa yana yatsine fuska "Nazo ne naga lafiyarki, sannan na shaida miki yau a d'akin Ummy zan kwana tunda ita ce babba, ita..." "Haba Ya Jamal wanne irin magana kakeyi, ni fa matarka ce kamar yanda take matarka" "Anma kinsan dai saida aka fara d'aura aurenmu sannan aka d'aura naki koh" Turo baki tayi tana bubuga hannuwanta akan gadon alamar shagwab'a. A hankali yace "Saida safe koh" Ya mik'e tai saurin rik'e gefen rigansa tana magana cikin shagwab'a "Ina wai zaka ni fa wallahi tsoro nakeji" Janye rigansa yayi ya hasale yana kallanta "Da dakike kwana ke kad'ai meya kamaki" Yad'anja guntun tsaki ya bar d'akin dasauri. Sama ya haura zuwa d'akin Ummy, yanda ya barta haka ya dawo ya sameta saidai yanzu ba kuka take ba sai ajiyar zuciya datake saukewa lokaci zuwa lokaci. Kan gadon ya zauna ya matso kusada ita tareda sa hannu ya janye mayafin dake kanta. Kawar da fuska tayi dasauri, yayi murmushi tareda d'ago fuskanta da hannunsa. Ta lumshe ido dasauri hawaye suka gangaro daga idanunta "Oh God! Ya zanyi dake Baeby, dan Allah ki daina kukan nan. Bud'e idanunki ki kalleni" Bud'e idon tayi a hankali ta sauke su k'asa ta fashe da kuka. Batareda b'ata lokaci bah ya rungumota jikinsa yana shafa bayanta a hankali, turesa ta soma yi tana kuka mai sauti "Meye haka ka sakeni banaso" Janye jikinshi yayi daga nata yana kallanta da narkakun idanunsa "Ni mai sanki neh, i so much love uh Baeby, pls karki ce baki sona dan zan iya shiga damuwa mai tsanani. Ina sanki sosai" Ta d'ago jajayen idanunta tana kallansa da kuka "Idan nayi haka na karya alkawari, Ya Bilal ya sadaukar da abubuwa da dama dan rayuwata dana iyayena su inganta, ya..." "Pls wannan maganan ya wuce, i know nafi shi sanki" Ta d'ago jajayen idanunta ta zubasu kan nashi "Babu namijin dake sona kamar Ya Bilal, shine wan..." Saurin katseta yayi tareda saukowa daga kan gadon "Ki aje a ranki ni mai sanki neh, kisa a ranki ni mai baki farinciki neh. Bandamu da ko ki soni bah, sanda nake miki ya ishemu. And pls ki daina min maganan Bilal hakan na k'ona raina" Bai jira mai zatace ba ya bar d'akin zuwa nashi dake nan saman. Ummy Abduol✍🏻 [3/22, 5:21 AM] 0mmer Farouk: ♠♠♠♠♠♠♠♠ ♠♠♠♠ *JAMALUDEEN* ♠♠♠♠ ♠♠♠♠♠♠♠♠ By *Ummy Abduol* Dedicated to My *Late Siblings* Page 39 Bai jira mai zatace ba ya bar d'akin zuwa nashi dake nan saman. Kuka Ummyn ta fashe dashi tana dukan gadon da duk iya k'arfinta, tana cikin kukan bacci mai nauyi ya d'auketa nan kan gadon. Jamal ko bacci ne yayi k'aura daga idonsa, sosai hankalinshi ke tashi a duk lokacin da Ummy ta ambaci sunan Bilal. Kukansa ya soma kaiwa wajan ubangiji sai gefen asuba sannan ya samu bacci ya d'aukeshi a kan sallayan. Da safe da wuri Ummy tayi wanka ta gyara d'akinta tsaf da toilet dan tasan a aladar hausa washe garin da aka kawo amarya anayin bud'an kai. Hakan ce ko ta kasance, 'yan uwanta da abokan arziki duk sunzo da kayan lefenta sai gara da Baba sallau da Baba Tanko suka mata wanda bai taka kara ya karya bah. Ango Jamal bai farka ba sai k'arfe shad'aya ta kwata na safe, shima hayaniyar jama'a ce tasa ya farkan. "Subhanallahi!" Ya fad'a ya mik'e dasauri ya fad'a toilet, wanka yayi tareda d'auro alwala ya fito ya tada sallah. Yana idarwa ya shirya cikin bak'in yadi mai sharashara, d'inkin rigan daidai guiwa, sosai kayan suka fito da kyansa saidai kalli d'aya zakama fuskansa ka gane yana cikin damuwa. Had'adiyar Lace Ummyn tasa cikin na kayan lefenta, Najwa ce tayi mata makeup tayi kyau sosai, Itama Amarya Mabrookah ta had'e cikin atampa lemon green d'inkin dogon riga, fuskan nan nata yasha heavy makeup har tayi wani iri kamar aljana. Anyi bud'an kai lafiya tareda walima, ango na side d'in Abba shida abokansa suna hira, wayansa ne yayi k'ara alamar sak'o, bak'uwar number ya gani ya bud'e ya soma karantawa kamar haka _Kada ka tab'a tunanin dan an d'aura maka aure da Ummy hakan na nufin ka sameta, Ni Bilal indai ina raye baka isa ka mallaki Ummy ba saboda tawa ce! Kana wahalar da kanka a inda ba'a sonka ba'a muradinka. Kayi gaggawan rabuwa min da matata dan babu mahaluk'in daya isa ya rabani da ita sai Allah_ Wani guntun murmushi Jamal ya saki duk da cikin zuciyarsa yana fargaban abinda zaije yazo. Haka ya zauna sukuku kamar mara lafiya har yanma. Bayan kowa ya watse da daddare bayan isha'i ya shiga ya gaida Abba dasu Mami sannnan ya nufi side d'inshi, kamar jiya yauma d'akin Mabrookah ya soma shiga, zaune take kan gado cikin wasu arnayen kayan bacci, kallo d'aya ya mata ya kauda kai. Baisan meyasa ba Sam Mabrookah bata burgeshi, shishige mai ta soma ya mik'e a fusace yana hararanta ya bar dakin. Kamar zai shiga na Ummy sai kuma ya fasa ya shiga d'akinshi. Itako Ummy tana chan d'aki zaune shiru abin duniya ya isheta. Dakyar ta mik'e ta shiga toilet tayi wanka ta sauya zuwa na bacci ta kwanta. Washe gari monday da wuri yayi wanka ya fito cikin shirisa na fita aiki, d'akin Ummyn ya kalla sannan ya sauko k'asa Nan kan dinning d'in k'asa ya tarar da Mabrookah tana breakfast, a hankali ya k'arasa ya zauna. Ta kalleshi tareda tab'e baki tace "Ina kwana!" "Lapia" yace ta takaice yana bin abincin da takeci da kallo, ganin haka yasa tace "Mami ce ta aiko dashi, na zuba maka neh" Yad'anyi jim sannan yace "Ni ina azumi but ki zuba Ummy, koda yake kirata inasan magana daku" Fara'ar dake fuskanta ya kau ta had'e rai tana murgud'a baki "Haba Ya Jamal ni ne zan kirata" Wani mugun kallo ya bita dashi ta mik'e tana turo baki ta haura saman, kamar yanda ta saba shiga mata d'aki a wulak'ance haka yauma ta shiga, zaune ta sameta kan gado tayi tagumi "Keh ki fito mijina na kiranki" D'an d'agowa tayi tana kallanta, a
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82