Skip to content

Chapter 29

Chapter 29

Jamaluddeen Book One Complete Hausa Novels 1,199 words 0 views Progress saved
Download Book

zan iyayin komai a kanta matuk'ar ana neman a rabani da ita" Jamal yayi murmushin takaici yace "Kana santa ka bari har na aureta? Hakan ya nuna kai raggo ne akan soyaiya, bazaka iyayin komai dan ka mallaki abinda kakeso bah duk cika baki neh" "Haka kace!" Cewar Bilal a harzuk'e ransa b'ace Jamal ya sake sakin murmushi yace "Haka nace" Fuuuuuu Bilal yabar zauren. Sosai ran Jamal ya b'aci ya figi mota yabar anguwan cikeda takaici. ****** A b'angaren su Mami kuwa zagewa sukayi itada Aunty Faty sunata gyara 'yar tasu dan saura sati biyu biki, su Mabrookah kuwa sai b'arin d'uwawu take ita a dole amarya. Ana cikin haka Laurat ta dawo bakin aikinta, a bakin masu aikin kicin take jin labarin abinda ya faru, kuka sosai tayi gashi batasan gidansu Ummyn bah balle taje wajanta. Su Twins ta samu suka mata kwatance, washe gari kuwa ta saci hanya ta tafi. Ummy na zaune a tsakar gidansu tayi tagumi kamar a mafarki taji muryan sahibar tata. Mik'ewa tayi suka rungume juna a tare kuma suka fashe da kuka, saida sukayi mai isarsu sannan Ummy taja hannunta suka shiga Falo. Mama suka samu a falon, Laurat ta gaisheta tareda mata gaisuwa, Ummy ta gabatar da Laurat a wajan Mama sannan suka shiga d'akin Ummyn. Bayan Laurat taci tasha Ummy bata b'oye mata duk abinda ke faruwa bah, sosai Laurat ta tausaya mata, Ummy tace "Gaskiya Laurat ina cikin tashin hankali, Wallahi bana san aurena da Ya Jamal, Ya Bilal nakeso" Laurat ta gyara zama tace "Duk da ban tab'a ganin Bilal d'in nan bah, kuma bansan halaiyarsa bah. Nidai haka nan hankalina yafi kwanciya da Jamal" Ta dafa kafad'ar Ummyn tace "Wallahi kun dace keda Jamal sosai" Ummy tai saurin buge hannun Laurat d'in tace "Wannan irin magana kikeyi Laurat, kema kina sahun masu san rabani da Ya Bilal kenan" "Ba nufina kenan ba Ummy, abinda nakeso ki gane a nan shine. Babu abinda yazo zaki iyayi dangane ga maganar nan, karki manta. Yanzu haka kina a matsayin matar Jamal ne, tunda har an d'aura aure ba kuma abinda ya rage daya wuce kiyi hak'uri kima mijinki biyaiya" Shiru Ummy tayi ta sake rushewa da kuka. Lallashinta Laurat ta soma dakyar ta samu tayi shiru sannan ta mata sallama itada Mama tabar gidan. Tun daga ranan Innan Bilal ta soma gyaran 'yar nata kamar ba gobe, dan ita sam bata nuna kishi akan auran. Bilal ko abin duniya ne ya ishesa yau ciwo gobe Lafiya, haka Itama Ummyn. Ango Jamal kuwa tunda Haka ta faru tsakanin su da Bilal bai sake zuwa gidan ba duk da yanda zuciyarsa kesan ganin Gimbiyar tasa. Abba ne da Mami sai Mabrookah dake gefe da kuma Jamal harda Aunty Faty dasu twins. Gyaran murya Abba yayi sannan yace "Kamar yanda kuka sani, yau saura sati d'aya d'aurin auren Jamal da Mabrookah, saidai akwai abinda baku sani ba wanda yau nakeso na warware muku" Mami tace "Menene kuma Alhaji" Ya d'anyi murmushi yace "Sati uku da suka wuce aka d'aura auren Jamal da Ummy" Mami ta mik'e dasauri "Ummy fah kace Alhaji" "Kwarai da gaske ita" "Haba Alhaji, ya zakayi mana haka yanzu ita Mabrookahn fah" Nan da nan Mabrookah ta fashe da kuka, Jamal ko sai hararanta yake, ji yake kamar ya shak'eta ta mutu kowa ya huta. "Bance miki ai baza'a d'aura da Mabrookah bah. Itama idan Allah ya kaimu sati mai zuwa za'a daura nata. Sannan inaso ku sani banasan tashin hankali ko k'ananan maganganu" Mami ta zauna a sanyaye tana kallan Aunty Faty wacce keta hararan Mamin, ba'a gama magana ba Aunty Faty ta mik'e tabar falon tana huci. Abba ya cigaba da cewa "Kamar yanda kika zab'ar mai Mabrookah, haka nima na zab'a masa Ummy saboda na lura yarinya ce marainiya" Twins sai dariya suke k'asa k'asa cikeda farinciki. "Gobe a tara 'yan uwa da abokan arziki dan akai lefe gidansu Ummyn, kuma inaso ya zama rana d'aya za'ayi bikin dana Mabrookah" Mami dai ba amsa sai huci datake yi cikeda bak'in ciki, sallaman su Jamal d'in yayi, Mabrookah ta mik'e tana kuka mai had'e da ihu ta haura sama, Twins ma suka mik'e suka bi bayan Jamal sunata mai Congrat. "Fisabillahi yanzu Alhaji abinda kayi ya dace" "Ni ko nasan ya dace" "Gaskiya Alhaji bazai yuwu bah, a rasa wacce za'a daura ma Jamal sai b'arauniya" "Ya Isa Maimuna! Ki shiga taitayinki, ya ina magana kina magana. Tho bari kiji, ba gudu baja da baya aure dai an d'aura, kuma kamar yanda na fad'a miki gobe za'a kai lefe gidan su Ummy, sannan set biyu za'a kai mana. Idan kuma kika sake naji wani magana ya taso zamu sabu sab'ani dake sosai" Ya mik'e fuuuu yabar falon ranshi b'ace. Haurawa Mami tayi zuwa d'akin Jamal, batareda wani b'ata lokaci ba ta d'auke shi da mari "Ni! Ni Jamal kakeso ka wulak'anta?" Ta rushe da kuka "Ba laifinka baneh" Ta bar d'akin dasauri, kuka shima Jamal d'in ya fashe dashi, shi yanzu ina zaisa ranshi, ga Ummy bata sanshi, Ga Mami na fushi dashi, ga kuma auren Mabrookah da aka tilasta masa akai. Ranar Aunty Faty da Mami kacha kacha sukayi, washe gari kamar yanda Abba ya umarta, set biyu na akwati aka d'auka aka barma Mabrookah d'aya, gidan su Ummyn aka kai, Mama tace akai gidansu Innan Bilal, nan Inna tayi kiran Mak'ota aka amsa kayan cikeda farinciki. Tunda Ummy taji shigowan masu kawo lefen ta fashe da kuka, shikenan tasan aikin gama ya gama an rabata da Ya Bilal d'inta. A ranar Ramadhan ya diro Zaria, shi kad'ai yazo gidansu Ummyn ya kawo mata kud'in d'inki, dubu hamsin wanda Abba ya bada a kawo. Saida ya dinga had'ata da Allah sannan ta amsa tareda waya k'irar Samsung da Jamal d'in ya bada a kawo mata. Duk abinda sukeyi Bilal na hango su wanda yake bak'in k'ofar gida, ranshi ya b'aci sosai. Ramadhan d'in na tafiya ta juyo tayi hanyar gida, had'a ido tayi dashi gabanta ya fad'i, baice mata komai ba yayi shige wanshi gida. A sanyaye ta nufi gida, Mama ta nuna ma kud'in da wayan, tasa albarka sannan tace takaima Inna dan itace mai shirye shiryen. Bata samu ta kaiba sai washe gari, Nan take Inna ta d'au kaya kala goma ta saka a leda ita da kanta takai Ummyn wajan masu d'inki dan tasan idan tace ita kad'ai taje bazata bah. Tun daga ranar Ummy bata sake ganin Bilal bah, ko ta shiga gidan bata ganinsa. Bahar ta tambaya a nan yake fad'a mata ya tafi abuja wajan Alhajin daya zauna wajansa. Wani k'walla ne ya gangaro mata tasa bayan hannu ta share. Yau saura kwana hud'u biki, Laurat dakyar ta samu Mami ta barta ta tafi hutu kan cewa marik'iyrata batada lafiya. Tana tafiya tayo gidansu Ummy dan tayata shirye shirye. Sosai Ummy tayi Farinciki da zuwanta. Wayan da Ramadhan ya kawo mata ta nuna mata, Laurat ta kyalkyale da dariya tana cewa "Hala ma ko kunnata baki iya bah" Harara Ummy ta wurga mata "Ni ina ruwana ma da wayar" Dariya Laurat tayi ta kunna mata wayan, text ne ya shigo ta bud'e tana cewa "Ashe ma akwai Sim a ciki, har

Table of Contents

Chapters

82 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82