Chapter 60
Chapter 60
yanda nakeyi dah_ *Kusha Kurumin ku masu tambayan Labarin Jamaludeen, Insha Allahu yazo k'arshe nan da kwana kad'an zan gama* Page 72 n 73 Already dama ya sayi Ghana must go a hanya, zama yayi dirshan ya soma k'irga kud'in yana sakawa cikin Ghana must gon batare da wani tunanin bah, dan gaba d'aya hankalinsa nakan Wife d'insa. *A gurguje* Ram ya kali Mifzal fuskanshi ba walwala "Naji High court wajan lawyern dayazo da Wannan Alhaji Tijjanin, abin was terrible" Mifzal ya gyara zama yace "Kamar yah?" Ram ya sauke ajiyar zuciya yace "Anyi hayansa ne kawai yaje ya bada shaida akan bashin da akace Alhaji Tijjani na binsa" Sosai Mifzal yayi mamaki, yace "To yanzu menene abin yi?" Ram ya gyara zama ya matso kusada Mifzal yace "Kama Barr nan zakuyi ku tuhumesa, or a turashi state CID for investigation" Sosai Mifzal yaji dad'in shawaran Ram, ya mik'e yana cewa "Muje tare dan akwai tambayoyin da nakeso Alhaji Ameenu ya amsa min kuma inaso ya kasance a gabanka" A tare suka mik'e suka fito, already dama Mifzal yasa record a wayansa, inda Alhaji Ameenu yake suna nufa, Mifzal ya zauna kan kujera Ram kuma na tsaye gefensa "To Alhaji tunda ga lawyern ka a kusa dakai yanzu ina iya maka tambayoyi koh" Harara Alhaji Ameenu ya wurga masa, Mifzal yayi murmushi sannan yace "Inaso nasan ko kai wanene" Saida Alhaji Ameenu ya kalli Lawyernsa ya gyad'a masa kai sannan yace "Sunana Ameenu Jibril, ni d'an Kano neh, inada mata d'aya da kuma 'ya'ya biyu namiji da mace. Mafi yawan zama na a Egypt nake yinsa tare da iyalina" Mifzal ya jinjina kai sannan yace "Ko zan iya sanin sana'arka?" Barr. Ishaq ya karb'e da cewa "D'an kasuwa neh ku..." Saurin d'aya masa hannu Mifzal yayi ransa b'ace "Ina magana neh da Alhaji Ameenu Jibril bakai bah" Gum Barr. Ishaq yayi sai hararan Mifzal d'in yake a fakaice. Alhaji Ameenu yace "Kamar yanda lawyer na ya fad'a ni bussiness man neh, a da ne nayi siyasa" "Menene Alak'ar ka da Alhaji Surajo" "Mene kuwa tsakanin mu? Ni ko sunansa ban tab'a ji ba balle nasan shi" Sosai yanda Alhaji Ameenu ya daburce yaba Mifzal dariya "Come down Alhaji" Gaba d'aya Alhaji ya tsure sai muzurai yake yana zufa, Mifzal yace "An kashe Alhaji Surajo Ranar Ashirin ga watan January da daddare an shiga gidan Alhaji Surajo an kashe shi, ko zaka iya fad'amin ranar kana ina" Alhaji Ameenu ya k'ara tsurewa, muryansa na rawa yace "I...inna k..kuwa? Ina gidana dake Abuja mana" Barr. Ishaq yayi saurin cewa "Why all this questions? Ni Lawyern Alhaji Surajo kadiri neh, haka zalika ni Lawyern Alhaji Ameenu neh. Kuma inada tabbacin babu wanda yasan wani tsakanin su" Ran Mifzal in yayi dubu ya b'aci musamman yanda Barr. Ishaq ke d'aga murya yana magana a fad'ace. Yace "Kullum da daddare wuraren k'arfe tara zuwa goma kana fita daga gida ina kake zuwa?" Alhaji Ameenu ya juya ya kalli Barr sannan ya juyo ga Mifzal "Bana zuwa ko ina sai wajan kasuwanci nah" "Detective wannan tambayoyin ya isa haka, ba hannun Alhaji Ameenu a duk wad'an nan abubuwan. Kuyi gaggawan sakinsa ko na maka ku a kotu" Wani dariya Mifzal ya saki "Dako naji dad'i idan ka kaini kotu" A fusace ya mik'e yama Ram nuni ya biyosa, ba musu suka fita daga seil d'in. Barr ya kalli Alhaji Ameenu yace "Alhaji ka kwantar da hankalin ka komai zaizo k'arshe yau d'in nan" Mifzal na fita yasa wasu 'yan sanda su fito masa da Barr Ishaq, cikin sauri suka fito dashi aka kaishi Secret room sai fizge fizge yake yana fad'a. State CID aka kira sukazo suka tafi dashi dan a tuhumesa. Mifzal yace "Jamal na cikin wani hali na rashin Ummy, idan ka ganshi sai ya matuk'ar baka tausayi" Jikin Ram yayi sanyi yace "Kafin mu samu wani information akan Barr Ishaq mu duba Jamal d'in mu dawo. sai shima mu tambaya ko sun k'ara kira" Ba musu Mifzal ya zari key suka bar office d'in. A b'angaren Jamal kuwa, Cikin Awa d'aya zuwa da rabi ya gama had'a kud'in tsaf ya saka a ghana must go kamar yanda suka buk'ata. Zama yayi yana jiran kiransu dan su fad'a masa inda zai aje kud'in. Ba dad'ewa wayansa ya soma ringing, numbern Ummyn neh yayi appearing ya d'auka dasauri jikinsa na rawa ya kara a kunnensa "Hello Wife!" Muryan namijin nan neh ya sake ji, gabansa ya fad'i ya yayi saurin cewa "Ina matata? Ina take? Ga kud'in ku na had'a muku ina zan sameku" Daga chan b'angaren yace "Good Boy! Lallai kana san matar nan taka." "Dan Allah ka bani naji muryanta, dan Allah" Ba musu ya kara ma Ummyn a kunne, tana kuka tace "Ya Jamal ina kake? Dan Allah kazo ka tafi dani, ban..." Akayi saurin fizge wayan, hawaye ne suka soma zarya a fuskansa yace "Pls karku tab'ata, ku fad'amin inda zan aje muku kud'in na d'auki matata" Cikin wani irin dariya Mutumin yace "Ka aje kud'in a wajan bishiyoyin Bomo Village, daka iso wajan zamu ganka by 11:00am dot, kana wucewa zamu kasheta" Wani k'ara ya saki, kamin yayi magana aka kashe wayan, agogo ya duba yaga 10:15am. Ya fashe da kuka ya d'au ghana must go d'in dakyar ya fita, bai ko kalli Mabrookah dake masa magana tana k'okarin k'arasowa inda yake. Yayi saurin shiga motan ya tada ya bar gidan a guje. Fitanshi Express yayi daidai da k'arasowan su Mifzal bakin Layin, sam Jamal bai lura dasu bah ya k'arama motar wuta yayi gaba, da Mamaki Mifzal yabi motar da kallo "Kaga Jamal chan ina kuma zashi" Ram yace "Ji yanda yake driving da gudu, anya kamar ba lafiya bah mu bisa" Ba musu ya juya kan motan suka soma binsa da gudu suma. Hold up ya samu wajan ABU ya daki stiering motan wasu hawaye suka sake gangaro masa, agogo ya duba 10:40am, ya rushe da kuka yanata danna horn. Yakai Minti Biyar a wajan ya samu ya wuce ya cigaba da gudu su Mifzal na binshi, Bomo Village sukaga ya shiga suka suka sa kan motarsu ciki. Daga mirrown gaban motan ya Hango motar Mifzal d'in, ya sake dukan Stiering yayi saurin Parking ya fito yana kuka. Suma suna ganin Haka sukayi parking, ya k'araso inda suke tsaye "Dan Allah ku koma, ku kyalleni Pls karsu kashe min matana. Amsota zanje yi, dan Allahu ku koma" Gaba d'aya ya basu tausayi, Ram yace "Ka samu kud'in neh?" Ya duba Agogon Hannunsa 10:50am, wasu Hawaye suka sake zubo masa, cikin fad'a yace "Ku rabu dani! Ku tafi ku kyalleni" Ya sassauta murya cikin kuka yace "Zasu kashemin matata idan har bankai bah har 11:00am bah" Ha had'e hannayensa alamar bada hak'uri "Dan Allah ku koma, kuyi hak'uri" Hawaye Ram ya share na tausayin abokin nasa, ya duba agogon Hannusa 10:54am, Mifzal yace "Yi sauri tho" cewar Mifzal. Da gudu ya shiga mota ya figa a guje yabar wajan. Da wani matsiyacin gudu ya k'arasa inda sukace masa, Parking yayi ya bud'e booth ya ciro kud'in, a hankali yake tafiya har ya k'arasa wajan da akace ya ajiye. Gabas da yanma, kudu da arewa ya duba baiga kowa ba
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82