Chapter 73
Chapter 73
abinda ya faru, Abba yayi murmushi yace "Baka kyauta bah, haka itama bata kyauta bah. Muda ba zama zamuyi bah? Abuja zamu koma insha Allahu Jibi, Mun tsaya ne jiran Areefa tazo dan mu a gabanka tasan abinda ke faruwa" Ya d'ago idanunsa dake cike da kwalla "Pls Abba ku zauna dani, nayi maraicin ku for About 28yrs inaso mu kasance tare Pls" Abba ya girgiza kai "No Son, ai bai kamata muzo nan mu zauna bah" Ya rik'o hannun Ammi hawayen dake cike a idanunsa suka zubo "Pls Ammi kiba Abba hak'uri ku zauna tare dani Dan Allah" Areef ya karb'e da cewa "Ah! Nidai babu inda zani ina nan" Ya gyara zama tare da kishingid'a akan kujeran dayake, Jamal ya sake cewa "Pls Abba" Shiru Abban yayi sannan ya mik'e yana cewa "Zanyi tunani akai" Ya fita daga falon saboda kiraye kirayen Sallan da ake a masallacin gidan. Ammi ta rik'o hannunsa tace "What you did was wrong Jamaludeen, babu kyau namiji ya rink'a dukan matarsa, karna k'ara gani ko na k'araji kanajina" Ya gyad'a mata kai, ta shafa kansa tana murmushi "Allah ya maka albarka" Yace "Ameen" a hankali Suka mik'e shida Areef dan zuwa masallaci. Baiwar Allah Ummy sam batasan abinda ke faruwa ba tana chan side d'insu, yau cike take da farincikin ganin Iyayen mijinta, abinci mai rai da lafiya ta soma had'awa tana mai cikin nishad'i. K'arfe biyu na rana ta gama komai, Side d'in Jamal ya shigo shida Areef bai ko kalli D'akin Mabrookah ba ya haura sama Areef na binsa a baya, a falon sukayi kicibus da Ummy ta fito daga d'akinta taci kwalliya cikin wani dakakkiyar lace lemon green mai adon duwatsu Orange, sosai kayan ya amsheta, Murmushi ya sakar mata ta mayar masa, ya k'arasa inda take tsaye tana wasa da zoben hannunta, rungumota yayi jikinsa tad'an turesa ganin Areef na haurowa, k'ara matseta yayi yana shinshina wuyanta "Uh Look Cute Wife" Yad'an rad'a mata a kunne "I hope wannan ranan nawa neh" K'okarin turesa takeyi yana k'ara matseta, Areef dake tsaye a falon yayi saurin sa hannayensa biyu ya rufe fuskansa ganin yana k'okarin laluban bakinta, a hankali ta fisge tana tura baki "Juya bayanka ka gani" Ya juya a hankali suk had'a ido da Areef, Gyaran murya Areef d'in yayi yana Murmushin shakiyanci "Uhummm! Emmm Bro i tot fita kace zamuyi" _Fans bani da bakin baku hak'uri na rashin post kwana biyu, Ku cigaba da hak'uri da Ummyn ku komai ya kusa zuwa k'arshe insha Allah_ Ummy Abduol✍🏻 🖤🖤🖤🖤🖤🖤🖤🖤 🖤🖤🖤🖤 *JAMALUDEEN* 🖤🖤🖤🖤 🖤🖤🖤🖤🖤🖤🖤🖤 By *Ummy Abduol* Dedicated to My *Late Siblings* *Fcbuk Page* https://facebook.com/Ummy-Abduol-Novels-1033022590196192/ Page 89 "Uhummm! Emmm Bro i tot fita kace zamuyi" Jamal ya sosa k'eya "Ina zuwa" Yaja hannun Ummyn sukayi d'akinsa tanata k'okarin k'wacewa tana tura baki, kan gado ya direta ta mik'e tsaye dasauri "Kaga fah jiranka akeyi" Ya matso kusada ita ya rik'e kugunta yana murmushi tare da zira hannunsa a maranta "Ya babyna?" Ta sake turo baki, "Ni babu ruwana da babyn nan kullum sai yayi ta sa mutum rashin lafiya" Yayi dariya tare da kai bakinsa kusada nata, tayi saurin gocewa dasauri tana dariya "Bro d'inka na jiranka fah" Ya harareta yana d'aukan keyn mota kan bedside drawer "Allah ko Wife! Hmm zaki sani" A shagwab'e tace "Me nayi toh" "Bari naje mu nemo nida ke ne akan.." Ya nuna mata makeken gadon dake d'akin, hannu biyu tasa ta rufe fuskanta tana murmushi, shima murmushin yayi ya fita yana cewa "Sai na dawo" "Allah ya kiyaye hanya" Tace a hankali tana bin bayansa da kallo. K'eyar Areef ya kad'a dan ya lura baya jin magana suka fice. Saida taga fitarsu ta window sannan ta d'au hijab tasa ta fito, abincin data girka ta had'a akan Mayan trays guda biyu ta d'au d'aya ta nufi falon Abba. Da sallama ta shiga Ammi dake falon kan sallaya ta amsa mata tana murmushi, kan dinning ta aje sannan ta dawo ta tsugunna har k'asa ta gaida Ammin, cikin fara'a ta amsa mata ta mik'e ta d'auko d'ayan trayn wannan karan harda Abba ta gani a falon, shima ta tsugunna ta gaida sa ta k'arasa ta aje trayn, tsugunnawa tayi a falon cikin jin kunya ta gabatar musu da abincin. Sannu Ammi ta soma mata tare da sa mata albarka. Cikin nishad'i ta mik'e ta fito daga side d'in ta koma nasu, a falon k'asa ta had'u da Mabrookah tana zaune tana taunar cingum, kallo d'aya Ummyn ta mata ta kauda kai, Mabrookah ta saki dariya mai sauti tana cewa "Ayi dai mu gani idan tusa na hura wuta, uwar 'yan shishigi daga zuwan mutane an kama musu girki" Ta tab'e baki tare da kauda kai "Dangin miji dai ko kanka zaka yanka ka basu basa gani, a gama kankan ban a bari" Ummy ta saki murmushi ta haura sama tana girgiza kai, tana daga falon ta tana jin habaicin da Mabrookahn keyi. A Side d'in Abba kuwa, Ummy na fita Ammi ta mik'e tana cewa "Allah kuwa Alhaji Yarinyan ta shiga raina, kaga dai yau na fara ganinta Anma Wallahi ta kwanta min" Ta k'are maganan tana bud'e warmers d'in dake kan Dinnin d'in, k'amshi ne ya musu sallama, Ammi ta sake cewa "Alhaji ga abinci sai dai ba abincin ka akayi bah" Dinning d'in ya k'araso ta bubud'e sauran warmers d'in tana dubawa, ya zauna yana cewa "Sai dai ki zubamin Farfesun kawai naci" Ba musu ta zuba masa farfesun kajin a saucer ta mik'a masa ya saka cokali ya soma ci. K'aran bud'e gate sukaji chan sai ga Jamal da Areef sun shigo da sallama rik'e da ledoji, Chak Areef ya tsaya yana cewa "Ashe ma anyi abincin" Ammi ta juyo tana kallansu, Areef ya k'araso dasauri ganin Abba nacin nama, Ammi ta hararesa "To kura!" Yayi dariya "I love Meat Mum!" Dariya sosai yana Jamal ya k'araso wajan yana dariya, ledojin hannunsa ya aje yana kallan abinda suke ci "Ammi girki kikayi" Kai ta girgiza tana cewa "Aa sarakuwa ta ce ta kawo mana" Ko ba'a fad'a masa ba yasan Ummy ce, sallamanta sukaji daga bakin k'ofan falon, suka amsa Areef ya mik'e dasauri ya amsa trayn hannunta dake d'auke da bottle waters da drinks kala kala "Kawo na tayaki Aunty nah" Tayi saurin duk'ar dakai tana murmushi a kunyace, gaba d'aya kunya ce ta lullub'eta dan ko ba'a fad'a ba tasan Areef ya girme mata nesa ba kusa bah. Kallanta kawai Jamal yake cike da so da k'auna, Ammi tace "Sannu Jaleelah Allah ya miki albarka" A hankali tace Ameen ta d'an d'ago ta saci kallan Jamal, kashe mata ido yayi tad'an yi murmushi ta musu sallama ta juya zata fita, jin muryan Jamal tayi yana cewa "Abba bakacin abincin" Areef ya amshe da cewa "Ai Abba baya cin Shinkafa, yanada Diabetes" Bataji amsar da Jamal d'in ya basa ba ta fita daga side d'in. D'akinta ta koma ta d'au wayanta ta shiga internet, browsing ta soma yi sannan ta mik'e dasauri ta shiga kitchen. Miyar Egusi ta d'aura mai rai da lafiya, nan da nan gidan ya bud'e da k'anshi, Mabrookah dake falonta sai had'iyar yawu take tana Hararan Stirecase d'in falon. Tana nan zaune Jamal ya shigo
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82