Chapter 54
Chapter 54
tab'e baki tace "Ai kinsan tarbiya daga gida yake farawa, idan uwa babu ta yara zasu samu" Mabrookah ta amshe da cewa "Ragowar Soyesoye, Allah dai yasa cikin nan nasa neh" Aunty Faty tace "Aikuwa kinsan irinsu da bin mazan tsiya, wayasan nawa aka zubar kafin a samu wannan" Ummy ta fashe da kuka tace "Dan Allah kuyi hak'uri, zan dunga zuwa da wuri ina gaish..." "Dallah rufe mana baki" cewar Aunty Faty, itako Mami tsabar takaici ne ya hanata magana sai bin Ummyn take da kallo cike da tsana. "Ai tuntuni ke kikayi sakaci Maimunatu har kika bari ta zauna a gidan nan bayan warkewan sa" Mami ta tab'e baki "To ya zanyi, Alhaji ne yace bazata ko ina bah, kuma kinsan duk abinda ya fad'a ta zauna babu wanda ya isa ya tsallake" Aunty Faty taja dogon tsaki batace komai bah. Chan kuma tace "Ai ko wallahi kafin Jamal d'in ya dawo sai kinci ubanki a gidan nan" Ta maida dubanta ga Mami "Tunda yanzu babu masu aiki, ai ga wata mun samu" Mabrookah ta fashe da dariyan k'eta tace "Wallahi kuwa Mummy, ni kawai girki zata dunga min" Ummy ta d'ago ta kalli Mabrookah, aiko suka had'a ido "Bar kallona, shegiya Maiya. Kindai san Ya Jamal baya nan, wallahi sai na miki shegen duka naga uban da zai k'waceki" Nan Ummy tasha jinin jikinta, in akwai abinda take gudu bai wuce a tab'a lafiyar jikinta. Mami tace "Aikin gidan nan ya koma hannunki daga yau, shara, mopping, gyaran d'akunan mu da girki." Wani shu'umin murmushi Aunty Faty tayi tana kallan Ummyn sannan tace "Ai yau zata fara aikin nata tunda dai babu masu yi" Tana hawaye ya mik'e ta shiga store inda ake aje tsintsiya da sauran abubuwa. Mami ta kalli Aunty Faty tace "Babban bak'inciki na bai wuce cikin dake jikin yarinyan nan bah, harga Allah banasan had'a zuri'a da wannan yarinyar" Aunty Faty ta fashe da dariya mai sauti sosai "Kwantar da hankalinki Maimunatu, wannan ai abu ne mai matuk'ar sauk'i" Mabrookah ta sauke ajiyar zuciya dan itama sosai ta tsani cikin Ummyn. *** Da wuri Jamal da Ram suka shirya suka fita zuwa Office d'in lawyern dake zone 2, saidai abin takaici basu samesa ba sai PA d'insa nan yake shaida musu baya k'asar yaje wani confrence meeting a Cairo anma zai dawo zuwa tuesday. Ba haka ransu yaso ba haka suka koma hotel d'in da suka sauka. Sun yanke shawaran tsayawa a abujan har zuwa sanda zai dawo. Jamal ya d'auko wayansa ya cigaba da neman layin Ummyn bata d'auka bah. Hankalinsa ne ya tashi sosai na rashin d'aukan wayansa da batayi ba. Tunani ya soma ko jikin nata ne ya tashi, da lafiya lau yasan da yanzu ta d'auka. K'ara kira yayi har ya katse ba amsa, yayi wurgi da wayan tareda jan tsaki "Anya Ram bazamu koma zaria ba kuwa" Ram dake kan gado yana chating ya juyo da mamaki "Saboda meh?" "Tun safe nake kiran Wife bata d'auka, inaji a jikina something is wrong dan ko laifi na mata bata k'in daukan wayana" Ram ya mik'e zaune yace "To ka kira Mabrookah mana ko Mami" Jim yayi na 'yan mintina sannan ya soma neman layin Mami, bugu d'aya ta d'auka da sallama, bayan sun gaisa yace "Mami tun safe nake kiran Ummy bata d'auka bah, i donno ko jikin ne dan na barta bata jin dad'i" Tad'an juya ta kalli Aunty Faty dake zaune kusada ita sannan tace "Lafiya lau take kam, dan ko d'azu da safe tashigo ta gaishe ni" Nannauyan Ajiyan zuciya ya sauke har saida Mami ta jiyosa, ta tab'e baki tace "To ita Mabrookan ka kirata" Saida yad'anyi Jim sannan yace "Itama bata d'auka bah" Tambayansa abinda sukaje yi tayi yake shaida mata basu samesa ba sai ran tuesday. Tamai addu'a sosai sannan sukayi sallama. A b'angaren Ummy kuwa ta wahala sosai ranar, ga jikinta da ba wani k'wari, duk bayan 'yan mintina sai tayi amai, tana kuka tana aikin har ta gama, ba ita ta koma side d'insu ba sai bayan sallahn Magriba, dakyar ta iya k'arasawa d'akinta tayi wanka ta kwanta, nan da nan zazzab'i mai zafi ya rufeta. Cikin bacci taji wayanta na ringing kan bedside ta mik'a hannu dakyar ya dauka tare da karawa a kunne "Haba Wife yanzu abinda kikamin kin kyauta kenan" Kuka ta soma mara sauti "Ya salam! Meya faru? Ko jikin neh" Duk yabi ya rud'e hankalinsa a tashe, kasa fad'a masa tayi dakyar ta iya cewa "Bai kaine kak'i dawowa bah" Ya sauke ajiyar zuciya tare da k'ara kara wayan a kunnensa "Tun safe nake neman wayanki baki d'auka ba Wife, hankalina ya tashi sosai na d'auka jikin neh" Hawaye suka k'ara gangaro mata, cikin sanyin murya tace "Banga wayan baneh kuma yana silent, sai d'azu na duba k'arkashin gado ashe nan ya fad'a" "Pls ki daina sa wayanki a silent kinji" "To" tace a hankali, sun d'an tab'a hira sannan sukayi sallama. Kuka ta sake fashewa dashi na tausayin kanta kafin Jamal ya dawo. A daran ranar Mifzal ya iso abujan, nan hotel d'in dasu Jamal suka sauka nan shima ya sauka. Washe gari dasafe dukansu suka shirya suka fita. Saida Mifzal ya fara reporting a Station d'in dayakai case d'in sannan suka wuce Wuse 2 dan a nan suka samu labarin Bilal d'in yake. Daga bakin layin sukayi parking, Mifzal da Ram suka fito suka shiga cikin layin sosai suna takawa suna bin gidajen layin da kallo. Wani mai shago suka samu nan suka zauna kan benchn sa tare da masa sallama. Bayan ya amsa Ram ya mik'a masa dubu d'aya "Bamu Fayrous guda biyu" Jiki na rawa mai shagon ya mik'o musu dan yau kusan kwana biyu kenan babu ciniki, ya irgo chanji ya mik'a masa. Mifzal yayi saurin cewa "Ka bashi, dan Allah mallam in tambayeka mana" Jiki na rawa yace "Allah yasa na sani" "Dan Allah wani nake nema sunansa Bilal, abokina ne sosai saidai lambarsa ta b'ace a wayata. Kuma gashi tun daga Kano nazo nemasa" Mutumin ya rik'e baki da Mamaki "Wai! Kace kasha tafiya, sai dai ni bansan wani mai suna Bilal ba anan layin" Mifzal ya d'au wayansa ya zak'ulo hoton Bilal d'in dake jikin Dp d'insa na whatsapp ya nuna masa "Ka ganshi nan" Baki mutumin ya bud'e "Aa indai wannan ne ai na sanshi, yakanzo nan wayena yasayi sigari" Ram da Mifzal suka kalli juna da mamaki. Ram ya wayance yace "Tabbas kuwa shine, dan Allah bakasan gidan dayake bah" Wani dank'ararren gidan chan gefensa ya nuna musu da hannu "Ga gidan chan, saidai...." Yayi saurin yin shiru ya matse bakinsa da hannu, Mifzal ya kallesa yace "Fad'a abinda kakeso ka fad'a babu komae" Ram ya ciro dubu uku ya aje masa ga wannan ka tab'a, aiko d'an fulani ya gyara zama "Akwai abinda mu 'yan unguwan nan bamu gane masa bah" "Na meh fah" cewar Ram "Alhajin nan bashi fita sai da daddare, sannan kuma kullum sai kaga wasu murd'a murd'an mutane a k'ofar gidansa wanda mu bamu yarda dasu bah" Mifzal ya jinjina kai, "Kamar da wani lokaci sukafi zuwa?" "Kaman tara haka zuwa goma na dare idan dai kazo nan zaka samesu" Mifzal
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82