Skip to content

Chapter 75

Chapter 75

Jamaluddeen Book One Complete Hausa Novels 1,202 words 0 views Progress saved
Download Book

saurin rik'osa yana cewa "Haba D'an Mami yi hak'uri mana, zauna kaji" Ya zaunar dashi shima ya zauna suna fuskantar juna "Suna prison yanzu haka baza'a bari ka gansu bah" Shiru yayi baice komai bah, Ram ya soma jansa da hira har ya samu ya ware sukayi ta hira, a nan yake basu labarin zuwan Areefah." A gida kuwa Areefah na sallah ta koma side d'insu Ummy, Kallo d'aya tama Mabrookah taja guntun tsaki ta haura sama wajan Ummy. Hira sukayi tayi gwanin ban sha'awa, tare sukayi abincin dare sunata hira kamar sun dade da sanin juna. Ran Mabrookah ya sosu sosai, ta mik'e ta shiga kicin ta soma kici kicin d'aura abinci. Tuwon shinkafa tayi da miyar Alaiyahu datasa Mai gadi tasayo mata. Cikin k'ankanin lokaci ta gama, wanka tayi ta sauya zuwa dogon rigan shadda. Ta had'a abincin a tray ta d'auka bayan anyi sallahn magriba, dai dai nan Areefah ta sauko da Tray itada Ummy, Kallansu Mabrookahn tayi ta watsar tayi gaba suna binta a baya, Areefah sai yatsine fuska take dan gaba d'aya Mabrookah bata burgeta, da Sallama Mabrookahn ta shiga Ammi ta amsa, kan dinning ta aje Trayn a tsaye k'erere ta gaida Ammin tana wani cika tana batsewa. Areefah ta k'arasa kan dinning d'in ta ture trayn Mabrookahn gefe ta aje na hannunta, Sannan ta amsa na Ummy a aje, Ammi na daga gefe tana ta musu sannu da godiya. Mabrookah tayi gaba, Itama Ummy ta mik'e ta musu saida safe ta fita, a falon k'asa tayi kicibus da Mabrookahn tana jiranta "Kwad'ayaiya, nasan dai duk abinda kikeyi nan na kwad'ayi ne dan kinga suna dashi, An saba da maula" Ran Ummy ya sosu ta wuce zata haura sama ta sake jiyota tana cewa "In ma so kike ki mallake su karyanki tasha k'arya, Uwa ta saba da bin bokaye dole 'ya ma tad'au hanya. Wayasan abinda aka kitsa miki da kikaje gidan ranan" Ran Ummy idan yayi dubu ya b'aci, ta sauko k'asan "Kullum kina zagina ban tab'a maida miki da martani bah, dan har yanzu ina miki kallan wadda ta girme mani, ko ba komai kin fini shekaru bazanyi musu dake bah. Anma yau kin kaini bango" Wani shewa Mabrookah ta saki tana cewa "In kinama Allah kada ki k'ara ganin girman nawa" Murmushin takaici Ummyn tayi tana cewa "Kiyi ta zagina daga nan har abada anma karki k'ara zagin iyayena dan basu miki komai bah" Bata ankara bah taji saukan Mari a kuncinta, ta dafe wajan dasauri tana kallan Mabrookahn "Kika mareni" Tana huci tace "An mareki ko zaki rama neh, shegiya 'yar masu bin bokaye" Mari Ummyn ta d'auke Mabrookahn dashi mai rai da lafiya, nan fa fad'a ya kaure tsakaninsu, kokawa suka shiga yi tsakaninsu dai dai lokacin Jamal ya shigo cikin gidan, kamar zai shiga side d'in Abba sai kuma ya nufi nasa, yana shiga Mabrookah ta rarumi Dogon speakern home theatern dake Falonta ta bugama Ummyn a...... Ummy Abduol✍🏻 🖤🖤🖤🖤🖤🖤🖤🖤 🖤🖤🖤🖤 *JAMALUDEEN* 🖤🖤🖤🖤 🖤🖤🖤🖤🖤🖤🖤🖤 By *Ummy Abduol* Dedicated to My *Late Siblings* *Fcbuk Page* https://facebook.com/Ummy-Abduol-Novels-1033022590196192/ Page 90 _*A Gurguje*_ Yana shiga Mabrookah ta rarumi Dogon speakern home theatern dake falonta ta bugama Ummyn akai, Wani k'ara ta saki take ta fad'i wajan a sume jini na fita a kanta. Jiki na rawa ya k'arasa falon gaba d'aya jikinsa rawa yake, tsugunawa yayi inda Ummy ke wance ya d'agota hawaye cike da idanunsa, d'agowa yayi yana wani irin huci yana kallan Mabrookah wace ya yarda Speakern itama jikinta na rawa tana kuka. A fusace ya mik'e ta juya zata gudu ya kamota ya soma had'ata da bango yana kuka, ihu take a wahale tana neman agaji, Ammi da Areefah ne sukaji yo ihun Ummy da farko, har Areefahn ta mik'e Ammi ta hanata, jin wani ihun yasa suka mik'e a tare sukayo side d'in. Suna shiga ya sake bugata da bango ta saki k'ara take itama kanta ya fashe. Ammi ta k'arasa dasauri inda suke tsaye ta rik'esa gaba d'aya ta rud'e "Jamaludeen karka kasheta, stop! Control your anger" Ya jefar da ita tare da nunta da yatsa "Na sakeki! Na sakeki!!" Harya bud'e baki da niyar furta wani abu Ammi ta d'aukesa da wani gigitacen Mari "A gabana Jamaludeen!" Baice komai ba sai hucin dayake, Areefah ko tunda ta shigo ta fashe da kuka ganin Ummy kwance cikin jini, inda take ta k'arasa ta tsugunna tana kuka. Jikinsa na rawa ya d'au Ummyn yayi waje da ita, ko takalmi babu a k'afan Areefah tabi bayansa, mota ya sakata ya ja da k'arfi bayan Areefah ta shiga suka bar gidan. Fitowansa yayi daidai da fitowan Abba da Areef daga masallaci, da ido sukabi motan ganin yanda yake gudu kamar wanda zai tashi sama. Suna shiga Ammi ta fito daga side d'in rik'e da Mabrookah wacce itama kanta ke jinin "Subhanallahi meya faru?" Cewar Abba yana k'arasawa wajan, Ammi bata b'oye masa komai akan abinda ta gani bah, sam Abbah baiji dad'in abinda ya faru bah. Areef yana daga gefe yana cin magani yanata ma Mabrookahn Allah ya k'ara a zuciya dan dama kwata kwata bata burgesa. Wani Private hospital mafi kusa Jamal yakaita, duk tabi ya rude in banda hawaye babu abinda yake haka Areefah dake gefensa sai kuka take itama, suna isa aka amsheta sukayi Emergency da ita, Wata nurse ta umarce shi daya je ya biya kud'in kati da sauransu, ba musu ya nufi receiption Areefah na biye dashi. Suna nan zaune wata nurse ta fito daga d'akin, Areefah tayi saurin mik'ewa tasha gabanta "Dan Allah ya jikin nata?" Nurse d'in ta mata murmushi "Dasauk'i karku damu" Bata jira cewar Areefan ba tabar wajan dasauri, suna nan tsaye likitan ya fito, Bayani yama Jamal d'in akan abin bai yi serious ba saidai su kiyaye nan gaba. Sannan ya basu umarnin shiga su ganta. Kwance suka sameta kan gado kanta nan nad'e da bandage tana bacci hankali kwance, wani nannauyan ajiyan zuciya Jamal ya sauke ya k'arasa bakin gadon, Areefah ta rik'e hannunta hawaye cike a idonta "Allah zai saka miki Aunty, kuwa wallahi..." Taji k'wafa ranta b'ace. Shidai Jamal bai iya cewa komai bah. Suna nan Abba ya kira wayan Jamal yana tambayansa mai jiki, halinda ake ciki ya fad'ama Abban sai a lokacin suma hankalinsu ya kwanta. A gida kuwa Ran Ammi ya b'aci sosai gaba d'aya ji tayi Mabrookah ta fitar mata a rai, babban damuwarta bai wuce cikin dataga alamar Ummyn nadashi bah. Buris tayi da Mabrookahn haka shima Areef ji yake kamar ya rufeta da duka. Dad'in ta d'aya ma dayaji Ammi tace Jamal ya saketa. Rashin sani gari yasa Abba had'a Mai gadi d'aya da Areef da ita Mabrookahn aka kaita wani Chemist nan kusa akayi mata treating kan. Koda Jamal ya fad'ama Abban halin da Ummyn ke ciki kasa sukuni Ammi tayi, kwatance tasa ya musu Areef ya d'aukesu itada Abba sukaje asibitin. Ammi har hawaye tayi ganin Ummy kwance a kan gado, Kwana biyun nan da sukayi sosai ta shiga ranta. Ta share hawayen fuskanta tana kallan Abba "A gaskiya Alhaji zaman Jaleelah da Yarinyan nan Mabrookah bazai yuwu bah" "Wani irin magana kike haka Hajiya, karki manta fah matarsa neh bamu isa mu rabasa ta itaba" Shidai Jamal

Table of Contents

Chapters

82 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82