Chapter 3
Chapter 3
kallan hannun tareda murmushi "Kyawun zoben yasa na siyeshi, dan nasan zaima Hrt d'ina kyau. Ki rik'emin amana pls, duk da nasan ke tawace, just 2weeks zanyi kinji" Kai ta gyad'a mai ya mata sallama ya shiga gidansu da sauri, tsaye Ummy tayi a kofar gidan tana kuka a hankali, tana san Ya Bilal tana kishinsa, batasan koda na kwana d'aya su rabu. Saida tayi mai isarta sannan ta shiga gida.. Kasancewar lokacin sanyi ne har Mama ta shiga d'aki saidai tana d'aga bak'in kofa tana jiran Ummyn, tana shigowa taji Mama daga d'aki tace "Ummy kece" A hankali tace "Eh Ni ce" "Yaudai kam kun dad'e" Batace komai ba ta shige d'akinta ta fad'a kan katifarta tana ajiyan zuciya. Kud'in dake hannunta ta duba, dubu biyu ne y'an dari biyar biyar guda hud'u. Ta tusa su k'arkashin Pillow ranta duk ba dad'i Tunanin rayuwar Ya Bilal ta soma, tun tasowan shi yake aikin k'arfi dan taimaka mai mahaifiyarshi da k'aninshi, ga kuma itada da iyayenta, duk da nauyin dake kanshi bai hanashi yin karatunshi bah, ynzu haka yanada degree saidai ita batama san maiya karanta bah. Tunani kala kala ta dunga yi har bacci ya d'auketa Da safe kamin ya tafi saida yashigo shida Bahar sukaima su Mama sallama, ya shiga sukayi sallama da Baba sannan suka fito Ummy na biye dasu, Bahar ya basu waje sukai sallama sai kuka takemai a haka suka rabu kowa zuciyarshi ba dad'i Ummy Abduol✍🏻 [3/11, 11:34 PM] +234 806 215 4020: ♠♠♠♠♠♠♠♠ ♠♠♠♠ *JAMALUDEEN* ♠♠♠♠ ♠♠♠♠♠♠♠♠ By *Ummy Abduol* Dedicated to my *Late Siblings* *Page 4* A haka suka rabu kowa zuciyarshi ba dad'i, yinin ranan sukuku Ummy ta yini, ko abinci tak'i ci saidai ta zauna tayi tagumi. Tun Mama na bata baki har ranta ya soma b'aci ta hau mata fad'a Haka suka cigaba da rayuwa a gida har na tsawon sati hud'u, tun Ummy na irga ranakun dawowan Bilal harta daina tasawa sarautar Allah ido, so dayawa takan shiga gidansu Bilal dan dai kawai taji ko ansamu labarinsa Anma shiru. Abubuwa sun taru sun mata yawa ga Rashin sanyin idaniyanta Bilal, ga talauci da suke fama dashi dan tuni sun cinye jarin waran, abinci ma yanzu dak'yar suke samu. Sosai abin ke damun Ummy duk ta rame tayi duhu kamar ba Ummyn dah bah.. Tana d'aki tana tunanin yanda rayuwarsu ta sauya lokaci guda, a hankali hawaye ya zubo mata murya chan k'asa tace "Allah sarki Baba Sanda kakeda idanu da lafiya ka watada mu, munji dadi Allah ya baka lafiya yasa kaci wannan jarabawan" Fashewa da kuka tayi mara sauti, saida tayi mai isarta sannan ta mik'e zaune tareda goge hawayen idanunta. Tunani ta soma na yanda rayuwarsu zai inganta nan gaba dole ta nemi mafita dan bazasu zauna su dogara ga Bilal ba shima akwai d'awainiyan gidansu a kanshi, dauriya kawai yake. Wasu hawaye ne suka zubo mata "Ya Bilal kana inane? Ka dawo dan Allah" Mik'ewa tayi a sanyaye ta janyo hijabinta tasa ta fito tsakar gidan, Mama ta gani tana kok'arin fitoda Baba tsakar gida yasha Iska. Dasauri ta k'arasa ta taimaka mata ta zaunar dashi kan tabarma "Sannu Baba" "Yauwa Sannu Ummy, ku cigaba da hak'uri kunji wata rana sai labari" Hawaye suka cika idanunta, ta shiga d'akinshi ta d'auko sandar shi ta tsugunna tace "Baba ga sandary ka" Lallube ya soma, ta kamo hannunshi ta saka mai sandar "Yauwa Ngd Ummy" Ta dubi Mama dake gefenshi tace "Mama barin shiga wajan Inna Yanzu zan dawo" (gidansu Bilal) "Tho a dawo lapia, karki dad'e" Tho tace ta mik'e ta fita, a zauren gidansu Bilal ta had'u da kaninshi Bahar, Gaidashi tayi ya amsa yana cewa "Ya kewar Yaya" D'an murmushi tayi kanta k'asa "Har yau bama samun wayansa, ina ga zanzo ne na bishi Abujan nan kawai dan jikina na bani ba lafiya" "Yanzu idan kaje Abujan ta ina zaka fara? Ance. Tanada girma sosai, mezai hana muje inda suke aiki ko zamu samu labarin shi wajan abokanan aikinsu dake nan" Gyad'a kai yayi "Hakane kin kawo shawara" "Barin shiga na gaida Inna sai na fito mu tafi" A tare suka shiga gidan, Inna na zaune tsakar gida tana bakace masara "Ummy ce da tsakar ranan nan" A kunyace ta tsugunna ta gaida Innan, "Ya Babanku da jiki?" "Dasauk'i" tace a hankali har lokacin kanta k'asa. Sallaman da akayi ne ya katse su, wata dilaliya ce dake anguwan ta shigo tana cigaba da rafka sallama, Ummy da Inna suka amsa mata ta k'araso ta nemi guri ta zauna, Ummy ce ta soma Gaidata sannan ta mik'e "Inna bari muje wajan aikinsu Ya Bilal yanzu zamu dawo" "Tho a dawo lapia" inna ta amsa mata, tana kok'arin fita daga gidan taji dilaliyan na cewa "Wallahi Ladidi wasu gidaje ne aka kawo min cigiyan masu aiki kuma za'a samu alheri dan ba gidajen k'ananan mutane baneh gashi har yanzu ban samu yarinya ba" Fita daga gidan tayi da sauri suka had'u da Bahar suka wuce wajan, mutanen dake wajan suka tambaya a nan suke shaida musu mummunan labari, d'ayansu ne yace "Ranar da suka tafi motarsu tai hatsari duka sun rasu babu wanda ya fita, dan achan aka musu sallah saboda yanda gawawakinsu sukayi" Ai bai k'arasa maganan ba Ummy ta fad'i wajan sumammiya.. Ummy Abduol✍🏻 [3/11, 11:36 PM] +234 806 215 4020: ♠♠♠♠♠♠♠♠ ♠♠♠♠ *JAMALUDEEN* ♠♠♠♠ ♠♠♠♠♠♠♠♠ By *Ummy Abduol* Dedicated to My *Late Siblings* Page 5 Ai bai k'arasa Maganan ba Ummy ta fad'i wajan sumammiya. A gigice Bahar yayi kanta yana kuka, jama'ar dake wajan sun tausaya sosai. Masu aikin wajan suka tsare musu napep suka saka Ummy dake sume a cikin napep d'in suka nufi gida. Suna isa gida Mai napep da Bahar suka shi da Ummy cikin gida sai kuka yake, a nan yake sanar da Inna abinda ke faruwa, nan itama ta sume a wajan kamin kace me unguwan gaba d'aya ta d'auka ko wane lungu da sak'o sunji labarin rasuwar Bilal.. Sosai rasuwansa ya girgiza mutane saboda Bilal mutum ne mai Gaskiya da rik'on amana, ga addini da son jama'a. Ba abnda ke tashi daga gidan Inna sai koke koke, Baba da Mama suna daga cikin sukajiyo kuka daga gidan Inna, ta yafa mayafinta ta fito tun a kofar gida ta soma cin karo mutane sunata shiga, itama ba'a barta a baya ba tana shiga taji wannan mummunan labari. Kuka ta soma ta k'arasa inda ze zaune ta rungumeta tareda fashewa da kuka "Allah ya jik'anka Bilal yasa ka huta" Ta k'ara rushewa da wani sabon kuka, Ummy ko dogon suma tayi bata farka ba sai washe gari da safe, a hankali ta bud'e idonta ta suka k'ankance Mama ta gani kusada Ita itama fuskanta ba walwala, mik'ewan datake k'okarin yi yasa Mama tasan ta farka "Sannu Ummy, ina zakije" Fashewa da kuka tayi tana kallan Mama "Mama yanzu dagaske ne Ya Bilal ya rasu" Kanta Mama ta shafa tana lallashinta "Bilal lokaci yayi Ummy, yanzu addu'an mu yake nema ba kuka ba kinji. Kiyi hakuri ki fawala wa Allah" Girgiza kai take tana kuka da k'arfi "Aa Mama, Ya Bilal bai mutu ba ni nasani bazai tab'a mutuwa yabarni ba. Dan Allah Mama idan wasa yake kuce ya
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82