Chapter 14
Chapter 14
ta fito ta tsugunna ta gaidasa, Mami ya tambaya tace taje aiki, baice komai ba ya haura sama zuwa d'akin Jamal. Ummy Abduol✍🏻 [3/11, 8:33 PM] Alion Bagari: ♠♠♠♠♠♠♠♠ ♠♠♠♠ *JAMALUDEEN* ♠♠♠♠ ♠♠♠♠♠♠♠♠ By *Ummy Abduol* Dedicated to My *Late Siblings* _*Shekara shidda kenan da rasuwan d'aya daga cikin yanina, Ina baran Adduar ku Allah ya masa rahama yasa Aljanna ce makoma a gareshi. Ameen*_ Page 17 Baice komai ba ya haura sama zuwa d'akin Jamal, wayam yaga d'akin ya fito dasauri ya nufi sashin masu aiki yana tambayansu inda Jamal d'in yake, Laurat ce masa jagora har zuwa garden din. Tun daga nesa ya hangosu tana share masa zufa tana cigaba da rera masa karatun alkur'ani, dakatar da Laurat saurayin yayi suka tsaya nan wajan sai binsu da ido yake. Suratul Baqrah tayi bismillah ta fara, tana kan aya ta ashirin bata ankara ba taji an mak'ure mata wuya, idanunta ta fifito dasu ta d'ago dasauri Jamal ta gani idanunshi sun rune sun koma ja haka fuskan nasa, tari ta soma had'e da kakari tasa hannayenta tana k'okarin cire hannunsa akan wuyanta. Dasauri saurayin nan ya k'araso wajan ya soma janta dakyar ya samu ya fincike hannunsa daga wuyan Ummyn, chan gefe ta fad'i tana rik'e da wuyanta tana tari had'e da kuka kamar ranta zai fita. Laurat ta k'arasa wajanta dasauri, shi kuma saurayin ya tsaya gabanshi yayi bismillahi ya cigaba da karatun daga inda ta tsaya fuskarshi d'auke da damuwa. Wani irin zabura Jamal d'in keyi yana wani irin ihu, belt d'in wheel chairn ya tsitsinka yana ihu yana k'okarin mik'ewa, kan kace meh ma'aikatan gidan sun taru a wajan suna ba idanunsu abinci, itako Ummy nachan gefe idanu sunyi luhu luhu sabda shak'an da yamata. Karatun saurayin ya cigaba yama wasu maza cikin masu aikin nuni akan su rik'eshi, su wajan biyar suka rik'eshi da kyar yanata k'okarin kwacewa. Wajan da Ummy take Saurayin ya k'arasa ya duk'a yace "Sannu tashi ki k'arasa ladanki" Kallanshi ta tsaya yi ya gyad'a mata kai ta mik'e tana rik'e da wuyan nata suka cigaba da rairo karatun alkur'ani a tare, chan gefe saurayin ya matsa ya soma neman Layin Abba, bayani ya masa sannan ya kashe ya kira Mami. Wani kukan kura Jamal yayi ya doke samarin dake rik'e dashi yayi kan Ummy, bata ankara ba taji ya d'auketa chak yayi wurgi da ita, wani razananen ihu ta saka a hankali ta sulale ta sume. Daddaneshi samarin suka k'arayi, duk hankalin saurayin nan baya jikinshi, kota kan Ummyn beyi ba sai safa da marwa dayake tayi a wajan, k'aran mota sukaji kan kace me masu aikin dake cike a wajan kowa yayi hanyarsa dasauri, Hankali tashe Abba ya shigo garden din shida wani dattijo, ganin halinda yake ciki yasa Abba ya karasa dasauri yana kokarin kama Jamal d'in, Dattijon ya dakatar dashi dasauri yamai nuni daya matsa, hawaye suka soma gangaro ma Abba ya matsa yana kallan d'an nasa. Ruwa dattijon yasa aka kawo mishi a wani bowl, addu'a yayi ya tofa yace samarin su sakeshi, suna sakeshi ya yunk'ura zai tashi Dattijon ya watsa masa ruwan a fuskansa da kirji, wani Ihu ya saki ya koma ya zauna har lokacin idanunshi a jujuye. Dattijon ya tsugunna gabansa yace "Wanene kuma me kake nema a jikinsa" Shiru yayi chan kuma ya soma wani irin ihu kamar na doki, Dattijon yayi murmushi yace "Kunaso ku nuna taurin kai koh? Idan bakuyi magana ba zan la'anta ku zan d'aidaita ku" Nan ma dai baiyi magana ba sai zare zaren ido dayake, Ana cikin haka Mami ta karaso wajan hankali tashe, ganin halinda d'an nata yake ciki yasa ta sulale ta zauna ta fashe da kuka. Dattijon nan kuwa ganin sunk'i magana yasa yayi gyaran murya ya soma karatu cikin k'ira'a mai dad'i, Nan ya soma ihu yana fizge fizge tareda Birgima a k'asa. Sun d'au lokaci a haka sannan yayi wani irin ihu yace "Ku tsaya zamuyi magana" Dattijon yace "Meyasa ka shiga jikinshi" Jamal yace cikin wani irin k'aton murya "Turomu akai dan mu kulle alak'ar sa, mu muka daki motarsa shekara uku da suka wuce mukayi anfani da wannan daman" Dattijon yace "Ka fita daga jikinshi sannan kaji tsoron mahalucin ka" Wani dariya Jamal d'ina yayi yace "Harkai ka isa kasa mu fita" Dattijon baice komai ba ya cigaba da karatun alkur'anin, Ihu ya cigaba ganin ba sarki sai Allah yace "Ka tsaya tsoho, ka daina k'onamu zamu fita" Dattijon yace "Maza ku fita sannan ku fita ta hanci" Atishawa Jamal d'in yayi sau uku sannan ya sulale baci mai nauyi ya d'aukeshi. Hamdala Abba ketayi ya k'araso ya tsugunna ya d'ago kan d'an nasa yana murmushin farinciki, "Allah na gode maka, Allah abin godiya" Dattijon yace "Alhamdulillah, sun fita sai a kiyaye" Ya kalli Abba yace "Zan turo akawo magani da zai cigaba da anfani dashi insha Allahu komai zai warware" Mami ta d'ago dasauri tana kallan Malamin "Yanzu Mallan lapia lau zai tashi ba wata matsala" Kai Mallamin ya gyad'a mata, ta fashe da kuka takai goshi k'asa taima Allah godiya. Godiya kam Mallamin nan yasha wajan Abba, kud'i masu yawa Abba ya basa yak'i karba yace yayi sadaka neh, nan suka k'ara masa godiya Abba yasa driver ya kaishi gida. Da taimakon Saurayin nan Abba ya d'au Jamal d'in suka d'aurasa kan Wheel chairn, sai a sannan idanunsu ya sauka kan Ummy dake kwace achan gefen Garden d'in kanta na fitarda jini. Abba hankali tashe ya nufeta shida Mami yana cewa "Ramadan garin yaya haka ta faru" Bai iya cewa komai ba ya d'auketa chak yana cewa "Tana bleeding akai, ka kira doctor Abba" Cikin gida yayi da ita, Mami ta gunguro Jamal ta shiga ciki tashi Abba kuma ya soma neman layin doctorn. Ummy Abduol✍🏻 [3/11, 8:30 PM] Alion Bagari: ♠♠♠♠♠♠♠♠ ♠♠♠♠ *JAMALUDEEN* ♠♠♠♠ ♠♠♠♠♠♠♠♠ By *Ummy Abduol* Dedicated to My *Late Siblings* ``` Ina kuke JAMALUDEEN FANS group Wannan shafin naku neh. Kuna bani farinciki sosai, ina godiya buhu buhu ``` Page 18 Cikin gida yayi da ita, Mami ta gunguro Jamal ta shiga ciki dashi, Abba kuma ya soma neman layin doctor. Mami tama Ramadan nuni da d'akin Ummyn, ya shiga ya shimfid'eta kan gado yana kallanta, sosai kanta ke fitar da jini, yasa wani zaninta dake kan gadon ya tare jinin gabanshi na fad'uwa. Bayan kamar minti goma sha biyar likitan ya k'araso gidan, bashi guri yace Ramadan yayi shi kuma ya shiga dubata. Mami da Abba suna bakin k'ofan chirko chirko cikeda zullumi, a haka Mabrookah ta shigo gidan ta samesu, tambayan abinda ya faru tayi Mami ta mata bayani cikeda damuwa. Likitan ya d'au lokaci kamin ya fito ya samu Abba nan bakin k'ofan, Mami ce tai saurin k'arasowa itada Ramadhan, likitan ya kalli Abba yace "Da sauki Alhamdulillah, saidai ta bugu sosai a kanta sannan ta samu karaya a hannunta na hagu" Mami ta saki sallati tana duban likitan "To yanzu wani hali take ciki doctor?" Cewar Ramadan Likitan ya cigaba da cewa "Na mata allurar bacci saboda yanayin da take ciki, but idan so samu ne da an kaita asibiti idan ta farka saboda ai mata xray ko akwai wata matsala" Ramadan ya mik'a masa hannu sukayi musabaha
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82