Skip to content

Chapter 27

Chapter 27

Jamaluddeen Book One Complete Hausa Novels 1,197 words 0 views Progress saved
Download Book

layin Ramadhan anma switch off. Yana nan d'aki har Abba ya dawo, direct side d'inshi ya nufa yayi sa'a ya sameshi shi kad'ai, zama yayi ya soma ma Abban bayani, bai b'oye masa san da yakema Ummyn bah. Sosai Abba yaji dad'i duk da shima hankalinshi ya tashi dajin maganan auren da akeso ama Ummyn. Washe gari da wuri Abba ya nemi aminan sa suka tafi gidansu Ummyn nema ma Jamal aurenta. Baba Sallau da Baba Tanko fafur suka k'i yarda, duk magiyan da suka musu suka ce sam, haka suka hak'ura suka dawo gida a sanyaye. Ummy batasan wainar da ake toyawa ba dan dama bata sanar da Jamal d'in abinda Mama tace ta fad'amai ba, kawai da ta fad'amai abinda su Baba Sallau d'in suka cene. Washe gari ranar bakwai, Ummy kuka take kamar mai hauka, Mama itama na tayata, Alumma ne cike a k'ofar gidan ana addu'an bakwai. Da gudu ya shigo cikin layin kamar zai tashi sama, yana parking a ya fito aka shafa fatihar k'arshe na d'aurin auren Ummyn. Hannu ya d'aura aka ya fad'i guyawu biyu a k'asa tareda fashewa da kuka. *Idan banga dogon comment ba, bazan cigaba ba ehe!* Ummy Abduol✍🏻 ♠♠♠♠♠♠♠♠ ♠♠♠♠ *JAMALUDEEN* ♠♠♠♠ ♠♠♠♠♠♠♠♠ By *Ummy Abduol* Dedicated to My *Late Siblings* *Oh! Fans duk saurin ungwazo ma ta bari dai a haihu koh! Naga comment d'inku, masu addu'a ina godiya, masu k'orafi ma na gode, masu zagi suma na gode dan bazance ban gode bah.* _Aysha Humaira (Aunty Nurse) ina tayaki murnar zagayo war ranar haihuwarki. Allah ubangiji ya k'aro shekaru masu albarka, ya nuna min aurenki mu kwaso shoki Lol_ Wannan shafin sadaukarwa ce gareki K'awar arzik'i Page 31 Hannu ya d'aura aka ya fad'i guyawu biyu a k'asa tareda fashewa da kuka. Ganin kukan nasa ba ci yasa ya mik'e ya shiga cikin gida kai tsaye, Inna dake tsakar gida tana shara ta d'ago dan taga mai shigo mata gida ba sallama, ba shiri tsintsiyar hannunta ya fad'i ta dafe k'irji tana sallati "Bi...Bilal! Kai nake gani ko gizo kakemin" Ya soma takowa a hankali yana share hawayen fuskansa, "Ni ne Innata" Ya mik'a mata hannunshi "Tab'ani kiji" Cikeda tsoro ta mik'a hannunta ta tab'a shi, ba shiri ta fashe da kuka, shima kukan ya soma ya jata suka zauna kan tabarman dake tsakar gidan "Bilal ina ka shiga duk lokacin nan, meyasa ka tafi ka barmu bayan kasan bamuda kowa daga Allah sai kuma kai" Kuka ya sake fashewa dashi kamar k'aramin yaro tareda rik'o hannun Innan, Bahar ne ya shigo gidan yana k'walawa Inna k'ira, ba shiri ya koma waje a guje yana Ihu, Inna ta soma magana tana cewa "Munyi ta jiranka ba wani labari, har tsawon sati uku, sannan Bahar da Ummy suka je nemanka inda kuke aiki, a nan muka samu labarin kunyi hatsari kun mutu" Ya sake kama hannun Innan yace "Tabbas munyi hatsari, saidai kafin motar ta kama da wuta Allah ya aiko mutane inda suka ciro ni ganin ina motsi, wani Alhaji ne ya d'auke ni ya tafi dani abuja, kasancewar ba mazaunin k'asan nan baneh yasa lokacin komawar sa nayi ya d'aukeni ya tafi dani Egypt, k'asar dayake kuma a lokacin bana cikin haiyaci na dan ban farfad'o bah" Ya sake sharb'e hawayen idonsa yace "Na d'au watani bansan inda kaina yake bah sai daga baya na dawo cikin hankalina. Alhajin da matarsa sunyi d'awainiya dani sosai har zuwa wani lokaci. Dawowan mu k'asar kenan shekaran jiya shine na taho gida. Inna ba abinda take sai sharb'ar hawaye "Allah sarki mutanen kirki" Duk abinda suke tattauna wa Bahar na jinsu wanda ke bakin zaure yana lek'ensu. Bayan yaji bayanin sa ya shigo ya zauna kusada yayan nasa tareda rungumeshi "Yaya munyi kewarka sosai, badan Ummy data fara aiki tana taimaka mana ba da bansan halin da zamu shiga ba" "Aiki!?" Bilal ya maimaita yana kallan Bahar, Inna tace "Kwarai kuwa" Nan ta soma basa labarin abinda tasani har zuwa yau da ake sadakar bakwai na Baba, kuma ranar da aka d'aura auren Ummyn. Hawaye ne suka gangaro masa na tausayin halin daya bar 'yan uwansa da kuma Ummyn. Baice musu komai ba saima mik'ewa dayayi ya fita, gidansu Ummyn ya shiga kai tsaye, mutane ya gani a ciki, bin gidan ya soma yi da kallo ganin yanda aka gyara shi tareda k'awata shi sosai. Falon ya shiga da sallama ya hango Mama zaune a k'asa gefen kujera, ta d'aura kan Ummy bisa cinyarta wacce da alama kuka take. Jiki a sanyaye ya k'araso ya tsugunna gabansu "Sannu Mama" Muryan da Ummy taji ne yasa ta d'ago a razane suka had'a ido da Bilal, ba shiri ta fashe da wani sabon kukan, Mama ko tsoro taji ta d'an matsa "Bilal! Kaine" "Ni ne Mama, ban mutu ba" Ummy ta mik'e dasauri tabar d'akin tana cigaba da kuka, zaure ta nufa yayi saurin fitowa ya kamo gefen hijabinta dasauri "Ina zaki Hrt, pls ki tsaya ki saurareni" Cikin kuka ta d'ago idanunta tana cewa "Ina katafi Ya Bilal, ina kaje ka barni, meyasa ka tafi baka waiwayo ni bah. Dama nasan baka mutu ba dan naji a jikina." Ta chakume shi tana wani irin kuka mai cin rai "Kai kad'ai nakeso Ya Bilal, kai nakeso na aura. Gashi kasa an aura min wanda banaso. Meyasa Ya Bilal" Shima hawayen ya soma "Nasan nayi kuskure Hrt, anma yakamata ki tsaya ki fahimceni kafin ki yanke hukunci" A hankali ta zame hannu wanta daga rik'on data masa tana kuka. Labarin abinda ya faru dashi ya soma bata tiryan tiryan, sassauta kukan datake tayi "Yannin babana sun aura min wani wanda banaso, wanda banma tab'a ganinsa bah" Gabansa ya fad'i, ya d'ago rinannun idanunsa yana kallanta, Baba Sallau ne ya shigo zauren, ganin Ummy tsaye da wani wanda bai sani ba yasa ya soma fad'a "Ke Ummy, yanzu saboda iskanci da rashin hankali a d'aura miki aure ki tsaya kina kula wani" Ya daka mata wata uwar tsawa "Maza bar nan!" A guje ta shiga cikin gida tana kuka, ya juyo ga Bilal dake tsaye kamar gunki "Kai kuma zaka bar nan ko sai na bugeka" Jiki a sanyaye ya bar zauren ya koma gida. D'akin Innansa ya shiga ya soma kuka wui wui, dan harga Allah bazai iya rayuwa ba Ummy bah. ****** Bayan an gama d'aurin aure Abba ya baro wajan ya dawo gida, Jamal ya tarar a falonsa kishingid'e kan kujera idanunsa a lumshe, har ya nemi guri ya zauna kusada shi bai sani bah. Gyaran murya Abban yayi anma shiru, kai ya girgiza ya d'an buga hannunsa, bud'e ido yayi ganin Abba yasa ya mik'e zaune dasauri yana kallanshi "Jamal tunanin me kake?" Yayi saurin girgiza kai tareda k'ago murmushi yace "Bakomai Abba, bacci nakeyi" Murmushi Abba yayi irin tasu ta manya, ya gyara zama tareda cire babban rigan dake jikinsa "Meya hanaka zuwa addu'an bakwai" Ya sosa k'eya yana kame kame "Ahan kai nake sauraro" "Ummm..mmm Dama Ramadhan nayi ta jira muje tare kuma baizo bah" Murmushi Abban ya sakeyi, "Bakomai ai tunda ni naje, na wakilce kah. Yanzu abinda nakeso dakai shine ka shirya dan nan da sati d'aya za'a kawo maka matarka" Da mamaki Jamal ya

Table of Contents

Chapters

82 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82