Skip to content

Chapter 17

Chapter 17

Jamaluddeen Book One Complete Hausa Novels 1,199 words 0 views Progress saved
Download Book

Ramadhan yayi shida Laurat, shi kuma gogan murmushi kawai yayi yana cigaba da kallan Ummyn. Ramadhan yace "Ka mata uzuri bata sami baneh, kuma kaga tasamu buguwa akai kila ta samu matsala neh" Maganan Ramadhan ya sosa mata zuciya, wato kenan ya d'auketa mahaukaciya ma kenan, idanunta cikeda kwalla ta d'ago tana kallan Jamal "Ni ba mahaukaciya bace da hankalina" Ta fashe da kuka tace "Kuma ai bansan ka warke baneh shiyasa ka bani tsoro. Ta sake d'agowa tana kallan Jamal wanda shima ita ya zubama ido "Ni ban kiraka da wannan sunanba sai ku ne zaku kirani da mahaukaciya" "No bah haka baneh baki fahimceni baneh, I'm sorry ba haka nake nufi ba believe me" Cewar Ramadhan cikin tattausan murya. "Nagode Laurat, har dake aka had'u ana zagina bakomai" Ta kwanta kan gadon ta janyo blanket ta rufe jikinta har kai tana cigaba da kuka. Tab'o Jamal Ramadhan yayi "Say something mana" Guntun tsaki yaja ya mik'e ya kama hannun Ramadhan d'in suka fito daga d'akin. Jamal ya saki Hannunshi yana cewa "Kaifa Matsalata dakai kenan bakin ka baida control" "Eh naji bakina ba control, kai kuma idonka da shegen gulma, tun dazu kaketa kallan musu 'ya" Dukan wasa Jamal ya kaimai yana dariya "Kai kaidai Ram ta shiga uku" Laurat ta fito daga d'akin Ramadhan ya tab'o Jamal suka juyo suna kallanta "Dama inaso ne naje gida na d'auko mata kayan da zata chanza" Ramadhan yace "Taci abinci neh" ta girgiza kai alamar A'a "Tak'i taci tayi fushi sai kuka take" Shiru ne ya biyo baya, Ramadhan yace "Yanzu muje ki d'auko kayan mu dawo" Gaba tayi Ramadhan ya tab'o Jamal yana y'ar dariya "Na barka da ita ka lallasheta kasan kai na mata neh" Bai jira mai Jamal d'in zaice ba yabar wajan dasauri yana masa dariya. Jim yayi yana tunanin yanda zai shiga d'akin dan shifa bai iya magana da mace ba dan shi a rayuwarsa ko budurwa bashida. Handle d'in ya murd'a ya shiga da sallama ciki ciki, zaune ya saketa ta jingina da pillow idanunta a lumshe, kan kujeran gabanta ya zauna yayi shiru yana kallanta a hankali yace "Ummy" Batace komai bah kuma bata bud'e idon ba saima turo baki datayi ta juya kai gefe, murmushi yayi mai sauti yana shafa sajen fuskansa "Kiyi hak'uri da abinda Ram ya fad'a dazu, ba ya fad'a baneh dan ranki ya b'aci" Shiru ne ya biyo baya na y'an mintina ya cigaba da cewa "And kiyi hak'uri akan abinda ya faru jiya, i wasnt my self har naji miki wannan raunin. And ina godiya da lokacinki da k'arfinki da kikayi wasting wajan lura dani" A hankali ta bud'e ido tace "Bana buk'atar godiyanka" Ya saki murmushi mai sauti yace "Ok! Ok!! But kiyi hak'uri pls akan abinda ya faru" "Na hak'ura" ta bashi amsa a takaice. Shiru ya sakeyi har lokacin idanunshi na kanta, kujeransa ya matso dashi kusada ita sosai yace "Dan Allah na miki wata tambaya mana" "Ina jinka" Ya shafa suman kanshi yace "Anma dai lokacin da banda lapia baki tab'a min wanka ba koh" Kuji min Jamal d'in nan fah Fans...Haha Ummy Abduol✍🏻 [3/12, 8:20 PM] ‪+234 703 981 8283‬: ♠♠♠♠♠♠♠♠ ♠♠♠♠ *JAMALUDEEN* ♠♠♠♠ ♠♠♠♠♠♠♠♠ By *Ummy Abduol* Dedicated to My *Late Siblings* Page 21 "Anma dai lokacin da banda Lapia baki tab'a min wanka ba koh" Maganansa sosai ya bata d'ariya, dakyar tayi k'okarin dakewa tana kallansa k'asa k'asa "Wanka na nawa kuma" Ta tab'e baki tace "K'arshen magana ma jiya ni na maka wanka" Mutuwar zaune yayi yana kallanta fuska a had'e, anma dai an gama cutar shi wallahi. Dogon tsaki yaja ya mik'e yana hararanta rai b'ace yana nuna kanshi, har ya bud'e baki zaiyi magana Mami ta turo k'ofa ta shigo, ya juyo dasauri yana kallanta har lokacin fuskanshi a had'e "Mami yanzu abinda akamin an kyauta knan?" Da mamaki Mami ta kalleshi ta juya ga Ummy tana kallanta "Me kuma aka maka?" "A rasa mai min wanka sanda banda lapia sai wannan?" Ya nuna Ummy fuskan nan nasa a had'e Mami da Ummy suka kyalkyale da dariya a tare "Ai Ummy tayi d'awainiya dakai sosai, wankan ka, wankin ka, kai hatta toilet idan kayi ita..." "Haba Mami! Habaaaaa" A fusace yabar d'akin yayi waje, Mami ta sake kyalkyalewa da dariya, "Allah ya shiryeka Jamal" Itama Ummyn dariya tayi, Mami ta mata sannu tana cewa "Nace ma dr ya sallameki ki koma gida sai a rink'a zuwa ana dubaki achan" Godiya tama Mamin, su Ramadhan suka shigo shida Laurat "Mami meh akaima Jamal ne naganshi yanata kumbure kumbure a waje" cewar Ramadhan. Mami ce ta fad'amai abinda ya faru, yayi dariya yana kallan Ummy "Oh kin rama knan" Harara ta wurga mai ta kauda kai gefe. Likitan da kansa ya kawo musu takadar sallama bayan ya k'ara dubata tareda rubuta mata magunguna. Laurat da Ramadhan suka kwaso kayan da aka kakkawo, Mami ta rik'o Ummy suka fito. A haraban asibitin suka had'u da Jamal sai cika yake yana batsewa, kallo d'aya Ummy tamai tayi dariya, harara ya zafga mata tareda kauda kai. Suna isa ya d'au wayan Ramadhan ya kira Layin Abba, saida ya tambayesa ya fad'a masa gaskiya sannan hankalinshi ya kwanta. Kiran ya kashe tareda sauke ajiyar zuciya "Lallai ma Yarinyan nan" Yayi k'wafa yace "Kinci bashi" K'in saukowa yayi k'asa shi a dole yayi fushi, yayi zamanshi a d'aki abinshi yanata bacci. Washe gari da safe Ramadhan ya koma Kaduna, hakan baima Jamal dad'i bah dan shi ke d'ebe masa kewa sbda har yanzu Abba yak'i yarda ya fita zuwa wani guri shi kad'ai. Ummy na zaune a d'akinta, duk hankalinta nakan Iyayenta gashi har weekend yazo ya wuce bataje ba kuma tasan suna chan hankalinsu tashe dan idan har zata jima takan fad'a musu. Laurat dake gefenta ta d'ibo abinci a plate, shinkafa da miyan naman rago sai salad, d'iba tayi takaima Ummyn baki dan bata iya cin abincin da kanta, ta kauda kai gefe idanunta cikeda kwalla "Ummy ci mana, tun safe fa Bakici abincin kirki bah" "Bazan iya ci bah, bansan halinda Iyayena ke ciki bah yanzu nasan hankalinsu nachan a tashe" "Haba ki kwantar da hankalinki, ai Mami tace yau ko gobe za'a kwance d'aurin kanki. Kinga hannu ma bazai jima ha knan" Gigiza kai kawai Ummyn tayi, dakyar Laurat ta lallab'ata tad'anci kad'an sannan ta koma bakin aikinta ta barta ta huta. Harta kwanta aka turo k'ofan d'akin, bata d'agoba dan a tunaninta Laurat ce. Kujera akaja aka zauna har lokacin ba'ayi magana bah. Jin shirun yayi yawa yasa ta d'ago suka had'a ido da Jamal, ya harareta yana cewa "Ke baki Iya gaisuwa bah" Fuska ta yatsine ta kauda kai gefe tace "Ina wuni" "Dah ban wuni ba zaki ganni" "Oho kai za'a tambaya" Buge mata baki yayi tasa hannuta na dama ta rik'e bakin tareda fashewa da kuka "Allah ya..." Rank'washin ta yayi a kai ta saki kuka tana sosa inda ya rank'washetan. Fuskansa ya matso dashi kusada nata yana kallan k'wayar idonta "I'm a free guy, kowa nawa neh, but banasan rashin kunya" Yayi murmushi yasa hannu ya shafa gefen fuskanta "Na lura bakida kunya, kuma gashi ni bansan rashin kunya" Ya saki murmushi mai sauti "From

Table of Contents

Chapters

82 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82