Chapter 71
Chapter 71
kansa Alhaju Ameenun Yanayin fuskansa ne ya sauya, anma ya dake yace l "Wani irin magana kakeyi neh?, me kake nufi" Ammi tayi saurin cewa "Areef kaine?" Areef ya zaro ido yana kallan Ammi da mamaki, Ram wanda ya gane inda maganar tasu ta dosa ya k'araso yana cewa "Wannan maganan ba'a nan yakamat ayita bah, ya kamata a natsa sai a zauna a tattauna" Ya mik'ar da Jamal tsaye, Mifzal yace "Alhaji ku shiga mota kubi bayanmu muje a tattauna a gida" Ba musu suka shishiga mota Jamal ya shiga nasa motan, Ram ne ke driving har zuwa gidansu Jamal. Suna isa Jamal ya musu Jagora zuwa side d'in Abba. Bayan an zazzauna ya koma cikin mota ya d'auko akwatin nan ya shigo dashi d'akin, Ammi na gani ta mik'e tsaye dasauri tana bin akwatin da kallo. Haka shima Alhaji zazzare ido yayi yana kallan akwatin, Areef da Bilal da kuma su Mifzal gaba d'aya bin su Abban suke da kallon Mamaki, Alhaji yayi k'arfin halin cewa "Ina ka samu akwatin nan" Jamal bai b'oye musu komai ba dangane ga abinda ya sani, Ammi ta fashe da kuka tana cewa "Na dad'e ina burin ganin wannan ranar gashi Allah ya kawoshi" Areef ya kalleta da Mamaki "Ammi kun sakani a duhu meke faruwa neh" Alhaji wanda shima k'walla ke zuba a idonsa yace yana nuna Jamal "Wannan yayanka neh, mu muka haifesa, sunansa kaci bayan mun rasa shi da muka haifeka muka maida maka da sunansa" Jamal dake gefe shima yana hawaye yace "Ammi meyasa kuka yar dani, baku damu da halin dazan shiga bah, baku damu da mai zai iya samu na a daran da kuka yardani bah" Ya fashe da kuka sannan ya cigaba da cewa "Ance tsakanin d'a da uwa akwai wata irin shak'uwa mai tsanani, meyasa Ammi kika yarda aka yardani, kuma baku k'ara waiwayan halinda zan shiga bah" Abba ya girgiza kai yana share hawayen dake gangaro masa "Ba laifin mu baneh Areef, ba laifin mu baneh" Haryanzu binsu da kallo Areef keyi cike da mamaki da kuma kokwanto, Alhaji ya soma magana cikin raunin murya "Sunana Alhaji Ameenu Jibril, ni haifafen Garin karaye ne dake Kano. Na taso cikin gata na iyaye kasancewar mahaifina hamshak'in attajiri ne a wanchan lokacin, nayi ilimin Addini dana boko sosai, ana haka iyayena suka rasu duka, hakan yasa na dawo garin kaduna da zama, inda na had'u da Hajiya zainab na aureta, cikin ikon Allah na fara sana'ar saida gwal da taimakon wani ubangidana danayi zuwana Kaduna" Ya sauke ajiyar zuciya sannan ya cigaba da cewa "Harkokin kasuwanci ya cigaba da bud'ewa, ina samun Alkahiri da dama haka ina samun cigaba a harkata, har nakaiga inacin gashin kaina nima inada yara, tunda sauran mutanen da muka fara sana'ar tare sukaga haka suka soma mini bak'in ciki, a haka na cigaba da sana'ata, na tara k'addara masu yawa, na gina gida na gani na fad'a. Ana haka matata ta haifeka inda muka saka maka suna Areef" Areef dake gefe ya zaro ido yana kallan Alhajin, Bilal ko k'uri ya musu shida Jamal tabbas ga kama nan da sukeyi da juna, haka kuma suna yanayi da Alhajin, ya cigaba da cewa "Ina sanka Areef fiyeda yanda nakesan kaina, dan kai ka zamo mini a matsayin 'yan uwana dana rasa, duk wani kula da jin dad'i nida matata munayi maka, ana haka wata rana da daddare wuraren k'arfe biyu na dare, mukajiyo shigowan b'arayi gidan, Sosai mukaji tsoro, Matata banda kuka babu abinda take, sunyi sunyi na bud'e k'ofa nak'i, a nan suke shaida min ba kud'i suke nema ba raina dana Matata dana d"ana suke nema, inajin mata jikina dana matata ya soma rawa, da kaina na sakaka a akwati na saka dukiya mai yawa a ciki, na mik'ama matata nace su gudu, ta k'ofar baya suka gudu ni kuma na sadak'ar nazo na bud'e musu k'ofan. Ganin ba iyalina yasa ransu ya b'aci suka sakar min harbi Allah ya taimakeni a Hannu neh, suna ganin na fad'i sukayi tafiyarsu" Ammi na kuka ta d'aura da cewa "Mun fita nayita gudu ina kuka, har Allah ya had'ani da wani mai mota inda ya sanar dani Zaria yayi, ba yanda na iya hakanan na bisa ya saukeni a wani anguwa nayi ta masa godiya dan bai amsa ko sisina bah, haka na kwana a wajan wani bola har washe gari da safe, na yini banci komai bah, da daddare yunwa ya addabeni dole na maidakai cikin akwatin dan bazan iya d'aukanka saboda jikina daba k'arfi, a nan na barka na tafi neman abinci, kafin na dawo an d'aukeka a wajan" Ta k'are maganan cikin kuka, Ram dake gefe yace "To ya akayi kuka had'u da mijinki" Ta share hawayen fuskanta tace "Nayi rayuwa a zaria na kusan shekara d'aya inayi ma wata mai abinci bauta, sannan daga baya na koma Kaduna wajan Iyayena inda anan na sake had'uwa da Mijina ashe yanada sauran kwana" Mifzal dake gefe ya tab'e dan gaba d'aya labarin akwai ganganci da rashin dabara a cikinsa. Ummy Abduol✍🏻 🖤🖤🖤🖤🖤🖤🖤🖤 🖤🖤🖤🖤 *JAMALUDEEN* 🖤🖤🖤🖤 🖤🖤🖤🖤🖤🖤🖤🖤 By *Ummy Abduol* Dedicated to My *Late Siblings* *Fcbuk Page* https://facebook.com/Ummy-Abduol-Novels-1033022590196192/ Page 88 Mifzal dake gefe ya tab'e baki dan gaba d'aya labarin akwai ganganci da rashin dabara a cikinsa. Alhaji Ameenu ya zamo daga kan kujeran dayake ya xauna a k'asa yana kuka a hankali "Tun dawowar Zainab danaji labarin b'atanka daga wajanta, babu irin kukan da bamuyi bah da nemenka anma babu wani labari, Wallahi Areef dakai kullum nake kwana a raina har Yau, kullum ina addu'ar ganinka dan a kullum inaji a jikina kanada Rai" Ammi cikin kuka tace "Ka gafarce mu Areef sam bamu yarda kai bah" A hankali ya rarrafa shima yana kuka ya rungume Abba yana kuka a hankali "Ka daina kuka Abbana, bakumin komai bah." Ya juya zuwaga Ammi itama ya rungumeta ya saki wani kuka mai sauti tare da ajiyar zuciya, Babu wanda baiyi k'walla a wajan bah, Ya saki Ammi da Abba yayi sujada yana mai godiya ga Allah. Hannu ya bud'ema Areef k'arami ya k'arasa ya rungumesa ya saki kuka yana cewa "I'm so sorry Bro been so Rude" Jamal ya girgiza masa kai yana share masa hawaye "Its Ok" Mifzal yayi gyaran murya yace "To Alhamdulillah Allah muna godiya daka kawomu wannan rana" Ya kalli Jamal yace "Ina tayaka Farinciki da ganin wannan rana, ranar da kaga Iyayenka na asali." Jamal ya mik'e zumbur yace "Ina zuwa pls" Bai jira mai zasuce ba yabar Falon dasauri, side d'inshi ya shiga ya samu Mabrookah zaune ta zabga tagumi, ya k'arasa tare da kamo hannunta, firgigit tayi ta d'ago tana kallansa, murmushi ya mata itama ta mayar masa "D'auko Hijabinki ina zuwa" Ya haura dasauri zuwa sama, d'aki ya samu Ummy tana bacci wanda yanzu ya zaman mata k'aida kullum da rana sai tayishi, hura mata iska yayi a kunne tare da kai mata kiss a bakinta, tad'an bud'e ido a hankali tana kallansa "Baeby tashi kiji" Ta turo baki ta k'ara lumshe ido "Bacci fa nakeyi" Shima ya shagwab'e fuska yana tura baki "Yanada mahimmanci neh" Dakyar ya lallab'ata ta tashi ya d'auko mata hijab tasa suka fito, Mabrookah na nan falonta tana
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82