Chapter 25
Chapter 25
kaduna ya nufa direct wajan Ramadhan dan maganar bata waya bace. K'arfe bakwai na safe daidai yayi horn a k'ofar gate d'in gidansu Ramadhan, Mai gadi ne ya bud'e masa ya shiga ya samu guri yayi parking, Ramadhan d'in ya soma nema a waya, cikin muryan bacci ya d'auka Jamal yace "Dallah ka fito ina k'ofar side d'inka" Ba shiri Ramadhan d'in ya mik'e, daga shi sai boxers da singlet ya fito haraban gidan da mamaki "Anma a hanya ka kwana koh" Jamal ya harareshi "Kaifa matsala ce dakai, Aa ka manta tun wachan shekaran nake hanya" Ramadhan ya fashe da dariya yana girgiza kai, side d'in Ramadhan d'in suka Shiga, bayan sunyi breakfast Jamal ya zaiyane wa Ramadhan duk abinda ke faruwa, dan bayada abokin daya wuce shi. Saida Ramadhan ya sauke ajiyar zuciya sannan yace "Tho yanzu kai ya kakeso ayi?" "Bangane ba Ram, Wallahi inasan Ummy so mai tsanani, kai kasani banda wata budurwa balle kace ko yaudaranta zanyi. Ni yanzu abinda nakeso ayi shine muje dakai ko Allah zaisa ta saurareni sai na bata hak'uri" "But Jamal, a yanda na fahimta kamar yarinyan nan bata sanka, meyasa zaka shiga inda ba'a buk'atarka" "She need me Ram, yarinyan da parents d'inta suna buk'atar taimako, Hmm dan baka zauna da ita baneh, Wallahi tayi ta kowane fanni" Ramadhan ya saki dariya yana girgiza kai "Kaifa d'an iska ne Ram, ya ina maka magana kana maidani wani abin dariya" Wani dariyan ya kuma yi, yana cewa "Ai naga abin naka neh naso ya wuce guri, harda wani ta had'u ta kowani fanni" Jamal ya b'ata rai, ganin haka yasa Ramadhan mik'ewa yana cigaba da dariya ya shiga bedroom d'insa. Wanka yayi ya sauyo cikin manyan kaya yana kallan Jamal "Anma dai ba haka zaka gidan sarakan naka ba kawani ci uban zanzaro, ka tashi ka shiga bedroom d'ina akwai kaya kan gado" Saida ya harari Ramadhan d'in sannan ya mik'e ya shiga d'akin ya chanzo zuwa kaftan, sid'e d'in Iyayen Ramadhan d'in suka ya gaida su sannan suka sake d'aukan hanyan zaria. Jamal ne ke driving motan har k'ofar gidansu Ummyn. Shiru dukansu sukayi Jamal ya sauke ajiyar zuciya tareda maida dubansa ga Ramadhan "Ta ina zamu fara?" "Muje mu nemi yaro ya mana sallama da ita" Jamal ya saki malalacin murmushi yana girgiza kai. Ramadhan ya fita daga motan, wani almajiri ya samu ya aikashi ya mai kiranta sannan ya idan ya tambaye shi waye yace Jamal neh. Tana zaune a falo tana tunani Mama na gefenta tana mata fad'an k'in cin abinci datayi, Almajirin ya shigo da sallama ya tsugunna bakin k'ofan ya isar da sako, Ummy tai saurin cewa "Kaje kace bazata zo bah" "Haba Ummy, meyasa haka? Ai ba shi ya miki laifi bah. Kije kiji mai zaice" Ta zunguro baki ta mik'e tad'au hijabinta ta fito, a bakin k'ofar gidan ta toge fuskanta had'e. Kallo d'aya Jamal ya mata yaji gabanshi ya fad'i, jiki a sanyaye ya fito daga motan suka k'arasa shida Ramadhan, "Salamu alaikum" Ramadhan yace yana murmushi Bata amsa ba saima juya fuskanta datayi gefe d'aya "Haba Ummy ai laifin wani baya shafan wani. Ko ba komai yakamata ki amsa sallama nah" Ta sake kauda kai gefe sannan ta amsa "Naji duk abinda ya faru kuma banji dad'i bah. Saidai ina rok'onki karki sa abin a ranki. Kiyi hak'uri da duk abinda ya faru" Hawaye suka cika mata ido tana kallan Ramadhan "Idan kai akayi ma abinda aka min zakaji dad'i? Talauci ba hauka baneh. Tunda nake ban tab'a sata bah haka iyayena, anma aka kirani da iyayena b'arayi" Ta rushe da kuka tasa hijab d'inta ta rufe fuska tana cigaba da kuka. Shidai Jamal ba halin magana saima ransa dake suya "Nasani an miki laifi, anma kiyi hak'uri" Ta d'ago dasauri tana kallanshi "Hak'uri? Inyi hak'uri fa kace?" "Allah muna masa laifi ya yafe mana balle mu y'an adam, karki zama d'aya daga cikin masu bin kururuwan shaid'an. An miki laifi kuma ba'a kyauta miki bah, Anma kiyi hak'uri. Kada ki yanke zumuncin dake tsakanin ki da Jamal Pls" Shiru tayi batace komai ba sai hawaye datake gogewa. Jamal ya d'ago kai yace "Pls Ummy badan niba, nasan harda laifina a ciki, anma kiyi hak'uri." "Shikenan komai ya wuce" Bata jira mai zasu ce ba tayi shigewanta gida. Ramadhan ya mik'ama Jamal hannu sukayi musabaha "Shikenan na gama nawa koh" Kai Jamal d'in ya gyad'a yana murmushi. Ranar a gidan Ramadhan ya kwana washe gari yasa driver ya maida shi gida. A ranar Jamal ya d'au su twins ya kaisu gidan su Ummy, tayi murna sosai da ganinsu dan tasan ba laifinsu cikin abinda aka mata, suma sun bata hak'uri dasu Mama, sun d'an jima a gidan sannan Jamal ya dawo ya d'aukesu Ya maida su gida. Da fad'a Mabrookah ta tari su Twins tana tambayan daga ina suke, Jamal na jinta ko kallanta baiyi ba ya bar wajan zuwa side d'in Abba. Har suka shiga falo tana balbalesu da masifa, Aunty Faty ce ta soma tambayan mai ya faru, Mabrookah ta soma magana tana cewa "Tun d'azu nake neman su ashe sun fita neh da Jamal, kuma bayan na fad'a musu zamuje wani guri dasu" Aunty Faty ta had'e rai tace "Daga ina kuke?" Batare da wani d'ar ba Najma tace "Daga gidansu Ummy, muje bata hak'uri" Wayan Hannun Mabrookah ne ya fad'i ta saki baki tana kallansu "Daga gidansu Ummy? Uban wa ya kaiku" Najwa tace "Ya Jamal" Nan Aunty Faty ta soma masifa, ta inda take shiga ba tanan take fita ba, Mabrookah ko side d'in Abba ta nufa a fusace, kishingid'e ta sameshi kan kujera idanunsa a lumshe, "Ya Jamal! Jamal!" Bai bud'e idonsa ba saima gyara kwanciya dayayi "Nasan dai kana jina, akan wani dalili zaka d'au Twins ka kaisu gidansu matsiyaciyar yariny...." Marin dataji a kuncinta ne ya hanata k'arasa maganan datayi niya, ya mik'e a fusace yana nunata da yatsa "Kinyi na farko kinyi na k'arshe, wallahi kika sake zagin Ummy sai na lahira ya fiki jin dad'i. Kar kiga kina abinda kika gadama ina saka miki ido, taraki nakeyi, kuma wallahi ko mutuwa zakiyi bazan aureki bah" Ta tushe da kuka tana nuna kanta "Akan wata banza zaka..." Wani marin ya sake d'auketa dashi "Fita! Kafin na la'anta ki" "Wallahi bazan fita ba koda kasheni zakayi, akan wannan yarinyan zata dukeni? Me ta fini dashi? Diri ko meh, ko dan ni bak'a ce. Wallahi saina aureka" Duka ya rufeta dashi dan dama yana ciki da ita, ihu ta dunga yi ba mai kwace ta, haka ya mata ligi ligi yabar side d'in. Saida tayi kuka mai isarta sannan ta koma side dinsu, Mami ta samu a falo itada Aunty Faty, ta shigo ta fad'a jikin Aunty faty tana kuka tareda labarta mata abinda ya faru. Ran Aunty Faty ya sake b'aci tace "Maimuna idan bazaki d'au wani mataki ba zan d'au 'yata nabar miki gidan, akan me d'anki zai kamata yayita jifga kamar ya samu jaka, ai ba shi kad'ai bane Namiji" "Ni Mommy ba inda zani, ina sanshi" Hak'uri Mami ta soma ba Aunty Fatyn dakyar ta samu ta shawo kanta, a ranar Jamal yaga b'acin rai wajan Mami anma hakan
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82