Skip to content

Chapter 66

Chapter 66

Jamaluddeen Book One Complete Hausa Novels 1,203 words 0 views Progress saved
Download Book

kuka take da ihu tana dafe k'afarta. Asibiti Ram da wani d'an sanda sukayi dasu Jamal, ba b'ata lokaci aka amshesu tare da basu taimakon gaggawa. Cikin awa da bai wuce d'aya ba Jamal ya farka tare da mik'ewa zaune. Ram dake kusa dashi yayi saurin rik'esa yana masa sannu "Ram ina Ummyna" Shine Farkon Abinda ya furta, cikin kwantar da hankali yace "Tana lafiya lau, ka kwanta ka huta" Ya fizge jikinsa yana k'okarin mik'ewa "I want to see her Pls" Ya sake maidasa zaune yana lallashinsa "Bazan iya zama batare da naga Wife d'ina bah. Dan Allah ka kaini na ganta hankalina ya kwanta" Hawaye suka cika masa ido, gaba d'aya yanzu tausayi Jamal keba Ram baice komai ba ya mik'e ya kira wata nurse ta cire masa drip d'in hannunsa. Da taimakon Ram d'in yasa takalmi suka fito Ram na rik'e dashi har d'akin da Ummyn take. Ummy Abduol✍🏻 [4/26, 8:18 AM] ‪+234 706 272 2689‬: 🖤🖤🖤🖤🖤🖤🖤🖤 🖤🖤🖤🖤 *JAMALUDEEN* 🖤🖤🖤🖤 🖤🖤🖤🖤🖤🖤🖤🖤 By *Ummy Abduol* Dedicated to My *Late Siblings* *Fcbuk Page* https://facebook.com/Ummy-Abduol-Novels-1033022590196192/ Page 81 n 82 Da taimakon Ram yasa takalmi suka fito Ram na rik'e dashi har d'akin da Ummyn ke take. Duk da yanda yake ganin jiri hakan bai hanasa sakin Ram ba ya murd'a kofan d'akin ya shiga. Kwance ya sameta kan gadon marasa lafiya tana bacci, hannunta sanye da canular ana mata k'arin jini. Ya k'arasa ya zauna bakin gadon yana kallanta hawaye cike a idonsa, sai yanzu abubuwan da suka faru suka dawo masa. Hawaye ya soma kansa k'asa har lokacin bai bar mamakin Mami da Aunty Faty bah. Yana nan zaune kusa da ita har bayan minti talatin, Ram da Mifzal suka shigo d'akin a tare. Hannu Mifzal ya mik'a masa sukayi musabaha sannan ya tambayesa ya jikinsa. "Dasauk'i. Nagode Mifzal" Ya juya ya kalli Ram yace "Nagode Ramadhan" Mifzal yayi murmushi yana d'an bubuga kafad'ar Jamal "Mu dakai ba godiya" D'an motsawa Ummyn tayi gaba d'aya hankalinsu ya koma kanta, ta b'ata fuska ta sake juya kwanciyanta. Duk idanunsu nakanta, juye juye ta soma tana rik'e da maranta tana kuka a hankali har lokacin idanunta a lumshe. A rud'e ya rik'o hannunta "Open ur eyes Wife, ni neh, Jamal ne" Kasa bud'e idon tayi har lokacin tana juye juye, Ram ya fita dasauri chan sai gashi shida Dr da wasu nurses. Rok'onsu Likitan yayi akan su bashi waje, dakyar Jamal ya saki hanunta suka fita daga d'akin har lokacin bai daina hawaye bah. Sun d'an dau mintina sannan suka fito, Jamal ya k'arasa inda likitan yake tsaye "Dr hw is she" Da murmushi yace "Komai Lafiya lau, munyi nasarar ba cikin jikinta kariya, yana lafiya ba wani abu. Jinnin data zubar da kuma buguwan data samu a maranta ne yake haddasa mata ciwo a maranta. But data farka zata dawo normal" Jamal ya mik'a masa hannu cike da murna, sukayi musabaha ya wuce. Ba yanda ba'ayi da Jamal ya koma d'akinsa bah dan shima yana under observation anma yaki, dole aka d'auko wani gadon aka sa a d'akin da Ummyn take suna karb'an medication tare. K'arfe takwas da rabi na dare lokacin Ram da Mifzal sun wuce bayan sun aje mai duk abinda yake buk'ata, tashi yayi daga kan gadonsa ya zauna kan kujeran dake kusada Gadon Ummy tare da d'aura kansa kan gadon. Nan da nan bacci mai nauyi da dad'i ya d'aukesa cike da mafarkai kala kala. A Police Station kuwa, Har aka kai Mami bata daina Ihu bah dan ji take kamar k'afar ya guntule ne gaba d'aya, tana kuka Aunty Faty nayi na danasani. Wani likita cikin 'yan sandan ne ya cire mata bullet d'in kafar nata tare da Treating wajan aka turasu a ceil itada Aunty Faty. Kan kace me dambe ya kaure tsakanin su wannan tace laifin wannan neh, wannan ma tace Laifin wannan neh. Babu wanda ya tankasu cikin 'yansandan, Mami ko taci duka wajan Aunty Faty dan ta kasa kwatan kanta saboda k'afarta dake mata zugi dan ko takawa bata iyawa. Iyalen Alhaji Ameenu ne suka zo garin Abuja dan labarin ya riskesu, Hankalinsu a tashe sukazo Police station d'in. Matarsa na ganinsa ta fashe da kuka "Alhaji haka ka koma? Garin yaya haka ta faru" Kasa magana Alhaji Ameenu yayi sboda tsananin b'acin rai, d'ansa kuwa ransa idan yayi dubu ya b'aci, kallo d'aya yama Abban nasa ya fita daga Station d'in. Duk yanda Matar Alhaji Ameenu taso a bada bailing mijinta da Bilal k'i sukayi kan cewa basu gama bincike akansu bah. Ba yanda ta iya hakanan ta hak'ura tabar Station d'in tana kuka. Wayan d'anta mai suna Areef ta soma kira har ya katse bai d'aga ba kuma ga motarda sukazo dashi a parke a k'ofar station d'in. Cikin motar ta zauna tana cigaba da hawaye na tausayin Mijin nata. Tana nan zaune ta hangosa ya sauka a Napeep shida wani sun shiga Station d'in. Ta fito ta bisa da sauri "Areef!" Ta kira sunansa, ya juyo tare da amsawa ransa a b'ace "Ina kaje inata nemanka" Ba tare da wani tunani ba yace "Naje Court ne nakai k'ara" Da mamaki ta kallesa "Kasan me kake fad'a kuwa" Kamar zaiyi kuka yace "Haba Ammi ki dubi abinda akama Abbana fah akan abinda baiji ba bai gani bah, nidai bazan tab'a yarda bah" Bai jira mai zatace ba ya shiga cikin station d'in. Mifzal na Office d'insa takardan sanmacin da Areef ya kawo ya samesa, bayan ya karanta ya saki lallausan Murmushi tare da duba date d'in da za'a shiga Kotun, ya sake yin murmushi "Allah ya kaimu! Ayita ta k'are" ••••••• Bud'e ido tayi a hankali tana bin d'akin da kallo cike da mamaki, tad'an juya gefenta na dama, Jamal ta gani ya d'aura kansa a gadon da take yana bacci bil hak'i da gaskiya. Tayi murmushi tare da cusa hannunta cikin suman kanshi tana d'an masa waiwayi, ya bud'e idonsa dakyar dan bacci ne fal a idonsa, murmushi ta masa ya bud'e ido dasauri tare da mik'ewa zaune. Hannu ta bud'e masa tana masa murmushi dan yanzu gaba d'aya tausayi yake bata, ba musu ta fad'a jikinta suka rungume juna sai hawaye na tausayin junansu, sun dad'e a haka sannan ya janye jikinsa yana kallan fuskanta hawaye na cigaba da gangara daga idonsa "Kiyi hak'uri Wife, nasan komai was my Fault, Laifi na neh ya sh..." Tayi saurin rufe masa baki tana girgiza masa kai, "Ba laifinka baneh My Prince haka Allah yaso" Sosai yaji dad'in sunan data kirasa dashi, ya langwabar dakai gwanin tausayi "Karki danne gaskiya Wife, laifina neh, nine na kasa baki kulawa data dace a matsayina na Mijinki. Ban kasance miji na gari a gareki bah" Ta b'ata fuska tare da juyawa tana kallan wani gefen, cikin shagwab'a tace "Nidai zamu b'ata idan kana wannan maganan. Kaddara ce haka Allah yaso" Ya sake rungumeta yana mai tsananin farinciki. Kula ya soma bata na musamman, shi da kansa yake jinyar abarsa, cikin kwana uku aka sallamesu Ram ya d'aukesu suka dawo gida. Direct Part d'insu sukayi yana d'auke da ita, Palour ya ajeta ya shiga d'akinta ya gyara tsaf sannan ya d'auketa ya kaita sai turo baki take wai ita ya barta tayi tafiya da

Table of Contents

Chapters

82 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82