Chapter 50
Chapter 50
jikinta ta mik'e ta shiga toilet ta saka key. Binta da ido yayi tareda sauke ajiyar zuciya, shi baisan yanda zaiyi ba, sam baya san fushin wife d'insa. Mik'ewa yayi ya fita daga d'akin. D'akinsa ya koma ya cire bedsheet d'in dake kan gadon ya sala cikin washing machine, wani ya d'auko ya shimfid'a ya kwanta cikeda kewa da tunanin Wife d'insa. Mabrookah shiru shiru bata gansa bah, taja tsaki ta rufe ko ina ta haura saman. A hankali ta bud'e k'ofan d'akin, kwance ta samesa idanunsa a rufe, duk a tunaninta bacci yayi, ta kashe wutan d'akin ta k'arasa ta kwanta kusa dashi tana k'okarin shiga jikinsa, cike da takaici yace "Pls Live me alone I'm not in the mood" Ta b'ata fuska "Kai Yaya dan Allah" Tashi yayi ta d'au pillow ya fita daga d'akin ganin tana san b'ata masa rai. Dogon tsaki taja ta kwanta cike da takaici. D'akin Ummy ya murd'a yajishi a rufe, a sanyaye ya hau kan kujeran falon ya kwanta ransa ba dadi. Kiran sallahn farko ya tadasa, ya mik'e ya shiga toilet d'in dake falon yayi alwala ya tafi masallaci. Kamar kullun yauma sai k'arfe bakwai da kwata ya fito daga masallacin, wasu mutane su biyu ya samu a k'ofar gidan tsaye da mai gadi, d'aya sanye da suit bak'i, d'aya kuma magidanci sanye da blue babban riga. D'aya daga cikin masu gadin yace "Yauwa ga Oga nan" Jamal ya k'araso wajan rik'e da chasbaha a hannunsa ya mik'a musu hannu suka gaisa. Mai sanye da suit yace "Sunana Barrister Najib Abubakar, daga Federal High court" Ya nuna dattijon yace "Wannan sunansa Alhaji Tijjani D'an asabe, abokin business ne na Alhaji Surajo. Munzo ne akan bashi dake tsakaninsu kusan shekara uku da suka wuce" Gyad'a kai Jamal yayi yace "Ku mu shiga daga ciki, wannan maganan bana tsaye bane ku shigo daga ciki" Ba musu suka bisa har side d'in Mami, saida suka zauna sannan ya shiga yayo kiran Mami suka fito tare. Bayan sun zauna aka k'ara gaisawa. Barristern ya mik'ama Jamal wani takarda yana cewa "Alhaji Tijjani d'an Asabe na bin Alhaji Surajo kud'i kimanin naira million d'ari da ashirin" Mami ta zaro ido da mamaki tana kallan Barristern "Naira Million d'ari da ashirin fa kace" Sai lokacin Alhaji Tijjani yace "Kwarai da gaske, dan ma ka duba takardan zaka gani a rubuce, harda sa hannunsa dana shaidu" Kurrrri Jamal yayi yana kallan takardar, tabbas ga sa hannun Abba, saidai sauran shaidun ne baisan su waye su bah. Ya mik'ama Mami takardar ta duba tace "Tabbas wannan sa hannun Alhaji ne" Jamal yace "A gaskiya Alhaji, duk shige da fice na mahaifina babu wanda ban sani bah. Duk abinda zaiyi yakan fad'amin, ni bansan da wannan ranchan fa, sannan wad'an nan sunayen na shaidu bansan su bah" Mami tace "Haka neh" Alhaji yace a fusace "Idan kai baka sani ba ai shi Alhajin ya sani, maganan kuma rashin sannin naka ai lokacin kana rashin lafiya." Yanayin yanda Alhajin ke magana yasa ran Jamal ya b'aci, ya mik'e tareda mik'ama Barristern takardar yana cewa "Banida masaniya akan wannan, sannan idan har kunaso mu tabbatar sai ku kawoo shaidun da akayi dasu" Ran Alhaji idan yayi dubu ya b'aci, shima ya mik'e a fusace "Wallahi baku isa bah, ni da hakkina nazo amsa ku cimin mutunci" Uffan Jamal bai sake fad'a ba ya bar falon a fusace. Mami da Aunty Faty ne suka soma basa hak'uri, anma ina sai masifa Alhajin yake har yana cewa zai kai kotu a k'watar masa 'yancin sa. Jamal na shige side d'insa sukayi kicibus da Ummy a bakin k'ofa, kauda fusaka tayi tareda turo baki gaba. Kallanta ya tsaya yi yana murmushi "In kikayi wasa wata rana bakin nan sai yakai kaduna" Duk da yanda take fushi anma hakan bai hanata murmushi ba, ja janyota jikinsa yana murmushi "Pls wife I'm sorry kinji" Yanda yayi magana yasa taji zuciyarta ta sanyaya, taja hancinsa da k'arfi har saida yayi k'ara "Ashhh!" Ta kyalkyale da dariya ta gyara jakan makarantan ta gudu tana dariya. Yau ma kamar jiya side d'in Mami ta shiga, yau ma saida suka zageta tas tareda mata habaici. Makullin motan ta mik'ama Mami, Aunty Faty tayi saurin fisgewa. Haka yau ma ta fito tana hawaye ta shiga mota tabar gidan. D'akinsa ya koma ya shirya ko takan breakfast d'in da Mabrookah ta masa baiyi ba ya fita, side d'in Mami ya shiga, fad'a ta masa sosai akan yanda yama Alhajin nan. Baice komai ba har ta gama ya mik'e ya musu sallama ya fita. A hanya ya dunga neman wayan Lawyern Abba dan yasan shi kad'ai ne zai tabbatar masa da maganan bashin nan da yaga sign d'insa a cikin shaidu. Ajiyar zuciya ya sauke tareda shafa suman kanshi, yanzu ma duk maganan nan da ake, baisan komai game da dukiyar Abban nasa ba sai gidan da suke da kuma Company d'in dayake aiki. Wayan ya soma kira switch off, sosai abin ya basa mamaki dan Lawyers ba kasafai suke chanza number bah. Har yakai wajan aiki bai daina kira ba anma a kashe. Ummy kuwa tun da ta isa makaranta wani zazzab'i ya rufe ta, tasan ba komai ya hadasa mata wannan ba sai rashin baccin da batasamu ba kwana biyu. A daddafe tayi karatu har aka tashi, tana fitowa taga motar Jamal a k'ofar makarantar yana jingine jiki ya hard'e k'afa yana latse latse a wayansa. Ummy Abduol✍🏻 🖤🖤🖤🖤🖤🖤🖤🖤 🖤🖤🖤🖤 *JAMALUDEEN* 🖤🖤🖤🖤 🖤🖤🖤🖤🖤🖤🖤🖤 By *Ummy Abduol* Dedicated to My *Late Siblings* *Wannan shafin sadaukarwa ce ga * Professor Ibrahim Aliyu Malumfashi Family* Allah ubangiji ya sanya albarka a aurenki ```Swt Meenarh Prof``` Ameen. Page 58 n 59 A daddafe tayi karatun har aka tashi, tana fitowa taga motar Jamal a k'ofar makarantar yana jingine jiki ya hard'e k'afa yana latse latse a wayansa. Da murmushi ta k'arasa inda yake tsaye, kurrri ya mata yana kallanta, ji yayi kamar ya rungumota anma ba hali saboda student d'in dake ta shige da fice a k'ofar gate d'in makarantar. K'arasawa yayi ya amsa jakan hannunta wanda dama ya mata nauyi, gaban motan ya bud'e mata ta shiga yaja suka bar haraban makarantar. Titi take ta kallo tana yatsine fuska sboda yanda takae jin jikinta. Yana driving lokaci lokaci yakan juya ya kalleta, ganin yanda b'ata fuska yasa yace "Yadai Wife, ko bakiyi murnan ganina baneh?" Sake turo baki tayi bata kallesa bah, d'an dariya yayi mara sauti, yau rigima kenan take jin yi. Har suka iso gida bata daina kallan windown tana b'ata fuska bah, yana parking ya fito ya zagaya ya bud'e mata ta fito ta wuce side d'insu. Da kallo ya bita har ta shige ya girgiza kai ya d'auko jakanta dake seat d'in baya yabi bayanta. Mabrookah ya samu zaune a falonta itada wata k'awarta suna hira, k'awar nata na ganinsa ta gaida sa ya amsa yana murmushi "Amarya sannu da gida" Jakan hannunsa take ta kallo tana yatsine fuska, baisake ce mata komai ba ya haura sama abunsa, d'akin Ummy ya nufa ya bud'e a hankali da sallama, kwance ya sameta kan gado ko uniform bata cire ba, ta k'uddun dune waje d'aya idanunta a lumshe sai hawaye dake gangara daga
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82