Skip to content

Chapter 10

Chapter 10

Jamaluddeen Book One Complete Hausa Novels 1,198 words 0 views Progress saved
Download Book

Camrey wanda Turawa masu aikin Jamal d'in ke ciki. Cikin ABU suka shiga suka d'an zazaga sannan suka fito suka tafi wani park. Ummy sai raba ido take dan sunan tana zaria neh kawai anma tunda take bata tab'a shiga cikin ABU bah. Bayan sunyi parking motocinsu Hajiya ta fito tareda shimfid'a k'aton carpet a k'asa, turawan suka kamoshi aka d'aurashi kan wheel chair d'insa. Kusa dashi Hajiya ta zauna tana kallanshi idanunta cikeda kwalla "Allah ya baka lapia Jamal, Ina kewarka sosai, Allah ya tashi..." Kasa k'arasa maganan tayi ta tushe da kuka, Ummy hawaye ya cika mata ido ta rarrafo kusada Hajiyar tana cewa "Kiyi hak'uri Hajiya, Addu'a yakamata ki rink'a masa ba kuka bah" Hajiya ta juyo ta kalleta tareda share hawayen fuskanta, wani malalacin Murmushi tayi tace "Bakisan yanda nakeji ba Ummy, Inasan Jamal fiyeda komai a duniya, da kud'i zaisa Jamal ya warke da tuni ya warke, banida wani buri yanzu daya wuce naga koda murmushin Jamal koda bazai bud'i baki yayi magana bah" Hawaye suka gangaro ma Ummy tace "Kiyi hak'uri Hajiya, kid'au hakan jarabawa ce a gareku gaba d'aya. Kiyi ta masa addu'a insha Allahu zai warke ya dawo yanda yake dah" Wani kukan Hajiya ta fashe dashi "Na cire wannan tsamanin Ummy, shekaran Jamal Uku a zaune a wannan kujeran, baya magana, baya motsi" Hijab d'in jikinta tasa tana sharema Hajiyan hawaye. "Duk mumini baya cire rai daga rahamar Allah, kiyi hak'uri wata rana sai labari. Insha Allahu wata rana sai kin gaji idan ya fara miki surutu" Sosai maganan Ummy yaba Hajiya dariya, tad'anyi murmushi tana duban Jamal d'in dake zaune kamar gunki kan keke. Kayan ciye ciye Hajiya ta siya musu sukaci suka sha, dama shi Jamal yana sanye da NG tube ta hancinsa dan baya iya tauna abinci saidai a d'ura masa abu mai ruwa ruwa ta hancinsa. Maltina Hajiya taba d'aya daga cikin masu kula dashi ta bashi, ta syringe ta soma zuk'a tana d'ura masa ta tube d'in, ganin yanda ake basa abincin tausayi yasa Ummy fashewa da kuka mara sauti ta kauda kanta gefe. Ummy Abduol✍🏻 [3/12, 8:25 AM] ‪+234 806 215 4020‬: ♠♠♠♠♠♠♠♠ ♠♠♠♠ *JAMALUDEEN* ♠♠♠♠ ♠♠♠♠♠♠♠♠ By *Ummy Abduol* Dedicated to My *Late Siblings* Page 13 Tausayi yasa Ummy fashewa da kuka mara sauti ta kauda kanta gefe. Ji tayi duk kayan ciye ciyen sun isheta ta turasu gefe ta d'ago idanunta tana kallan Jamal d'in. Hajiya ta nisa tace "Ina jin dad'in zama dake Ummy, kinda Hankali da tarbiya ga natsuwa" Murmushi Ummyn tayi ta duk'ar da kanta k'asa "Inaso ki d'aukeni a matsayin Uwa a gareki, kada kiji tsoro ko shakkan sanar dani damuwarki kinji?" Gyad'a kai tayi sannan tace cikin sanyin Murya "Nagode Hajiya" Murmushi Hajiya tayi tace "Ki rink'a kirana da Mami kamar yanda Mabrookah take kirana. Ke da ita duk d'aya na d'aukeku" Godiya Ummy ta mata sosai, sun jima sannan suka d'au hanyan gida. A wani boutique suka tsaya Mami tace Ummy ta biyota ciki, kaya Mami keta d'auka na maza ga dukan alamu na Jamal neh, sai kuma wasu data d'auka na mata itadai Ummy sai binta take a baya, juyowa tayi suka had'a ido tace "Ki d'auka duk abinda kikeso" Ware ido Ummy tayi tana kallan Hajiyar, kasa d'aukan komai tayi ganin tak'i d'auka yasa Mami ta d'aukan mata dogaren riguna da ready made atamfofi wanda zasu mata. Sun biya Ummy ta d'au ledojin suka nufi mota suka wuce gida. Saida takaima Hajiyar kayan d'aki sannan ta sauko ta koma d'akinta ta sauya kayan jikinta zuwa uniform ta nufi kicin wajan Laurat, koda taje ta sameta ta cika tayi fam saura kad'an ta fashe. Kallo d'aya Ummy ta mata ta kyalkyalle da dariya "Hajiya Laurat, yadai meya faru?" Laurat ta k'ara turo baki ta kauda kai, dariya Ummy ta k'arayi tace "Ahaf karkiyi maganan, ai gobe ina gida abuna maga da wanda zakiyi" Jin haka yasa ta juyo dasauri tana yatsine fuska "Ai kece kin cika abin haushi, ba inda ban nemeki ba a gidan nan ban ganki bah" "Tho maida wuk'ar, mun fita ne da Hajiya d'azu" Da mamaki Laurat tace "Dah Hajiya?" Ummy ta gyad'a kai tareda zama kusada ita ta soma bata labarin fitar nasu. Hannunta Laurat ta kama tana murmushin farinciki "Ummy kin shigo gidan nan da k'afar dama, lallai kinada sa'a" Ummy tai dariya kawai batace komai bah. Washe gari misalin k'arfe goma Ummy ta fito daga kicin dan tasan a wannan lokacin ya isa ace su Hajiyan sun tashi, sama ta haura tayi knocking d'akin Hajiya, izini Hajiyan ta bata ta shiga da sallama, zaune ta sameta kan stool tana shafa cleanzer a fuskanta, har k'asa ta tsugunna ta gaidata ta amsa tana kallanta da murmushi "Barin baki guri kiyi aikinki" Tashi Hajiyan tayi har takai bakin k'ofa sai kuma ta dawo tace "Jiya shine kika ajemin kayan nan a d'akina? Ai na saya miki neh ki d'auka ki cigaba da anfani dasu." Ta nuna mata k'aton ledan dake kusada bedside tana cewa "Gashi chan ki d'auka" Godiya Ummy ta shiga mata tai saurin girgiza mata kai tana cewa "Ba godiya a tsakanin mu Ummy, kin wuce haka a wurina" Bata jira mai zatace ba tabar d'akin, aikinta ta shiga yi ta gyara ko ina tasa turaren wuta mai k'anshi ta fito bayan ta d'au ledan kayan. K'asa ta sauka ta kai ledan d'aki sannan ta dawo ta shiga d'akin Mabrookah, saida ta gama mata wulak'anci da zagi sannan ta fito ta bata waje. Dama kuka baima Ummy wuya, saida tayi mai isarta sannan ta gyara d'akin ta fito. Yau ko k'ofar d'akin Jamal bata kalla ba ta sauko k'asa ta koma d'akinta. Kayan da Mami tasai mata ta bud'e ta duduba, kaya ne masu kyan gaske da tsada, set biyu wanda tasan zaima Mamanta ta d'auka tasa a leda sannan ta sauya kaya cikin wanda Mamin tasai mata, dogon riga neh pink swait mai stones a k'irji, sosai kayan suka amsheta tayi kyau sosai, dama Ummyn ba banza ba akwai diri. Farin hijab tasa ta fito zuwa falo, Mami tama sallama wannan karon driver akasa ya kaita gida. Iyayenta sunyi farinciki da zuwanta, ranar kusan raba dare sukayi suna hira, a nan Ummy ke fad'a musu matsalan Jamal, sunyi alhini tareda mai addu'an samun Lapia. Washe gari saida ta musu girki da duk wani abu da suke buk'ata sannan ta taho, wannan karan bata shiga gidansu Bilal bah dan wannan satin a kuraren lokaci tazo. D'akinta ta shiga ta sauya kayanta sannan ta haura sama zuwa d'akin Mami ta shaida mata dawowanta, kicin ta shiga ta samu mutuniyar nata na gyaran alaiyahu, ta gaida sauran mutanen kicin d'in sanan ta zauna kusada Laurat tace "Sannu da aiki" "Yauwa, anma fah yau kin dad'e baki dawoba" Ummy ta saki murmushi tana hararanta da wasa "Keko ina tsakiyar Baba da Mama mai zai kaini dawowa yanzu" Murmushin k'arfin hali Laurat tayi, idanunta suka ciko da kwalla tunawa da Kakarta dan ita batasan dad'in Iyayeba saboda tana k'arama suka rasu. Ummy tai saurin kauda zancen da cewa "Mama na gaishe ki, har y'ar tsaraba ta bani na kawo miki" Da fara'a Laurat ta d'ago tace "Kai dan Allah dagaske?" Ummy ta gyad'a

Table of Contents

Chapters

82 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82