Skip to content

Chapter 31

Chapter 31

Jamaluddeen Book One Complete Hausa Novels 1,196 words 0 views Progress saved
Download Book

it_ Ummy Abduol✍🏻 [3/12, 9:44 PM] ‪+234 903 823 4806‬: ♠♠♠♠♠♠♠♠ ♠♠♠♠ *JAMALUDEEN* ♠♠♠♠ ♠♠♠♠♠♠♠♠ By *Ummy Abduol* Dedicated to My *Late Siblings* Page 35 Ram ko kamar ya fashe saboda b'acin rai. Harara yaketa wurga ma Taseem har suka bar wajan. Ummy na shiga zauren gidansu Inna ta mik'a ma Laurat kedan tana cewa "Wai kayan dinner da ko menene oho" Amsa Laurat d'in tayi suka k'arasa cikin gidan, Inna ta mik'ama kayan sannan suka bud'e, Gowns ne guda biyu, d'aya Red mai touch d'in yellow, sai Head Bak'i, d'inkin sosai yayi kyau Laurat sai yaba kayan take. Da zumud'i ta d'aga d'ayan gown d'in, shi kuma bak'i neh da Farin Head, sai rafan y'an dubu guda biyu daya fad'o. Inna ta d'auka baki bud'e "Wannan kud'in fah!" "Ina tunanin na manni neh" cewar Laurat Itadai Ummy ko uhumm batace bah saima kauda kai gefe datayi tana kallan kayan ta gefen ido, dan itama sun burgeta sosai. A chan b'angaren Amarya Mabrookah kuwa, shirye shirye ake duk da dukansu babu wanda ransa ke cikin dad'i na maganan Auran Ummy. Bak'i ne cike a gidan daga b'angaren Mami da kuma Abba, itama Aunty Fatyn nata tawagar duk a nan suka yada zango. Su Aunty Zainab duk sun iso, itadai sam batajin dad'in zaman da Aunty Fatyn keyi a gidan Mami, tadaiyi shiru ne dan tasan idan tayi magana zasu iya rabuwa baran baran dan ba hak'uri Aunty Fatyn keda shi bah. Da daddaran ranar Najma da Najwa suka samu Aunty Zainab Umminsu a d'aki, zama sukayi Najma ta soma rok'onta akan ta barsu suje Gidansu Ummy suyi nasu shagalin. Da mamaji Aunty Zainab tace "In banda shashanci irin naku, yaushe ake barin sha'anin gida a tafi na bare" Najwa tace "Ummi kinga fah mu itace k'awarmu, kuma Aunty Mabrookah ba kulamu takeyi bah" Nan suka kwashe duk abinda ya faru lokacin da ta tafi suka sanar da ita. Sosai ta tausaya ma Ummyn "Idan na barku kuka tafi zan jama kaina surutu neh, kuyi hak'uri kawai ku zauna nan" Ga mamakinta sai gani tayi sun fashe da kuka, binsu da ido take tayi da mamaki. Ajiyan zuciya ta sauke sannan tace "Shikenan kuje, anma dan Allah ku kiyaye" Rungumeta sukayi a tare har saida suka fad'a kan gadon datake zaune, duka ta d'aka musu "Tho ku k'arsani ku huta" Suka mik'e suna dariya suka nufi d'akinsu, kaya suka loda suka fito tareda ma Ummin nasu sallama. Ram suka samu ya kaisu lokacin anata kiraye kirayen sallan Magriba, dan dama shima Abba ya aikeshi gidan wajan kawun nan Ummy. A mota Ram ke cewa "D'azu muka dawo daga gidan, sun ce wallima kawai zasuyi" Najma tace "To Ya Ramadhan nawa kuka basu" "50k" yace a takaice "Haba Ya Ramadhan, 50k mai zeyi wallahi yayi kad'an." Murmushi yayi yasa hannu a aljihu ya ciro wani rafan yan d'ari biyar ya mik'a musu "Wannan fah" Najwa tace "Eh to za'ayi managi" Da mamaki ya d'an kuyo ya kalleta "Lallai ma yaran nan" Suka kwashe da dariya daidai lokacin da suka k'arasa gidan. Dasauri suka fito suka shige cikin gidansu Ummyn, a cike suka samu gidan, dakyar suka iya lalubo Mama, bayan sun gaisa take fad'a musu tana chan mak'ota. Rige rigen shiga suka soma yi gidan Inna, Ummy dake zaune tsakar gidan kan kujeran tsuguno zatayi alwala ta mik'e cikeda farinciki ta rungumosu tana dariya. Laurat da Inna suka fito suka musu sannu da zuwa. Sosai Ummy taji dad'i da suka fad'a mata nan zasu zauna ayi biki. Inna ma tayi farincikin zuwansu musamman data lura yaran wayaiyu ne kuma sunada tarbiya. Dakyar suka matsa ma Ummy a daran suka kakkai ma k'awayenta dake layin kati, da kuma maza wad'anda suke abin arziki lokacin da take saida Awara. Laurat ta d'iba taba Bahar dan ya rabama nasa abokanan da kuma 'yan uwa da abokan arziki. Ranar da daddare Ummy ta k'uduri niyan kiran Bilal dan suyi shawaran abinda za'ayi, dan yace mata kada ta k'ara nuna ma kowa bata san auren. Bayan kowa yayi bacci ta lalubo numbern Bilal d'in ta danna kamar yanda Laurat ta koya mata. Ringing biyu ya d'auka, sallama ta masa ya amsa a dak'ile "Ina yini Ya Bilal" "Lafiya lau ya shirye shiryen biki" Ta d'anyi Jim batace komai bah "Na lura duk fad'in sanda kike min k'arya neh. Har yana kawo miki kati kuna rabawa." "Wallahi ba haka baneh Ya Bilal ni..." Yayi saurin katseta da cewa "Ba abinda zaki fad'amin Ummy! Nagode da yaurada ta da kikayi" "Dan Allah ya Bilal kayi hak'uri, wallahi ina sanka karka min haka" "Inda kina sona da baki kai har yau da auransa a kanki bah. Nayi dana sanin baki amanar zuciyata Hrt, ashe bazaki iya amanar da kika d'aukan min bah" Kuka ta fashe dashi ta k'ara rik'e wayan sosai a kunnenta. Shima kukan yake a hankali "Bazan tab'a rayuwa bake bah. Sai na nuna ma Jamaludeen kuskurensa na san abinda nakeso" Kan tayi magana ya kashe kiran. Da kuka ta sake kira anma taji switch off. Kuka ta fashe dashi ta kwanta tana kuka sosai. Haka ta tashi washe gari da kumburaren fuska, Kallo d'aya Inna ta mata ta gane kuka tayi. Fad'a sosai ta mata dan tasan bai wuce akan maganan Bilal. Wuraren k'arfe takwas na safe suka bar gidan, Gyallesu suka nufa gidan Lalle, an rangad'a mata lalle kyan gaske da gyaran jiki, suma k'awayen amaryan an musu mai kyau duk sun fito tsaf abinsu. Twins ne suka biya cikin kud'in da Ram ya basu jiya. Sannan suka zarce Kanuri beauty saloon, nan ma aka gyara musu gashin su, su twins sai santin yawan gashin Ummyn sukeyi. Basu bar wajan Saloon d'in ba sai k'arfe biyu da rabi na rana, dan ma Dinnern k'arfe shidda ne. Kasuwa suka shiga suka sai abubuwan da zasuyi anfani dasu na walimar su sannan suka dawo gida a gajiye. Reedah makeover su twins suka gaiyato ta rangad'a musu kwaliya mai kyan gaske, black gown amarya ta saka, aka d'aura mata White head. Kar kuso kuga Ummy ni kaina sai dana yaba abinka da farar fata sai Gowm d'in ya fito da ita sosai. Su Twins dama sun musu d'inki su da Laurat, suma sunyi kyau cikin Milk Gown da Red head. Kan kace me gidan ya cika da k'awayen Ummy dukan su cikin shirin zuwa dinner. A chan gida kuwa rigima ce ya b'alle tsakanin Jamal da Amaryar tasa Mabrookah. Ummy Abduol✍🏻 [3/12, 9:45 PM] ‪+234 903 823 4806‬: ♠♠♠♠♠♠♠♠ ♠♠♠♠ *JAMALUDEEN* ♠♠♠♠ ♠♠♠♠♠♠♠♠ By *Ummy Abduol* Dedicated to My *Late Siblings* Page 36 A Chan gida kuwa rigima ce ta b'alle tsakanin Jamal da Amaryar tasa Mabrookah, lokacin da taji cewa shi da abokansa ne zamu je d'aukan Ummy Itama kwaliya taci cikin Brown Gown mai tsadar gaske da milk head, tayi kyau itama sosai, k'awayenta kuma suna sanye da red gown suma duk sunyi kyau. Ana gama shiryata ta shiga side d'in Abba dan a nan Jamal d'in yake, ko kallon abokanan angon dake nan falo batayi ba ta shiga bedroom d'insa. Tsaye ta samesa yana sanya agogo, shima yayi matuk'ar kyau, yana sanye da Arsh d'in shadda sai zuba k'amshi yake. "Haba Jamal! Ya za'ayi kace ni

Table of Contents

Chapters

82 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82