Chapter 39
Chapter 39
a tray ta aje gefe. D'akinta ta koma sake wanka ta sauya kaya zuwa dogon rigar yadi robber mai taushi, kayan sun mata kyau sosai saboda duk shape d'inta saida ya fito cikin rigan. Tana nan zaune akayi magriba, ta shiga d'aki tayi sallah ta zauna har akayi isha'i. Bud'e kofan d'akinta akayi lokacin ta cire hijabin jikinta kenan, ta juyo suka had'a ido. Wani miyau Jamal ya had'iye dakyar yana binta da ido. Kanta k'asa tamai sannu da zuwa, bai amsa ba sai k'arasowa dayayi ta janyota jikinsa yana murmushi "Kinyi kyau sosai Wife" K'ara sunkuyar dakai tayi tana murmushi "Oh Come on bansan kunyan nan, yana tauye ni. Ki saki jikinki pls. I promise to shower uh with my love" Ummy Abduol✍🏻 [3/22, 5:23 AM] 0mmer Farouk: ♠♠♠♠♠♠♠♠ ♠♠♠♠ *JAMALUDEEN* ♠♠♠♠ ♠♠♠♠♠♠♠♠ By *Ummy Abduol* Dedicated to My *Late Siblings* Page 43 Ya juyo zuwaga Mami kacha kacha ya mata ya mik'e ya haura d'akinsa dan ta soma kaisa bango. Binsa da ido Mami tayi ranta b'ace, tai kwafa tana cewa "Ai wallahi bai isa ki rabani da d'ana bah Ummy, inkin san wata ai baki san wata bah" Taja dogon tsaki ta fita zuwa nata side d'in. Jamal kuwa d'akinsa yayi da Ummy daketa kuka tana k'okarin kwace kanta daga rikon daya mata. Bakin gadonsa ya ajeta ya tsugunna gabanta yana share mata hawaye. "Kiyi hak'uri Wife, karkiyi fushi da Mamina, i know wata rana zata daina kinji" Kan gadon ta fad'a ta fashe da kuka mai sauti, shima ya biyota kan gadon ya rungumota jikinsa yana lallashinta. Dakyar ya samu tayi shiru, ya tayar da ita zaune ya share mata hawaye "Wata rana sai labari, insha Allahu Mami zata soki zata k'aunace ki kinji" Kai ta gyad'a masa da wani k'wallan a idonta. Lightt kiss ya mata a lips d'inta ya shafa suman kanta yace yana zuwa. K'asa ya sauka zuwa d'akin Mabrookah dan sosai ta b'ata masa rai yau. Yana ya tarar da ita ta fito wanka, nunata yayi da yatsa ransa b'ace "Yaushe na fara wasa dake da har kike neman raina ni" Ta zunguro baki "To mai kuma na maka" "Wallahi idan kika k'ara zuwa kika had'ani da iyayena, ko kikayi gigin sake tab'a Ummy" yayi kwafa "Kana tauye ni kuma kace bazanyi magana bah" Ta fashe masa da kuka "Baka shigowa d'akina, baka kula da alamura nah" "Jaraban ki ce ta rufe miki ido har kika ga bana shiga d'akinki. So nawa ina fad'a miki sai Ummy ce uwargida and saina gama mata ranakunta tukun" Ta rushe da kuka ta fad'a kan gado "Bakayin adalci Ya Jamal" Tsaki yayi ya fita daga d'akin dan yasan ransa ne zai cigaba da b'aci a banza a hofi. Haka rayuwar gidan Jamaludeen ta cigaba da kasancewa kullum Ummy zatayi girki tasa ma Abba, Ran Mami ko ya k'ara b'aci. Har side d'insu Ummyn tazo ta mata kacha kacha, ta kuma mata kashedin karta sake sakama Abba abinci. Kullum lesson teachern ta saiya zo, tana jin dad'in karatun sosai. Haka idan Jamal ya dawo daga office zai zauna ya sake mata bita da kuma k'arin bayani. Shak'uwa kam tsakanin Jamal da Ummy ba'a magana. Saidai Abu d'aya da kullum ke damunta rashin k'aunar da Mami da Mabrookah ke mata. Haka ango Jamal ya gama kwanakin sa wajan uwargida ya dawo wajan amarya. Ranar da zai dawo karku so kuga Mabrookah baki har kunne, sai rawar k'afa ake da iyayi anama Ummy kallan banza. Ranar bataje school ba da kanta ta shiga kicin tamai girki sai k'anshi ke tashi a gidan. Bayan ya dawo daga office sama ya haura yayi wanka ya sauya kaya zuwa na shan iska. D'akin Ummy ya lek'a ya sameta kwance ta takure waje d'aya, ya k'arasa bakin gadon ya tab'a jikinta yaji ba zafi "Wife ya dai" Zaune ta tashi saiga hawaye shar, nan da nan ya rud'e "Lapia Wife me aka miki" Kuka ta fashe dashi, ya rungumota jikinsa yana lallshinta, duk yabi ya rud'e dan ko kad'an baisan kukan Wife d'in tasa. "Fad'amin me aka miki, waya tab'aki" A shagwab'e tace "Ni inaso naje gida naga Mama" Ya d'ago fuskanta yana share mata hawaye "Mama kikeson gani" Ta gyad'a masa kai, wani hawayen na gangara a idonta. "Dauko mayafinki muje" Ta d'ago kai dasauri tace "Dagaske" Kai yad'an gyad'a mata, ta rungumeshi tana dariya. Murmushin jin dad'i yayi, ya k'ara janyota jikinshi ya had'a bakinsu guri d'aya. Mutsu mutsu ta soma ya rik'eta sosai. Sun dad'e a haka sannan ya janye bakinsa ya dafe kansa da hannayenshi. Tayi saurin mik'ewa tana turo baki ta shige toilet, dakyar ya iya tashi ya koma d'akinsa. Wanka ya sakeyi ya sauya kaya zuwa kaftan fari k'ar. A falo suka had'u itama ta shirya cikin pink shadda dogon riga. Ya matso ya kama kugunta da hannayensa biyu yana mata murmushi "Kinyi kyau sosai Wife" "Nagode" tace a hankali. Bakinsa yakai wuyanta yad'anyi kissing, tayi saurin lumshe ido dan sak'on nasa ya shigeta sosai. Murya a sanyaye ya rad'a mata "Yaushe zaki bari na nuna miki san danake miki, I'm suffering alot i need uh" Ta janye jikinta dasauri tana murmushi, sauka tayi k'asa, yad'anyi jim tareda sauke ajiyar zuciya sannnan yabi bayanta. Tana saukowa ta samu Mabrookah a falonta, tayi gayu cikin Top fari mai kyau da wando iya guiwa, ya matseta sosai, fuskan nan yasha makeup. Tayi kyau sosai dan itama mai kyau ce. Kallo d'aya Ummy ta mata ta kauda kai ta fita, tsaki Mabrookahn taja chan saiga Jamal ya sauko. zumbur ta mik'e ta k'araso tana karairaya "Haba Honey ina kuma zaka bayan kasan kwana na neh yau" Yad'an yatsine fuska tareda matsawa gefe sbda kokarin datake na chafko rigansa. "Uzuri ne ya kama zamu fita, but idan nadawo ai shiknan" Bai jira mai zatace ba ya fice ya barta tsaye cikeda takaici. Har tayi hanyan k'ofa dan zuwa sanar da Mami sai kuma ta fasa tuna abinda ya fad'a mata rannan. Hakanan badan ranta yaso ba ta koma ta zauna ranta b'ace. Bakin motarsa Ummy taja ta tsaya harya k'araso, bud'e mata yayi ta shiga sannan shima ya shiga suka d'au hanya. Tsaraba ya tsaya yama Maman nad'an abinda ba'a rasa ba sannan suka k'arasa. Dagudu ta shiga cikin gidan ta fad'a jikin Mama dake falo tana lazumi, a tsorace Mama ta janye jikinta dan bata ga fuskan waye bah, ganin Ummy ce yasa itama ta rungumeta tana tambayanta gida. Kuka Ummy ta fashe dashi tunawa da kullum idan ta dawo gidan aikinta, Bayan ta gaida Mama wayan Baba take zuwa su sha fira abinsu. Nan ta sake rushewa da kuka, Mama ta soma lallashinta, itama ta kasa daurewa sukayita kukan tare. Dakyar sukayi shiru, Mama ta tambayeta 'yan gidan nasu ta amsa da lafiya kawai. Jamal jin shiru shiru ba Ummy yasa yad'au ledan tsaraban ya shiga da sallama, jin sallaman shi yasa Mama gyara hijabin jikinta, ai sai kice min da mijinki kuke. Kai Ummy ta duk'ar ya shigo ya samu guri ya zauna tareda gaida Maman. Ledan ya mik'ama Ummy ta mik'ama Mama, godiya Mama tayi tana cewa "Badai ka gajiya" Yayi murmushi baice komai bah, Mama tace "D'an leka ki gaida Innan Bilal" Had'a ido sukayi
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82