Skip to content

Chapter 43

Chapter 43

Jamaluddeen Book One Complete Hausa Novels 1,205 words 0 views Progress saved
Download Book

wajan dake da kansa dake jini, kuka take tana kallansa ba halin taimaka masa. Ummy har lokacin tana hannun d'aya daga cikinsu tana kuka tana fifizgewa. Wani daga cikin b'arayin ya shigo yama Ogan magana a kunne ya fita, chan ya d'aga kai ya dubi agogo sannan ya tako har inda Abban yake tsugunne yace "Kamar yanda na fad'a maka a baya, bama buk'atar kud'inka. Ranka kawai mukazo d'auka" Abba ya zaro ido, Haka Mami dake kusa dashi "Dan Allah kuyi hak'uri kar ku kashe min mijina na rok'e ku" Rarrafowa tayi ta kama k'afan Ogan, yayi kicking nata gefe, Ba Tausayi bare tsoron Allah ya saita Bindigar Hannunshi ya harbi Abban Har sau biyu a ciki. Wani ihu Jamal yayi ya mik'e yana ganin jiri yayi wajan Abban yana kuka sosai, Ummy kuwa luuuuu tayi ta fad'i sumamiya a Wajan. Da gudu b'arayin suka bar gidan suka shishiga motocin su suka gudu. Duk da yanda kan Jamal d'in ke jini ga kuma Jiri dake d'ibansa bai hanasa rungumo Abban ba zuwa jikinsa yana kuka yana girgiza sah. Dakyar Abban Ya iya bud'e idonsa yace "Ka...ka..k..ka Gafar...ce ni d'ana" Ummy Abduol✍🏻 [3/29, 8:36 AM] ‪+234 701 141 1639‬: ♠♠♠♠♠♠♠♠ ♠♠♠♠ *JAMALUDEEN* ♠♠♠♠ ♠♠♠♠♠♠♠♠ By *Ummy Abduol* Dedicated to My *Late Siblings* *Wannan Page tukuici ce gareku Jamaludeen Fans a ko ina kuke a fad'in duniya* Gaskiya ina matuk'ar jin dadin yanda kuke so na kuma kuke san novel d'ina. Allah yabar zumunci Ameen Page 47 to 49 Dakyar Abban Ya iya bud'e idonsa yace "Ka...ka..k..ka Gafar...ce ni d'ana" Idanun sa suka rufe lufff, wani razananen Ihu Mami ta saki ta k'arasa tareda fashewa da kuka. Tuni Jamal ya fad'i jikin Abban shima ya some Mami duk tabi ta rud'e, Abba da Jamal kawai take jijigawa tana kuka da k'arfin gaske. Kan kace gidan ya cika dank'am da mutane, lokaci guda 'yan sanda suka cika layin. Abulance d'in ABUTH ne sukazo suka d'au Abba da Jamal da kuma Ummy, Mabrookah da Mami suka bisu sai kuka suke dukansu. Masu Aikin gidan babu wanda bai zubar da kwalla bah ganin yanda aka fita da Abba da Jamal. Cikin mintina kad'an suka iso asibitin, direct Emergency akayi dasu, nan likitoci suka duk'ufa akan Abba saidai Ina Rai ya ruga yayi halinsa. Shima Jamal sunyi treating d'insa, tareda suturing wajan saboda kan nasa ba k'aramin fashewa yayi bah. Mami da Mabrookah da kuma sauran mak'ota. Suna bakin k'ofar d'akin cirko cirko, Mami da Mabrookah sun rungume juna sai kuka suke, wasu daga cikinsu na lallashinsu. Jamal aka soma fitowa dashi, kansa nan nad'e da bandeji, Mami tayi kanshi tana tambayan Nurses d'in. Daya daga cikinsu ne ta juyo tace "Yana lafiya lau da ransa" Wani d'aki suka kaisa, sannan suka dawo suka fito da Ummy itama suka kaita d'akin. D'aya daga cikin likitocin ya fito yana cire gloves d'in hannunsa "Doctor yaya mijina, wani hali yake ciki yanzu" Ajiyar zuciya ya sauke ya d'an girgiza kai yace "I'm sorry to say..." Wani chafka Mami ta kaima kwalarsa "No Doctor kar kace min ya mutu" Bai iya cewa komai bah sai kura mata ido dayayi, ta sake fashewa da kuka, Mabrookah ta rungumeta tana kuka sosai, dakyar ta zama hannayenta daga rigan likitan ta fashe da kuka "Allah ya isa tsakanin mu daku, bazan tab'a yafe muku kashe min mijina da kukayi bah" Duk wanda yake wajan sai daya tausaya ma Mami, haka Mak'ota da sukazo tare suka d'au gawan Abba aka maida shi gida. Nan da nan gida ya d'auka da koke koke, Mami duk tabi ta zauce kamar ba ita bah. A cikin daren aka masa wanka. Washe gari kan kace meh gida ya d'auka, daga wurare daban daban sai bulbulowa ake janaiza. Jamal kuwa yana chan kwance har lokacin bai farfad'o bah, haka itama Ummyn. Nurses ne ke tare dasu suna kula dasu. K'arfe Tara na safe Ummy ta farfad'o da kuka, Nurse d'in dake tare dasu ta soma lallashinta, Jamal ta kalla dake kusada gadonta ta sake fashewa da kuka tana kallansa "Ya Jamal! Ya Jamal!!" Jin shiru yasa ta sake fashewa da kuka. Wajan nurse din ta juya "Ina Abba yake?" Saida Nurse d'in tad'anyi Jim sannan tace "Allah ya masa rasuwa" Karaf akan kunnen Jamal lokacin daya farka daga dogon suman dayayi. Ba shiri ya mik'e idanunsa cike da kwalla "Ina Abbana? Ina yake" Ummy ta rungumesa tana kuka "Abba ya rasu" Tureta yayi yace "Nooo!" Ya fad'i wajan guyawu biyu ya fashe da kuka. Daidai lokacin Ramadhan ya shigo d'akin wujiga wujiga, Jamal na ganinsa ya sake fashewa da kuka "Sun kashe min Abbana Ram, sun kashe shi" Duk yanda Ram yaso ga daurewa kasawa yayi ya fashe shima da kuka ta tsugunna kusada Jamal d'in, had'a goshi sukayi suna kuka mai ban tausayi. Ummy dake chan gefe itaba ba abinda take sai kukan. Dakyar Nurse d'in ta lallashe su ta fita dan ta kira likita. Jamal idanunsa na zubar da kwalla yace "An kaisa neh" Ram yace "Aa sai sha d'aya" Agogon d'akin ya kalla yaga goma da kwata, mikewa yayi dasauri ta tumb'uke Drip d'in dake hannunsa "Muje Ram, muje naga Abbana kafin a tafi dashi" Tausayin sa ne ke ratsa Ummy, duk hankalinta na kansa, ba musu Ram ya mik'e ya rik'e hannun Jamal d'in suka fito d'akin Ummy na binsu a baya. Suna shiga layin suka soma hango dandazon mutane, dakyar suka samu aka mamatsa musu suka shiga da motar cikin gida saboda kayan dake jikin Ummyn. Ganin cikin gidan dank'am da mutane yasa Jamal k'ara fashewa da kuka. Dasauri ya fito daga cikin motan, mutanen dake haraban gidan sai kallansa suke, direct side d'in Abban ya nufa yana kuka kamar ransa. A Falon sama ya hango gawansa, Mami da sauran 'yan uwa a gabansa suna kuka wasu na masa addu'a. Wani jiri ne ya d'ebesa yayi baya zai fad'i, Ram dake bayanshi yayi saurin rik'eshi. Har gaban gawan Abban ya kaisa ya zaunar dashi. Kuka kam Jamal yayi shi kamar ba gobe a gaban Abban, mutanen dake wajan ne keta basa baki, dakyar ya iya tsagaitawa ya d'aga hannu biyu yana masa Addu'a hawaye na cigaba da kwaranya daga idonsa. Ya dade yana masa addu'an, ya sake kallansa murya chan k'asa yace "Tafiyan dakace zakayi kenan Abba! Meyasa ka zab'i ka tafi ka barni" Mami ta fashe da kuka jin maganar da Jamal keyi. Dakyar aka d'agasa aka fita dashi daga falon, Ram ya d'iban masa ruwan Alwala ya tasa shi a gaba, kasa yi yayi, Ram da kansa ya masa alwalan ya d'agasa suka koma waje wajan jama'a. Ummy na chan side d'insu tana kuka bayan ta sauya kayan jikinta zuwa dogon rigan atampha. Kuka kam itama tayi har ta gode Allah na tausayin Rayuwarta da kuma na mijinta. Saida tayi mai isarta sannan tasa hijab ta fito zuwa side d'in Abban. Daga chan nesa da gawan ta tsugunna tana kuka tana masa Addu'a. Sai a lokacin ta lura da har su Twins dasu Aunty Faty da Zainab sun iso. Kamar yanda aka fad'a, karfe sha d'aya aka fito da gawan Abba, Aka masa sallah, Sannan aka tafi dashi zuwa gidansa na gaskiya. ``` A daidai nan gab'ar inaso naja hankulan mu

Table of Contents

Chapters

82 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82