Chapter 13
Chapter 13
uku taba Mama, yadi da shadda taba Baba yanata murna, da kanta takai musu d'inkin, ta biya kud'in. Bata samu shiga gidansu Bilal ba sai dare, ganin kayan abincin da Ummy ta kawo yasa Umman Bilal fashewa da kuka, lallashinta Ummy ta dungayi har Bahar k'anin Bilal ya shigo gidan yana cewa "Umma wannan shekaran ma na rasa, duk inda nake tunanin samun rancen kud'i naje ban..." Kasa k'arasa maganan dayake yayi ganin Ummy dan sai a lokacin ya lura da ita, duk da ya girme mata hakan bai hanashi gaisheta ba, dan murmushi tamai tana cewa "Ni yakamata na gaisheka bakai bah" Murmushi yayi ta gaida shi ya amsa, atampha ta mik'ama Umma shima ta mik'amai Yadi, nan sukaita zuba godiya kamar sun ari baki har saida tayi hawaye. Tambayanshi tayi ranchan kud'in me yake nema yace yasan ya rubuta jamb neh ya koma makaranta, batareda bata lokaci ba tace ya biyota gida ya amsa. Umma ta sake fashewa da kuka, Ummy itama ta saki kuka ta rungumo Umman tana cewa "Ki daina kuka Umma, duk abinda nake muku bazan tab'a biyan Ya Bilal abinda yamin ba a rayuwa" Sun dade suna kuka, Bahar ne yayita basu baki har sukayi shiru, Umma sai sa mata albarka take ta mata sallama Bahar ya biyota dan amsan kud'in. Bayan ta basa yayi godiya ta rok'eshi alfarman ya amso masu Mama d'inkinsu data bayar nan layin bayansu. Batareda b'ata lokaci ba ya amsa mata bayan ya k'ara mata godiya. Ummy Abduol✍🏻 [3/11, 8:33 PM] Alion Bagari: ♠♠♠♠♠♠♠♠ ♠♠♠♠ *JAMALUDEEN* ♠♠♠♠ ♠♠♠♠♠♠♠♠ By *Ummy Abduol* Dedicated to My *Late Siblings* *Xaboorah Hapsert* Wannan shafi kacokan taki ce kyauta. Ina matuk'ar godiya Page 16 Batare da b'ata lokaci ba ya amsa mata bayan ya k'ara mata godiya. Koda ta dawo gida abinci Mama ta zuba mata, Tuwon shinkafa da miyar egusi sai k'anshi yake, nan kan tabarma suka zauna a waje suna shan iska kasancewar lokacin zafi neh. D'ibo tuwon Ummy tayi harta kai saitin bakinta Jamal ya fad'o mata a rai, tunani ta soma dan tasan yanzu lokacin cin abincinsa neh, Allah sarki ta fad'a a hankali, dakyar takai loman ta soma taunawa a hankali kamar tana cin magani. Mama dake gefenta tanaba Baba abinci ta kalleta "Ummy lapia, ko bakij dad'in abincin baneh?" Girgiza kai tayi ta kirkiro murmushi "Aa abincin yayi dad'i sosai, Jamal na tuna nasan ynzu lokacin bashi abinci neh" Baba yace "Allah sarki, Allah kenan shiyasa kullum nake k'ara godema Allah dayasa nake ji nake iya magana, kuma nake sauran Alamura na duk da bana gani" Tausayawa Mahaifin nata tayi tace "Insha Allahu Baba zak warke, zaka cigaba da gani kamar yanda kowa yake gani" Murmushin takaici yayi batare da yace komai bah. Labarin abinda ya faru da Jamal rannan ta basu, Mama tace "Anya kuwa ciwon yaran nan baida nasaba da mutanen b'oye" Baba ya gyad'a kai yace "Maganarki abin dubawa ce, saidai zai iya yuwuwa basu d'in baneh kawai dai ya fad'i neh" Itadai Ummy batace komai ba sai kallansu datake. Mama tace "Anma Mallan wannan alamace ai ta cewa akwai su a tare dashi, kasan su mutanen nan basu san suratul Yasin musamman idan sunyi k'amari" Baba ya gyad'a kai yace "Hakaneh maganarki, koma dai basu d'in bane kamata yayi asama masa na gargajiya inaga zaifi na bature" Ummy tayi murmushi tana kallan Iyayen nata yanda suke hira cikeda sha'awa. Washe gari wuraren azahar ta baro gida ta dawo bakin aikinta, kasancewar lahadi ce a falon k'asa ta had'u da Mami itada wasu bak'i, gaidasu tayi ta bar wajan ta shiga d'akinta. Saida tad'an huta sannan tasa uniform ta fito ta shiga kicin. Sun gaisa da mutanen kicin d'in, Laurat ta tareta da fara'a tana cewa "Oyoyo Nannyn Jamal" Duka ta d'akama Laurat d'in da wasa tana cewa "Bakida kirki wallahi" Dariya sukasa duka, Laurat tace "Kinbar Mami da aiki dan naga daga jiya zuwa yau ita ta chanje ki" Ummy tayi murmushi ta d'aga kai tana duba agogon kitchen d'in "Saura minti talatin lokacin feeding d'insa yayi, barinje zamu had'u anjima" Fita tayi ta haura sama zuwa d'akinsa, Yau kaftan ce a jikinsa, brown yadi mai tsadan gaske da santsi, d'inkin yayi fitting d'inshi kamar a jikinshi aka d'inka, sosai yama Ummy kyau sai kallansa take kyaftawa batayi. Muryan Mami ne ya dawo da ita tana cewa "Yauwa Ummy, gwara da kika dawo da wuri dan fita zanyi" Ummy tayi murmushi tace "Dama nayi tunanin wanda zai rik'e aikin kafin na dawo" Mami tace tana k'okarin fita "Babu kowa niketa d'awainiya, nima ga gajiyar aiki" Bata jira mai Ummyn zatace ba tabar d'akin. Coasterd ta dama ta barshi ya huce sannan tasa madara ta soma zuk'a a syringe tana d'ura masa. Haka tai tayi harta gama ta kwace kayan ta fita dasu, yau bata kaisa waje ba dan gudun magana wajan Mabrookah. Kula sosai Jamal ke samu daga wajan Ummy, har wata yar k'iba yayi, Abba da Mami na matuk'ar jin dad'in yanda Ummyn ke kula dashi. Yauma kamar kullum chan garden d'in gidan ta kaisa, tun bayan fitarsu Mami taganshi wani iri har yanayin idanunshi sun chanza kamar da abinda ke damunsa Jikinta ne yayi sanyi ta zuba masa narkakun idanunta tana kallansa, gashi batada waya balle ta kira Mami ko Mabrookah ta sanar dasu halin da ake ciki. Hannu tasa ta tab'a wuyanshi, zafi taji jikinshi yayi sosai, nan hankalinta ya tashi ta rasa yanda zatayi, kitchen ta shiga ta kira Laurat suka fito waje ta baya "Laurat kamar Jamal bashida lapia" "Bashida Lapia kuma? Shida baya magana ya akai kikan baida lapia" cewar Laurat tana kallan Ummyn Hannunta Ummy ta kama sukazo inda yake zaune a garden ta nuna mata shi tana cewa "Kinga yanda idanunsa suka sauya? Kuma jikinshi ma da zafi" Laurat tayi Jim sannan tace "Tho yanzu meye abinyi? Gashi su Hajiya basu nan kuma ni banga wani mai waya a cikin ma'aikatany gidan nan bah" Shiru sukayi gaba d'aya suna kallansa "Abu mafi sauk'i shine ki kyallesa kawai ko ki maidasa d'aki idan Aunty Mabrookah ta dawo sai ki sameta dan naga tana rigasu dawowa" Kai Ummy ta gyad'a Laurat ta koma kicin bakin aikinta. Rasa abinyi tayi ta sake tab'a jikinsa taji ya k'ara zafi fiyeda d'azu. Hankalinta ya tashi nan da nan hawaye suka cika mata ido. Kallanshi kawai takeyi tana chan kuma tace "Sannu! Sannu!! Allah bakay lapia" Ta k'arasa hannu ta tab'a goshinsa tana cewa "Kayi hak'uri kaga ba kowa da an kaika asibiti, Sannu" Tausayinta ne ya mamaye mata zuciya, saitin kunnensa tasa bakinta, Bismillah tayi sannan ta karanta fatiha ta da Qulhuwallahu, Falaq da Nas. Ta tofa masa a jikinsa gaba d'aya. Wani zufa ne ya soma karyo masa, tasa d'an kwalin riganta tana share masa a hankali, Suratul mulk ta soma rerowa a hankali cikin zazzak'ar muryanta tana cigaba da goge masa zufan dake goshinsa. Wangale gate d'in gidan akayi wata had'adiyar red doddge ta shigo ciki tayi parking a haraban gidan. Kyakyyawan saurayi ne bak'i ya fito daga cikin motar sanye da blue gezina sai hek'i take da d'aukar ido. Direct side d'insu Mami ya shiga sallama ya dinga dokawa a falon k'asa, d'aya daga cikin ma'aikatan gidan ce
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82