Chapter 47
Chapter 47
kud'in da zai gada" "Ni dai Umma ina sanshi ban damu da kud'insa bah" Duka Aunty Faty ta d'aka mata tana huci "Wallahi ki shiga taitayinki, Albasa dai batayi halin ruwa ba Mabrookah" Ta mik'e a fusace tana cewa "Ki zauna nan soyaiya ta rufe miki ido, idan bakiyi anfani da maganin nan ba kina nan Ummyn da kika raina zata k'wace gidan gaba d'aya" Fuuuu tabar d'akin a fusace. Mabrookah ta sake fashewa da kuka tana ganin abubuwan da suka faru d'azu tsakanin Ummy da Jamal take gani a idonta. Suna shiga d'akin Ummy ta sakeshi ta shiga toilet ta had'a masa ruwan wanka ta fito. Kwance ta samesa kan gado fuskansa na kallan ceilng idanunsa a lumshe ta k'arasa bakin gadon "Ruwan wanka na jiranka" Yi yayi kamar baiji bah, ta turo baki ta matsa sosai kusa dashi. Yayi saurin janyota ta fad'a kan k'irjinshi, tashi take kokarin yi ya rik'eta sosai a jikinsa "Dan Allah Ya Jamal ka daina wallahi banaso" Yanda tayi maganan a shagwab'e yasa shima ya shagwab'e fuska yace "In ni kuma inaso fah" Ta mak'e kafad'a dakyar ta janye jikinta, ya mik'e yana cije leb'e ya shiga toilet d'in. Falo ta koma ta tarar Mabrookah tabar wajan, ta rik'e k'ugu tana murmushin mugunta. D'akinta ta koma ta sake wanka tayi sallan isha'i sannan ta chanza zuwa night wears ta kwanta. Har bacci ya soma d'aukanta taji kamar ana shafata, a razane ta mik'e zaune taga Jamal ne duk yabi ya susuce, kamar zatayi kuka tace "Dan Allah ka bari" "Pls Ki tausaya min wife, a matse nake plssss" Bai jira mai zatace ba ya soma shafata. (Asuba ta gari Angon Jaleelah) Kukan shagwab'a Ummy keyi tana kai masa duka a k'irji, murmushi ya mata ya d'auketa ya kaita toilet. Wanka ya mata ya dawo da ita sai kukan shagwab'a take masa. Dakyar ta yarda ya shiryata cikin dogon riga bak'i mai pink flowers a jiki. Har ya gama bata daina turo baki bah. Murmushi yayi ya d'ago hab'arta ta lumshe ido dasauri. Cikin sanyin murya yace "Allah ya miki albarka Wife, bansan da kalmar da zanyi anfani dashi ba wajan gode miki. I love uh so much" Hannunta ya kama ya saka mata keyn mota ya dunkule hannun "Tukuicin faranta min da kikayi First night, Thank uh so much" Tunda ya saka mata keyn a hannu take bin hannun da kallo idaunta waje. Kwantar da ita yayi yaja mata bargo "Kisha baccin ki dan jiya ban bari kinyi bacci bah" Cikeda kunyansa tace "Nago..." Yatsansa yasa a lips d'inta "Shhhhhh... Babu godiya tsakanina dake Wife, just sleep" Tayi saurin lumshe idonta tana murmushi. Farinciki yau yakeji fiye da ko yaushe, dakin ya sauka ya shiga na Mabrookah. Zaune ya sameta kan gado tana shirin zuwa makaranta, kallo d'aya ta masa ta kauda kai, ya zauna kusa da iya da d'an murmushi "Amarya tah!" Ta kauda kai gefe tana saka handout a cikin jakanta "Amarya yau ba magana" Batace komai bah ta d'au jakanta ta fita tana gungunai, murmushin takaici yayi ya mik'e ya fita. Sama ya hau yayi wanka ya shirya, d'akin Ummyn ya lek'a ya samu tana bacci, peck ya mata a goshi ya fita. Direct side d'in Mami ya nufa, bai tarar da kowa a falo ba ya haura sama zuwa d'akinta, zaune ya sameta tana latsa waya. Ya zauna k'asa kusada iya ya gaidata. Amsawa tayi tareda aje wayan a gefenta "Yanzu dai Ummy sai tagadama take zuwa tana gaida ni" Yad'an sosa k'eya tareda duk'ar dakai "Batada lafiya ne kwana biyu shiyasa" Gyad'a kai kawai tayi sannan tace "Naga sabon mercedes a haraban gida na wanene" Gabansa ne ya fad'i ya d'an dago suka had'a ido yace "Na Ummy neh" "Mene!" Mami ta furta a fusace "Na Ummy fah kace, waya bata mota?" Murya a d'an sark'e yace "Ni na siya mata" Ran Mami idan yayi dubu ya b'aci tace "Ita kuma Mabrookah fah" Jim yayi chan wayansa ya soma ruri, cirowa yayi daga aljihun shi yafa Mifzal ne yad'an kalli Mami dake ta hararansa "Tun ba'aje ko inaba kenan ka fara nuna rashin adalci Jamal, yau sati biyu da rasuwan mahaifinka har ka fara b'arna da kud'i" Shiru dai yayi baice komai bah kansa k'asa "Ina magana kayi banza dani" "Dan Allah kiyi hak'uri, kinga fa Mami kwata kwata Mabrookah bata daraja ni taya zanji dad'i har na mata ky..." "Rufemin baki shanyayen banza, to bari in gaya maka dole itama Mabrookah sai ka saya mata mota itama" "Anma Mami..." Ta d'aga masa hannu tana huci "Na gama magana, ka tashi ka bani guri" Mik'ewa yayi a sanyaye ya fita daga d'akin, a corridor ya had'u da Aunty Faty, saida ya juya k'eya sannan ya gaidata, harara ta zafga masa bata amsa ba ta bar wajan. Motansa ya shiga yabar gidan ransa ba dad'i, yana cikin driving Mifzal ta sake kiransa. Gefen titi yayi parking sannan ya kirasa, daga chan b'angaren Mifzal yace "Idan baka komai kazo Office akwai wasu mahimman abubuwa danakeso na fad'a maka akan Case d'in nan" Toh kawai Jamal yace ya kashe kiran ya tada motan ya nufi office d'in Mifzal. Bayan sun gaisa Mifzal ya gyara zama yace "Kasan hausawa na cewa idan baka iya kama b'arawo ba sai b'arawo ya kamaka" Ummy Abduol✍🏻 ♠♠♠♠♠♠♠♠ ♠♠♠♠ *JAMALUDEEN* ♠♠♠♠ ♠♠♠♠♠♠♠♠ By *Ummy Abduol* Dedicated to My *Late Siblings* Page 54 n 55 "Kasan hausawa na cewa idan baka iya kama b'arawo ba sai b'arawo ya kamaka" Jamal ya gyara zama yana sauraronsa "Bazai yuwu hakanan muje mu kamasa ba duk da akwai hujjoji masu kyau a hannun mu" Jamal ya b'ata fuska "To yanzu me kace zaka fad'amin mai mahimmanci" Mifzal ya cigaba sa cewa "Munyi bincike a kansa sosai mun gano yana zaune ne a gidan wani hamshak'in mai kud'i mai suna Alhaji Ameenu, sai dai mutanen unguwar babu wanda yasan menene sana'ar mutumin. Kuma kwanan nan suka dawo k'asar dan da ba anan yake bah" Jimm Jamal yayi yana tunani, Mifzal yace "Yanzu haka sun bar k'asar shida Alhajin, anma iyalensa na nan. Dole yanzu zamu jira dawowan su dan mu cigaba da bibiyarsa, saboda mu gane shi Alhajin Ameenun wanene, kasan kama babban mutum a k'asar nan nada hatsari. Musamman shi da bamusan meya taka bah" Mik'ama Mifzal d'in hannu yayi sukayi musabaha "Nagode sosai Friend, Allah ya saka da Alheri" Da murmushi ya amsa da "Ameen. Ka kwantar da hankalinka, insha Allahu zamuyi iya yinmu dan mu kama mai hannu cikin wannan kisan" Ya lumshe ido ya bud'e a hankali tareda mik'ewa ya masa sallama ya tafi. Office ya nufa yana tunanin abinda Mami tasa shi dole yayi, bawai baida kud'in baneh Aa. Tunaninsa kawai yanda zai b'annatar da kud'insa wajan wacce bata darajasa, da biyaiya ko na second d'aya. Dogon tsaki yaja yasaka hannu cikin suman kanshi yana ya mutsawa yana b'ata fuska. Waya yayi dan a kawo masa motan, cikin awa da baifi d'aya ba aka kawo masa, sak irin na Ummy ce, saidai na Mabrookah Bak'i neh, ita kuma na Ummy Arsh ce. Gida yasa suka kai masa motan, shi kuma bayan ya tashi aiki ta biya kasuwa ya sayi kayan masarufi ya nufi gidansu Ummy. Sosai
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82