Skip to content

Chapter 69

Chapter 69

Jamaluddeen Book One Complete Hausa Novels 1,200 words 0 views Progress saved
Download Book

"Shhhh! Ka daina kuka dan Allah, ko kanaso nima nayi?" Ya girgiza mata kai yana kallan kwayan idanunta dake cike da k'walla Ta rik'o hannunsa tasa a maranta tana kallansa "Ni da Babyn mu muna tare dakai" Ta k'are maganan tana kuka a hankali, ya rungumeta tsam a jikinsa yana lallashinta. Ta shagwab'e fuska tace "Pls Ya Jamal inaso inje inga Mama, rabona dana ganta wata d'aya kenan kuma nasan itama tanasan ganina kawaici ne ya hanata zuwa" Ta k'are maganan tana zumb'ura baki, ya ja bakin ta saki k'ara k'adan. Murmushi yayi yace "Ba yanzu bah, ni nama manta jiya danaje tace na gaishe ki" Ta kallesa da mamaki, ya kashe mata ido d'aya ya mik'e ya fita, chan sai gashi da wani bak'in leda ya mik'a mata yace "Tace na baki" Jiki na rawa ta amsa ta bud'e, kayan k'amshi ta gani da sinadaran girki kala kala, sai wani leda kuma dake ciki shima ta bud'e, magunguna ta gani ko ba'a fad'a mata ba tasan na menene, tad'anyi murmushi tana cigaba da kallan cikin ledan. Karo sukayi ta d'ago tana kallansa tare da rufe ledan "Meye kake kallan min sirri" Ta murgud'a baki tana k'ara b'oye ledan a bayanta, yayi dariya ya k'ara matsowa "Idan abin ci ne to a raba aba kowa nasa dan bazan yarda bah" Hararan wasa ta masa "Bayan ka riga ka bud'e ka d'auka" Ya d'aga hannu dasauri kamar criminal "Babu ruwana, yanda ta bani haka na d'auko na aje, duk ke kika mantar dani jiya da nabaki da wuri" Ta sake turo baki "Dan Allah Ya Jamal ka kaini" Ya mak'e kafad'a yana kwaikwayan irin magananta "Aa nak'iya" Takai mai dukan wasa ya rik'e hannun ta saki kukan shagwab'a, kwantar da ita yayi kan gadon ya soma lallubenta, ina ganin haka na tattara nabar musu d'akin. K'arfe takwas da rabi na dare ya fito daga masallaci bayan yayi sallahn isha'i, side d'insu ya shiga dasauri dan so yake ya fita, Mabrookah ya samu a falonta tsaye duk tayi wani laushi, rana d'aya harta fad'a, ya k'arasa kusada ita dan yanzu tausayi take basa ya kama hannunta yad'an matse ta lumshe ido wasu sabin hawaye suka gangaro mata "Haba k'anwata, banace ki daina kukan nan bah" Ta bud'e idanunta a hankali tana kallansa "Bazan iya daina kuka na ya Jamal har sai naje naga Mummy da Mami, dan Allah ka kaini wajansu" Yad'anyi jim yana kallanta, shima chan d'in yakeso yaje kafin gobe a shiga court yaji yanda za'ayi, dan har a zuciyarsa baisan wani abu ya samesu, ko ba komai Mami tamkar mahaifiya take a garesa, sannan Aunty Faty surikarsa ce. Maganan datayi ne ya dawo dashi daga duniyar tunanin daya tafi, ya d'ago yana mata murmushi, "Ki bari komai will be fine insha Allah" Ta girgiza masa kai tana cigaba da kuka "Aa pls, dan Allah Ya Jamal" Ya k'are maganan da matsanancin kuka, ya d'ago kanta yana share mata hawaye "Stop crying" "Dan Allah zanje na gansu" Ya sassauta rik'on daya maya mata yace "Jeki shirya" Dasauri ta shiga d'akinta ya bita da kallo tare da sauke ajiyar zuciya. Sama ya haura ya shiga d'akinsa ya sauya zuwa kaftan ya fito ya shiga d'akin Ummy, ta gama shiryawa kenan cikin doguwar rigar Atampha tana murza powder a fuska ya shigo, wajan mirrown ya k'arasa ya sak'ala hannunsa a wuyanta "Kinyi kyau sosai Wife" Tayi murmushi tana kallansa ta mirrown "Ya Jamal ina zaka?" Ya sunkuyo da fuskansa kusada nata yace "Ko kin fasa zuwa wajan Maman neh" Ai dasauri ta mik'e har tana kokarin turesa ta d'auko Hijab sai dariya yake mata, hannunta ya kama suka fito, a falon k'asa suka samu Mabrookah itama ta shirya, Tana ganinsu tare taja guntun tsaki tayi gaba suna binta a baya, tun daga k'ofar falonsu ya danna button d'in security motar ta k'arasa ta bud'e dasauri ta shige gaba. Sam Ummy bata nuna damuwa ba ta bud'e baya ta shiga yaja suka bar cikin gidan. Jefi jefi shida Ummyn suke hira har suka k'arasa kofar gidansu Ummyn, ta bud'e dasauri ta fita, ganin bai fitoba yasa ta juya tana kallansa "Ka shigo mana" Yad'an kalli Mabrookah dake gefensa tana cika tana batsewa yace "Zamu d'an fita ne idan zan biyo na d'aukeki sai na shiga mu gaisa" Batace masa komai ba ta juya ta shiga cikin gidan rai b'ace. Police station d'in suka nufa, sunyi sa'a sun samu Mifzal bai riga ya tafi bah. Jamal na masa bayani ba b'ata lokaci yasa wani daga cikin 'yan sandan ya fito dasu zuwa secret room. Mifzal da kansa ya musu jagora zuwa d'akin, Kallo d'aya Mabrookah ta musu ta fashe da kuka ta k'arasa inda suke zazzaune, Mami nakan wheel chair duk sun rame kamar basu bah. Ta tsugunna gabasu tana kuka tana kallansu "Mummy, Mami meyasa kukayi haka? Meyasa kuka bari shed'an yaci galaba akan ku" Barin musu wajan Mifzal yayi, Jamal na bakin k'ofa yana hawaye, kallan Mami yake tayi ganin yanda k'afanta ke nannad'e da bandage sai zuban ruwa yake yana wani irin k'arni. Daga Mami har Aunty Faty kasa magana sukayi sai bin Mabrookahn suke da kallo, A hankali Jamal ya soma takawa zuwa wajan, Mami da d'ago ad'an tsorace tana kallansa, ya tsugunna guiwa biyu gabanta ya kama k'afarta dabaida ciwo yana kallan fuskanta hawaye na zuba a idanunsa. Tayi saurin kauda fuska ta fashe da kuka, ya d'ago yace "Har gobe Mami ke uwace a gareni, har yanzu matsayinki a rayuwata yana nan bai chanza bah, duk abinda kikamin na yafe miki Mamina" Ta janye k'afanta daya rik'e tana cigaba da kuka "Rud'in duniya da bin zugan shaid'an su suka jamin na shiga wannan halin, ka gafarce ni D..." Yayi saurin sa hannu ya rufe mata baki yana girgiza mata kai. Kasa magana Mabrookah tayi sai kuka datake kamar ranta zai fita. Mifzal ya shigo ya fad'a musu lokaci yayi, hakanan sunaji suna gani suka bar wajan suna kuka suna waiwayen su Mamin. Ransu duk ba dad'i suka shiga mota suka bar station d'in, saida ya tsaya ya d'au Ummy daketa cika tana batsewa sannan suka nufi gida. Daru suka sha daren ranar shida Ummyn dan sosai ranta ya b'aci na barinta dayayi suka wuce. Washe gari ranar da za'a shiga Court, da wuri ya tashi ya shirya saidai Yau Wife d'insa ta tashi da zazzab'i, dole saida ya tsaya ta shirya sannan suka sauko yana rik'e da ita dan jiri take gani, Mabrookah suka samu a falo ta shirya tana zaune tana jiransu lokacin k'arfe takwas da rabi. Shi da kansa ya bud'e ma Ummy mota ta shiga gaba, Mabrookah ta turo baki ta shiga baya suka d'au hanya. Tara daidai duka isa Court d'in, sun samu mutane duk sun hallara, bayan zazzauna aka soma gabatar da k'aran da Areef d'an Alhaji Ameenu ya kawo akan abi ma Mahaifinsa hak'insa, bada umarnin a kawo Alhaji Ameenun Alk'alin yayi, nan wani d'an sanda ya shigo da Alhajin da Bilal, Ummy dake rakub'e jikin Jamal saboda sanyin datake ji ta zaro ido tare da d'agowa tana kallan Bilal wanda duk ya rame kamar bashi bah. Gaban Jamal ya fad'i sanda ya d'ago ya kalli Alhaji Ameenu, Ummy ko Areef ta

Table of Contents

Chapters

82 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82